.

Quran translation in hausa language

Chapter 1 (Sura 1)
1Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
2Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
3Mai rahama, Mai jin ƙai;
4Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
5Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
6Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
7Hanyar waɗanda Ka yi wa ni´ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.
Chapter 2 (Sura 2)
1A. L̃. M̃.
2Wãncan ne Littãfi, bãbu shakka a cikinsa, shiriya ne ga mãsu taƙawa.(1)
3Waɗanda suke yin ĩmãni game da gaibi, kuma suna tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa.
4Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, kuma game da Lãhira suna yin yaƙĩni.
5Waɗannan suna kan shiriya, daga Ubangjinsu, kuma waɗannan su ne mãsu cin nasara.
6Lalle ne waɗanda suka kãfirta(1) daidai ne a kansu, shin kã yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, ba zã su yi ĩmãni ba.
7Allah Ya sa hãtimi a kan zukãtansu, da a kan jinsu, kuma a Kan ganin su akwai wata yãna; kuma suna da wata azãba mai girma.
8Kuma akwai daga mutãne wanda(2) yake cewa: "Mun yi imani da Allah kuma da Yinin Lãhira." Alhãli kuwa su ba muminai ba ne.
9Suna yaudarayya da Allah da waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli bã su yaudarar kõwa fãce kansu, kuma bã su sakankancħwa!
10A cikin zukãtansu akwai wata cũta. Sai Allah Ya ƙãramusu wata cũta, kuma suna da azãba mai raɗaɗi sabõda abin da suka kasance suna yi na ƙarya.
11Kuma idan aka ce musu: "Kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa," sukan ce: "Mũ mãsu kyautatawa kawai ne!"
12To, lalle ne su, sũne mãsu ɓarna, kuma amma bã su sansancewa.
13Kuma idan aka ce musu: "ku yi ĩmãni kamar yadda mutãne suka yi ĩmãni," sukan ce: "Zã mu yi ĩmãni ne kamar yadda wãwãye suka yi ĩmãni?" To, lalle ne su, sũ ne wãwãye, kuma amma bã su sani.
14Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni,sukan ce: "Mun yi ĩmãni. "Kuma idan sun wõfinta zuwa ga shaiɗãnunsu,(3) sukan ce: "Lalle ne muna tãre da ku: Mu mãsu izgili, kawai ne."
15Allah Yana yin izgili(4) gare su kuma Yana taimakon su a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa.
16Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, sai fataucinsu bai yi rĩba ba, kuma ba su kasance masu shiryuwa ba.
17Misãlinsu(1) shĩ ne kamar misãlin wanda ya hũra wuta, to, a lõkacin da ta haskake abin da yake għfensa (na abin tsõro), Allah Ya tafi da haskensu, kuma Ya bar su a cikin duffai, bã su gani.
18Kurãme, bħbãye, makãfi, sabõda haka bã su kõmõwa.
19Ko kuwa kamar girgije mai zuba(2) daga sama, a cikinsa akwai duffai da tsãwa da walƙiya: suna sanyãwar yãtsunsu a cikin kunnuwansu dãga tsãwarwakin, dõmin tsõron mutuwa. Kuma Allah Mai kħwayewa ne gã kãfirai!
20Walƙiyar tana yin kusa ta fizge gannansu, ko da yaushe ta haskakã musu, sai su yi tafiya a cikinta, kuma idan ta yi duhu a kansu, sai su yi tsaye. Kuma dã Allah Yã so, sai Ya tafi da jinsu da gannansu. Lalle ne Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.
21Yã ku mutãne! Ku bauta(3) wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku !
22Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya fitar da abinci daga ´ya´yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane.
23Kuma idan kun kasance a cikin shakka daga abin da Muka sassaukar ga Bãwanmu, to, ku zõ da sũra guda daga misalinsa (Alƙur´ãni). Kuma ku kirãwo shaidunku (4) baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya.
24To, idan ba ku aikata (kãwo sura) ba, to, bã zã ku aikata ba, sabõda haka, ku ji tsoron wuta, wadda makãmashinta mutãne da duwãtsu ne, an yi tattalinta dõmin kãfirai.
25Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka yi ĩmãni. kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, cħwa lallene, suna da gidãjen Aljanna, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Ko da yaushe aka azurta su da abinci daga wasu ´ya´yan itãce daga gare su,(1) sai su ce: "Wannan shi ne aka azurta mu da shi daga gabãnin haka," Kuma a je musu da shi yana mai kama da juna, Kuma sunã da, a cikin su, mãtan aure mãsu tsarki, kuma su, cikin su madawwama ne.
26Lalle ne, Allah bã Ya jin kunyar Ya bayyana wani misãli, kõwane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, sai su san cewa lalle shi ne gaskiya daga Ubangijin su, kuma amma waɗanda suka kãfirta, sai su ce: "Mħne ne Allah Ya yi nufi da wannan(2) ya zama misãli?" na ɓatar da wasu mãsu yawa da shi, kuma Yana shiryar da wasu mãsu yawa da shi, kuma bã Ya ɓatarwa da shi fãce fasiƙai.
27Waɗanda suke warware alƙawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma su yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi a sãdar, kuma suna ɓarna a cikin ƙasa, waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
28Yaya kuke kãfirta da Allah, alhãli kuwa kun kasance matattu sa´an nan Ya rãyar da ku, sa´nnan kuma Ya matar da ku, sa´an nan kuma Ya rãya ku, sa´an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku?
29Shi ne Wanda Ya halitta muku abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya, sa´an nan kuma Ya daidaita(3) zuwa sama, sa´an nan Ya aikata su sammai bakwai. Kuma Shi ga dukan kõmai Masani ne.
30Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya ce ga malã´iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halĩfa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, zã Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma ya zubar da jinainai alhali kuwa mu, muna yi maka tasbihi game da gõde maka, kuma(1) muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba."
31Kuma Ya sanar da Ãdam sũnãye dukansu, sa´an nan kuma ya gitta su a kan malã´iku, sa´an nan Ya ce: "Ku gaya mini sũnayen waɗannan, idan kun kasance mãsu gaskiya."
32Suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka! Bãbu sani a gare mu, face abin da Ka sanar da mu, lalle ne Kai, Kai ne Masani, Mai hikima."
33Ya ce: "Yã Ãdam! Ka gaya musu sũnãyensu." To, a lokacin da ya gaya musu sũnãyensu, (Allah) Ya ce: "Ashe, ban ce muku(2) ba, lalle Ni, Inã sane da gaibin sammai da ƙasa, kuma (Inã sane da ) abin da kuke bayyanawa da abin da kuka kasance kuna ɓõyewa?"
34Kuma a lõkacin da Muka ce ga malã´iku: "Ku yi sujada ga Ãdam," Sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai.
35Kuma muka ce: "Ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a gidan Aljanna, kuma ku ci daga gare ta, bisa wadãta, inda kuke so, kuma kada ku kusanci wannan itãciyar, har ku kasance daga azzãlumai."
36Sai Shaiɗan ya talãlãɓantar da su ga barinta, sai ya fitar da su daga abin da suka kasance a cikinsa. Kuma muka ce: "Sãshenku nã maƙiyi ga sãshe, kuma kuna da a cikin ƙasa matabbata da jin dãɗi zuwa ga wani lõkaci."
37Sai Ãdam ya karɓi wasu kalmõmi daga Ubangjjinsa, sabõda haka ya karɓi tũba a kansa. Lalle ne Shi, Shĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
38Muka ce: "Ku sauka daga gare ta gabã ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki."
39"Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗannan sũ ne abõkan Wuta; sũ a cikinta madawwama ne."
40Yã Banĩ Isrã´Ĩla(1) ! Ku tuna ni´imãTa wadda Na ni´imta a kanku, kuma ku cika alƙawariNa, In cika muku da alƙawarinku. kuma Ni, ku ji tsõro Na.
41Kuma, ku yi ĩmãni da abin da na saukar, yana, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku, kuma kada ku kasance farkon kãfiri game da shi. Kuma kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da ãyõyiNa. Kuma ku ji tsõrõNa, Nĩ kaɗai.
42Kuma kada ku lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma ku ɓõye gaskiya, alhãli kuwa kuna sane.
43Kuma ku tsayar da salla; kuma ku bãyar da zakka; kuma ku yi rukũ´i tãre da mãsu yin rukũ´i.
44Shin, kuna umurnin mutãne da alhħri, kuma ku manta da kanku alhãli kuwa kuna karatun littãfi? Shin, bãzã ku hankalta ba?
45Kuma ku nħmi taimako da yin haƙuri, da salla. Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa, mai girma ce fãce fa a kan mãsu tsõron Allah.
46Waɗanda suka tabbata cħwa lalle ne su mãsu haɗuwa ne da Ubangijinsu, kuma lalle ne sũ zuwa gare Shi mãsu kõmãwa ne.
47Yã banĩ Isrã´ĩla! Ku tuna ni´imaTa, wadda Na ni´imta a kanku, kuma lalle ne Ni, na fĩfĩta ku a kan tãlikai.
48Kuma ku ji tsoron wani yini, (a cikinsa) rai bã ya wadãtar da wani rai da kõme, kuma ba a karɓar cetõ daga gareshi, kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma bã su zama ana taimakon su ba.
49Kuma a lõkacin da muka tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, su na taya muku muguntar azãba, su na yayyanke ɗiyanku maza su na rãyar da mãtanku. Kuma a cikin wancan akwai jarabawa mai girma daga Ubangijinku.
50Kuma a lõkacin da Muka raba tħku sabõda ku, sai Muka tsĩrar da ku kuma Muka nutsar da mutãnen Fir´auna, alhãli kuwa kũ kuna kallo.
51Kuma a lõkacin da muka yi wa´adi ga Mũsa, dare arba´in, sa´an nan kuma kuka riƙi maraƙi daga bãyansa, alhãli kũ, kuna mãsu zãlunci (da bauta masa).
52Sa´an nan kuma muka yãfe muku daga bãyan wancan, tsammãninku, kuna gõdħwa.
53Kuma a lõkacin da Muka baiwa Mũsa Littãfi da rarrabħwa, tsammãninku, kuna shiryuwa.
54Kuma a lõkacin da Mũsa ya ce ga mutãnensa: "Ya mutãnena! Lalle ne ku, kun zãlunci kanku game da riƙonku maraƙin, sai ku tũba zuwa ga Mahaliccinku, sai ku kashe kãwunanku. Wancan ne mafi alheri a wajen mahaliccinku. Sa´an nan Ya karɓi tuba a kanku. Lalle ne Shi, Shi ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
55Kuma a lõkacin da kuka ce: "Ya Musa! Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka, sai munga Allah bayyane," sabada haka tsãwar nan ta kamaku, alhãli kuwa kuna kallo.
56Sa´an nan kuma Muka tãyar da ku daga bãyan mutuwarku, tsammãninku, kuna gõdħwa.
57Kuma Muka sanya girgije ya yi inuwa a kanku, kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kanku; "Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku." kuma ba su zãlunce Mu ba, kuma amma kansu suka kasance suna zãlunta.
58Kuma a lokacin da Muka ce: "Ku shiga wannan alƙarya. Sa´an nan ku ci daga gareta, inda kuka so, bisa wadata, kuma ku shiga ƙofa kuna masu tawalu´i, kuma ku ce; "kãyar da zunubai" Mu gãfarta muku laifukanku, kuma zã mu ƙãra wa mãsu kyautatawa."
59Sai waɗanda suka yi zalunci suka sake magana watar wannan da aka ce musu, saboda haka muka saukar a kan waɗanda suka yi zãlunci da azãba daga sama sabõda abin da suka kasance suna yi na fãsiƙanci.
60Kuma a lokacin da Mũsa ya nemi shãyarwa domin mutãnensa, Muka ce; "Ka dõki dũtsen da sandarka." Sai marmaro gõma sha biyu suka ɓuɓɓuga, haƙĩƙa, kõwaɗanne mutãne sun san wurin shansu. "Ku ci kuma ku sha daga arziƙin Ubangijinku, kuma kada ku yi fasadi, a cikin ƙasa, kuna mãsu ɓarna."
61Kuma a lõkacin da kuka ce: "Yã Mũsã! Bã zã mu yi haƙuri ba a kan abinci guda. Sai ka rõƙa mana Ubangijinka Ya fitar mana daga abin da ƙasa take tsirarwa daga ganyenta, dumanta, da alkamarta da albasarta. Ya ce: "Kuna nħman musanya abin da yake mafi ƙasƙanci da wanda yake mafi alhħri? Ku sauka wani birni (daga cikin birane), domin lalle ne, kuna da abin da kuka rõƙa. "Kuma Muka dõka musu wulãƙanci da talauci. Kuma suka kõma da wani fushi daga Allah. Wancan sabõda lalle su, sun kasance suna kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe Annabãwa, bãda hakki ba. Wancan, sabõda sãɓawarsu ne, kuma sun kasance suna ƙħtarewar haddi.
62Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, da waɗanda suka tũba (1) , da Nasãra da Makarkata, wanda ya yi ĩmani da Allah da Yinin Lãhira, kuma ya aikata aikin ƙwarai, to, suna da ijãrarsu a wurin Ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba.
63Kuma a lõkacin da Muka riƙi alƙawarinku, kuma Muka ɗaukaka dũtse a bisa gareku: "Ku kãma abin da Muka baku da ƙarfi. Kuma ku ambaci abin da yake a cikin sa, tsammãninku ku kãrekanku.
64Sa´an nan kuma kuka jũya daga bayan wancan, to, bã dõmin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa, haƙĩƙa, dã kun kasance daga mãsu hasãra."
65Kuma lalle ne, haƙĩƙa, kun san waɗanda suka ƙħtare haddi daga gare ku a cikin Asabar, sai muka ce musu: "ku kasance birai ƙasƙantattu."
66Muka sanya ta (mas´alar) azãba, dõmin abin da abin da yake gaba gareta, da yake a bãyanta, kuma wa´azi ga mãsu taƙawa.
67Kuma a lõkacin da Musa yace ga mutanensa: "Lalle ne, Allah Yana umurnin ku da ku yanka wata sãniya." Suka ce: "Shin kana riƙon mu ne da izgili?" Ya ce: "Ina nħman tsari ga Allah da in kasance daga jãhilai."
68Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana, mecħ ce ita?" Ya ce: "Lalle ne, Shi, Yana cewa: "Lalle ne ita sãniya ce; bã tsõfuwa ba, bã kuma budurwa ba, tsakãtsaki ce a tsakãnin wancan,´ sai ku aikata abin da ake umurninku."
69Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka Ya bayyana mana abin da yake launinta." Ya ce: "Lalle ne, Shi Yana cewa: "Ita wata saniya ce Fatsi, mai tsan-tsan launi, tana faranta ran masu kallo."
70Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana abin da yake ita, lalle ne shãnu suna yi mana kamã da jũna, kuma mu, idan Allah Yã so, haƙĩƙa, shiryuwa ne."
71Ya ce: "Lalle ne Shi, Yana cħwa: "Ita wata sãniya ce; ba horarra bã tana noman ƙasa, kuma ba ta shayar da shuka, lãfiyayya ce: bãbu wani sõfane a cikinta." Suka ce: "Yanzu kã zo da gaskiya. Sai suka yanka ta, kamar ba zã su aikata ba.
72Kuma a lõkacin da kuka yi kisan kai, kuka dinga tunkuɗa wa jũna laifĩ a cikinsa,(1) kuma Allah Mai fitar da abin da kuka kasance kuna ɓõyħwa ne.
73Sai Muka ce: "Ku dõke shi da wani sãshenta." Kamar wancan ne Allah Yake rãyar da matattu, kuma Ya nũna muku ayõyinSa, tsammãninku kuna hankalta.
74San´nan kuma zukãtanku, suka ƙħƙashe daga bãyan wancan. Sabõda haka suka zama kamar duwatsu. ko mafi tsananin ga ƙeƙashewa. kuma lalle ne daga duwãtsu, haƙĩka, akwai abin da maremari suke ɓuɓɓuga daga gare shi, kuma lalle ne daga gare su, haƙĩƙa, akwai abin da yake tsatstsagewa har ruwa ya fita daga gare shi, kuma lalle ne, haƙĩƙa, daga gare su, haƙĩƙa, akwai da yake fãɗõwa dõmin tsõron Allah, kuma Allah bai zama gãfili ba daga barin abin da kuke aikatãwa.
75Shin fa kuna tsammãnin zã su yi imãni sabõda ku, alhãli kuwa, haƙĩƙa, wata ƙungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa´an nan kuma su karkatar da ita daga bãyan sun gãne ta, alhãli sũ, suna sane?
76Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni sukan ce: "Mun yi ĩmãni," kuma idan sãshensu ya wõfinta zuwa ga sãshe, sukan ce: "Shin, kuna yi musu magana da abin da Allah Ya buɗa muku ne dõmin su yi muku hujja da shi a wurin Ubangijinku?" Shin fa, bã ku hankalta?
77Shin, kuma bã su sanin cħwa lalle ne Allah Yana sanin abin da suke ɓõyħwa da abin da suke bayyanãwa?
78Kuma daga cikinsu akwai ummiyyai, bã su da sanin Littãfi, fãce tãtsuniyoyi, kuma sũ bã kõme suke yi ba fãce suna yin zato.
79To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubũta littãfi da hannuwansu sa´an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, dõmin su sayi kuɗi kaɗan da shi, san nan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubũtãwa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sanã´antãwa.
80Kuma suka ce: "Wuta bã zã ta shãfe mu ba, fãce, ´yan kwãnuka ƙidãyayyu."Ka ce: "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah, sa´an nan Allah ba zai sãɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba bisa ga Allah?"
81Na´am! Wanda ya yi tsiwur-wurin mũgun abu, kuma laifinsa ya kħwaye shi, to, waɗannan su ne ´yan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne.
82Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan, ´yan Aljanna ne, sũ a cikinta madawwama ne.
83Kuma a lõkacin da Muka karɓi alkawarin Bani-Isrã´ĩla(1) : "Kada ku bauta wa kõwa fãce Allah, kuma ga mahaifa ku kyautata, da mai zumunta da marãyu da matalauta, kuma ku faɗi magana mai kyau zuwa ga mutãne, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka, sa´an nan kuka jũya bãya, fãce kaɗan daga gare ku,alhãli kuwa kuna mãsu bijirħwa.
84Kuma a Lõkacin da Muka riƙi alkawarinku; bã zã ku zubar da jininku ba, kuma bã zã ku fitar da kanku daga gidãjenku ba; sa´an nan kuka tabbatar alhãli kuwa kuna bãyar da shaida (a kanku).
85Sa´an nan kuma, gã ku, yã waɗannan! Kuna kashe kanku, kuma kuna fitar da wani ɓangare daga gare ku daga gidãjensu, kuna taimakon jũna a kansu da zunubi da zãlunci kuma idan kãmammu suka je muku kuna fansarsu alhãli kuwa shĩ fitar da su abin da aka haramta muku ne. Shin fa, kuna ĩmãni da sãshen Littãfin ne, kuma ku kãfirta da sãshe? To, mħne ne sakamakon wanda ke aikata wancan daga gare ku fãce wulãkanci(1) a cikin rãyuwar dũniya? Kuma a Rãnar Ƙiyãma ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azãba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga barin abin da kuke aikatãwa.
86Waɗannan su ne waɗanda suka sayi rãyuwar dũniya da Lãhira, dõmin haka bã zã a sauƙaƙa azãba ba daga kansu, kuma sũ, bã a taimakonsu.
87Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã Littãfi, kuma Mun biyar daga bãyansa da wasu Manzanni, kuma Muka bai wa Ĩsã ɗan Maryama hujjõji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafa shi da Rũhi mai tsarki.(2) Shin fa, kõ da yaushe wani manzo ya je muku tãre da abin da rãyukanku bã su so, sai ku kangara, wani ɓangare kun ƙaryata, kuma wani ɓangare kuna kashħwa?
88Kuma suka ce: "Zukatanmu suna cikin rufi." A´a, Allah Yã la´ane su, dõmin kafircinsu kadan kwarai suke yin ĩmãni!
89Kuma a lõkacin da wani Littãfi daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, alhãli kuwa sun kasance daga gabãnin haka suna fãtar taimako(1) da shi a kan waɗanda suka kãfirta. To, a lõkacin da abin da suka sani ya je musu, sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka la´anar Allah ta tabbata a kan kãfirai.
90Tir da abin da suka sayi rãyukansu da shi; watau su kãfirta da abin da Allah Ya saukar sabõda zãlunci;(2) kada Allah Ya saukar da falalarsa a kan wanda Yake so daga bãyinsa. Sai suka kõmo da fushi game da wani fushi. Kuma ga kãfirai akwai azãba mai wulãƙantarwa.
91Kuma idan aka ce musu: "Ku yi ĩmãni da abin da Allah Ya saukar." Sai su ce: "Muna ĩmãni da abin da aka saukar a gare mu," kuma suna kãfircħwa da abin da ke bãyansa, alhãli kuwa, shi ne gaskiyar (da suka sani) mai gaskatawa ga abin da yake tãre da su (na Attaura). Ka ce: "To, don me kuke kashe annabãwan Allah gabãnin wannan, idan kun kasance mãsu bãyar da gaskiya?"(3)
92Kuma lalle ne haƙĩƙa Mũsã ya zo muku da hujjõji bayyanannu, sa´an nan kuka riƙi maraƙi(4) daga bãyansa, alhãli kuwa kuna mãsu zãlunci.
93Kuma a lõkacin da Muka riƙi(5) alkawarinku kuma Muka ɗaukaka dutse a bisa gare ku, (Muka ce:) "Ku riƙi abin da Muka kãwo muku da ƙarfi kuma ku ji" Suka ce: "Mun ji kuma mun ƙi." Kuma aka zuba son maraƙin a cikin zukatansu sabõda kãfircinsu. Ka ce: "Tir da abin da ĩmãninku yake umurnin ku da shi, har idan kun kasance mãsu ĩmãni!"
94Ka ce: "Idan Gidan(1) Lãhira ya kasance sabõda ku, a wurin Allah keɓe bã da sauran mutãne ba, to, ku yi gũrin mutuwa, idan kun kasance mãsu gaskiya."
95Kuma bã zã su yi gũrinta ba har abada sabõda abin da hannayensu, suka gabãtar. Kuma Allah Masani ne ga azzãlumai.
96Kuma lalle ne, zã ka sãme su mafiya kwaɗayin mutãne a kan rãyuwa, kuma sũ ne mafiya kwaɗayin rãyuwa daga waɗanda suka yi shirka. Ɗayansu yana son dã zã a rãyar da shi shekara dubu, kuma bã ya zama mai nĩsantar da shi daga azãba dõmin an rãyar da shi. Kuma Allah, Mai gani ne ga abin da suke aikatãwa.
97Ka ce: Wanda ya(2) kasance maƙiyi ga Jibirilu, to, lalle ne shi ya saukar da shi a kan zũciyarka da izinin Allah, yana mai gaskatãwa ga abin da yake gaba gare shi, kuma da shiriya da bishãra ga mũminai.
98Wanda ya kasance maƙiyi ga Allah da malã´ikunSa da manzanninSa da Jibirĩla da Mĩkã´ĩla to, lalle ne, Allah Maƙiyi ne ga kãfirai.
99Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun saukar, zuwa gare ka, ãyõyi bayyanannu, kuma ba wanda yake kãfirta da su fãce fãsikai(3) .
100Shin, kuma a kõ da yaushe suka ƙulla wani alkawari sai wani ɓangare daga gare su ya yi jĩfa da shi? ôa, mafi yawansu bã su yin ĩmãni.
101Kuma a lõkacin da wani manzo (Muhammadu) daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, sai wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littãfi, suka yar da Littãfin (Alƙur´ãnin) Allah a bãyan bãyansu, kamar dai sũ ba su sani ba.
102Kuma suka bi abin da shaiɗãnu(1) ke karantawa a kan mulkin Sulaimãnu, kuma Sulaimãnu bai yi kãfirci ba, kuma Shaidãnun, sũ ne suka yi kãfirci, suna karantar da mutãne sihiri. Kuma ba a saukar da shi ba a kan malã´iku biyu a Bãbila, Harũta da Mãrũta. Kuma ba su sanar da kõwa ba balle su ce: "Mũ fitina kawai ne, sabõda haka kada ka kãfirta," balle har su yi ta nħman ilmin abin da suke rarrabħwa tsakãnin mutum da mãtarsa da shi daga gare su. Kuma su (mãsu yin sihirin) ba su zama mãsu cũtar da kõwa da shi ba, fãce da iznin Allah. Kuma suna nħman ilmin abin da yake cũtar da su, kuma bã ya amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas, wanda ya saye shi, bã ya da wani rabo a cikin Lãhira. Kuma tir da abin da suka sayar da rãyukansu da shi, dã sun kasance suna sani.
103Kuma dã lalle ne sũ, sun yi ĩmani, kuma sun yi taƙawa, haƙiƙa, da sakamako daga wurin Allah shi ne mafi alhħri, dã sun kasance suna sani.
104Yã kũ waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku ce: ´Rã´inã´(2) kuma ku ce: ´Jinkirtã manã´, kuma ku saurara. Kuma kãfirai suna da azãba mai raɗaɗi.
105Waɗanda suka kãfirta daga Ma´abuta Littãfi, bã su son a saukar da wani alhħri a kanku daga Ubangijinku, kuma mushirikai mã bã su so. Kuma Allah Yana keɓance da wanda Yake so da rahamarSa. Kuma Allah Ma´abũcin falala mai girma ne.
106Abin da Muka shãfe(1) daga ãya, ko kuwa Muka jinkirtar da ita, zã Mu zo da mafi alhħri daga gare ta ko kuwa misãlinta. Ashe, ba ka sani ba, cħwa lalle ne, Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne?
107Shin ba ka sani ba, cħwa lalle ne Allah, Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa kuma bã ku da, baicin Allah, wani majiɓinci, kuma bã ku da wani mataimaki?
108Kõ kuna nufin ku tambayi Manzonku, kamar yadda aka tambayi Mũsã a gabãnin haka? Kuma wanda ya musanya kãfirci da ĩmãni, to, lalle ne yã ɓace tsakar hanya.
109Mãsu yawa daga Ma´abuta Littãfi sunã gũrin dã sun mayar da ku, daga bãyan ĩmãninku, kãfirai,sabõda hãsada daga wurin rãyukansu, daga bayãn gaskiya tã bayyana a gare su. To, ku yãfe, kuma ku kau da kai, sai Allah Yã zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne.
110Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka. Kuma abin da kuka gabãtar dõmin kanku daga alhħri, zã ku sãme shi a wurin Allah. Lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne.
111Kuma suka ce: "Bãbu mai shiga Aljanna fãce waɗanda suka zama Yahũdu ko Nasãra." Waɗancan tãtsũniyõyinsu ne. Ka ce: "Ku kãwo dalilinku idan kun kasance mãsu gaskiya."
112Na´am! Wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yana mai kyautatãwa, to, yana da ijãrarsa, a wurin Ubangijinsa, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba.
113Kuma Yahũdãwa suka ce: "Nasãra ba su zamana a kan kõme ba," kuma Nasãra suka ce: "Yahũdãwa ba su zamana a kan kõmeba,"(1) alhãli kuwa su, suna karãtun Littãfi. Kamar wancan ne waɗanda ba su sani ba suka faɗa, kamar maganarsu sabõda haka Allah ne ke yin hukunci a tsakãninsu a Rãnar Ƙiyãma, a cikin abin da suka kasance suna sãɓawa jũna a cikinsa.
114Kuma wãne ne mafi zãlunci(2) daga wanda ya hana masallãtan Allah, dõmin kada a ambaci sunanSa a cikinsu, sai kuma ya yi aiki ga rushe su? Waɗannan bã ya kasancħwa a gare su su shigħ su fãce suna mãsu tsõro. Suna da, a cikin duniya wani wulãkanci, kuma suna da, a cikin Lãhira, azãba mai girma.
115Kuma Allah ɗai yake da gabas da yamma sabõda haka, inda duk aka jũyar da ku, to, a can fuskar Allah take. Lalle ne, Allah Mawadãci ne, Mai ilmi.
116Kuma suka ce: "Allah Yã riƙi(3) ɗã." Tsarki yã tabbata a gare Shi! A´a, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, dukansu, a gare Shi, mãsu ƙanƙan da kai ne.
117Mai kyautata halittar sammai da ƙasa, kuma idan Ya hukunta wani al´amari, sai kawai Ya ce masa: "Kasance." Sai ya yi ta kasancewa.
118Kuma waɗanda bã su da sani suka ce: "Don me Allah bã Ya yi mana magana, ko wata ãyã ta zo mana?"(4) Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka faɗa, kamar maganarsu. zukãtansu sun yi kamã da jũna. Lalle ne, Mun bayyana ãyõyi ga mutãne masu sakankancewa.
119Lalle ne Mun aike ka da gaskiya, kana mai bãyar da bishãra, kuma mai gargaɗi, kuma bã zã a tambaye ka ba, game da abõkan Wuta.
120Kuma Yahũdu bã zã su yarda da kõme daga gare ka ba, kuma Nasãra bã zã su yarda ba, sai kã bi irin aƙidarsu. Ka ce: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya." Kuma lalle ne idan ka bi son zũciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bã ka da, daga Allah, wani majiɓinci, kuma bãbu wani mataimaki.
121Waɗanda Muka bai wa Littãfi suna karãtunsa a kan haƙƙin karãtunsa, waɗannan suna ĩmani da shi (Alƙur´ãni). Kuma wanda ya kãfirta da shi, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
122Yã Banĩ Isrã´ĩla! Ku(1) tuna ni´imaTa wadda Na ni´imtar da ita a kanku, kuma lalle ne Nĩ, Nã fĩfĩtã ku a kan tãlikai.
123Ku ji tsõron wani yini, (a cikinsa) wani rai bã ya tunkuɗe wa wani rai kõme kuma bã a karɓar fansa daga gare shi, kuma wani cħto bã ya amfanin sa, kuma ba su zama ana taimakon su ba.
124Kuma a lõkacin da Ubangijin Ibrãhim Ya jarrabħ shi da wasu kalmõmi, sai ya cika su. Ya ce: "Lalle ne Nĩ, Mai sanya ka shugaba dõmin mutãne ne." Ya ce: "Kuma daga zũriyata." Ya ce: "AlkawarĩNa bã zai sãmu azzãlumai ba."
125Kuma a lõkacin da Muka sanya Ɗãkin ya zama makõma ga mutãne, da aminci, kuma ku riƙi wurin salla daga Maƙãmi Ibrãhĩm, kuma Muka yi alƙawari zuwa ga Ibrãhĩm, da Ismã´ila da cħwa: "Ku tsarkake ƊãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu lizimta da mãsu rukũ´i, mãsu sujada."
126Kuma a lõkacin da lbrãhĩm ya ce: "Yã Ubangijĩna! Ka sanya wannan gari amintacce, Ka azurta mutãnensa, daga ´ya´yan itãcen, wanda ya yi ĩmãni, daga gare su, da Allah da Ranar Lãhira." Allah Ya ce: "Wanda ya kãfirta ma Ina jiyar da shi dãɗi kaɗan, sa´an nan kuma Ina tĩlastã shi zuwa ga azãbar Wuta. Kuma makõmar, ta munana."
127Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm yake ɗaukaka harsãshin gini ga Ɗãkin, da Ismã´ĩla (suna cħwa:) "Yã Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Mai sani.
128"Ya Ubangijnmu! Ka sanyã mu, mu biyu, waɗanda suka sallama (al´amari) gare Ka, kuma daga zuriyarmu (Ka sanya) al´umma mai sallamãwa zuwa gare Ka, Kuma Ka nũna mana wurãren ibãdar hajjinmu, kuma Ka karɓi tũba a kanmu. Lalle ne Kai, Kai ne Mai karɓar tũba, Mai rahama.
129"Ya Ubangijinmu! Ka aiko, a cikinsu, wani manzo(1) daga gare su, yana karanta musu ãyõyinKa, kuma yana karantar da su Littãfin(2) da hikimar, kuma yana tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne Mabuwãyi Mai hikima."
130Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai.
131A lõkacin da Ubangijinsa Ya ce masa: "Ka miƙa wuya," ya ce: "Nã miƙa wuya ga Ubangijin tãlikai."
132Kuma lbrãhĩm ya yi wasiyya da ita ga ɗiyansa, kuma Ya´aƙũbu (ya yi wasiyya,suka ce:) "Yã ɗiyãna! Lalle ne, Allah Ya zãɓã muku addini don haka kada ku mutu, lalle, fãce kuna Musulmi."
133Ko kun(3) kasance halarce a lõkacin da mutuwa ta halarci Ya´aƙũbu, a lõkacin da ya ce wa ɗiyansa: "Mħne ne zã ku bauta wa daga bãyãna?" Suka ce: "Muna bauta wa Abin bautawarka kuma Abin bautawar ubanninka lbrãhĩm da lsmã´ĩla da Is´hãƙa, Ubangiji Guda, kuma mu a gare Shi mãsu miƙa wuya ne."
134Waccan, wata al´umma ce, ta riga ta shige, tana da abin da ta sanã´anta kuma kuna da abin da kuka sanã´anta, Kuma bã zã a tambaye ku ba daga abin da suka kasance suna aikatãwa.
135Kuma suka ce: "Ku kasance(1) Yahũdãwa ko Nasãra, kwã shiryu."Ka ce: "A´a aƙidar Ibrãhĩm dai, maikarkata, zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."
136Ku(2) ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã´ĩla da Is´hãka da Ya´aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu rarrabħwa a tsakãnin kõwa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, mãsu miƙa wuya ne."
137To, idan sun yi ĩmãni(3) da misãlin abin da kuka yi ĩmãni da shi, to, lalle ne sun shiryu, kuma idan sun jũya bãya, to, suna a cikin sãɓãni kawai sabõda haka Allah zai isar maka a gare su, kuma Shi ne Mai ji, Masani.
138Rinin Allah! Kuma wãne ne mafi kyau ga rini daga Allah? Kuma mu, a gare Shi, mãsu bautãwa ne.
139Ka ce: Shin kuna jãyayyar hujia ne da mu a cikin al´amarin Allah, alhãli kuwa Shi ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku, kuma muna da ayyukanmu, kuma kuna da ayyukanku, kuma mũ, a gare Shi, mãsu tsarkakħwane?
140Ko kuna cħwa: Lalle ne, Ibrãhĩm da Ismã´ĩla da Is´hãƙa da Ya´aƙũbu da Jĩkõki, sun kasance Yahũdãwa kõ kuwa Nasãra? Ka ce: Shin kũ ne kuke mafi sani kõAllah? Kuma wãne ne ya zama mafi zãlunci daga wanda ya bõye shaida a wurinsa daga Allah? Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa!
141Waccan, wata al´umma ce, tã riga ta shige, suna da abin da suka sana´anta kuma kuna da abin da kuka sana´anta kuma bã a tambayar ku daga abin da suka kasance suna aikatãwa.
142Wãwãye daga mutãne zã su ce: Mħne ne ya jũyar da su daga alƙiblarsu wadda suka kasance a kanta? Ka ce: "Allah Ɗai ne Yake da gabas da yamma, Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya."
143Kuma kamar wancan, Muka sanya ku al´umma matsakaiciya(1) dõmin ku kasance mãsu bãyar da shaida a kan mutãne. Kuma Manzo ya kasance mai shaida a kanku. Kuma ba Mu sanya Alƙibla(2) wadda ka kasance a kanta ba, fãce dõmin Mu san wanda yake biyar Manzo daga wanda yake jũyãwa a kan duga-dugansa. Kuma lalle ne, tã kasance haƙĩƙa, mai girma, sai a kan waɗanda Allah Ya shiryar. Kuma ba ya yiwuwa ga Allah Ya tõzartar da ĩmãninku.(3) Lalle ne, Allah, ga mutãne, haƙĩƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai.
144Lalle ne, Muna ganin jujjũyãwar fuskarka a cikin sama. To, lalle ne, Mu jũyar da kai ga Alƙibla wadda kake yardã da ita. Sai ka jũyar da fuskarka wajen Masallãci Tsararre, kuma inda duk kuka kasance, to, ku jũyar da fuskõkinku jiharsa. Kuma lalle ne waɗanda aka bai wa Littãfi, haƙĩƙa su, sunã sanin lalle ne, shĩ ne gaskiya, daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da suke aikatãwa.
145Kuma hakĩka, idan ka je wawaɗanda aka bai wa Littafi da dukan ãyã, bã zã su bi Alƙiblarka ba, kuma kai ba ka zama mai bin Alƙiblarsu ba, kuma sãshensu bã mai bin Alƙiblar(4) sãshe ba ne. Kuma haƙĩƙa, idan ka bi son zũciyõyinsu daga bãyan abin da ya zo maka daga ilmi, lalle ne kai, sa´an nan, haƙiƙa, azzãlumi kake.
146Waɗanda Muka bã su Littãfi, suna saninsa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Kuma lalle ne wani ɓangare daga gare su, haƙiƙa, suna ɓõyewar gaskiya alhãli kuwa sũ, suna sane.
147Gaskiya daga Ubangijinka(1) take sabõda haka, lalle kada ka kasance daga mãsu shakka.
148Kuma kõwane ɓangare yana da alƙibla wadda yake shi mai fuskantar ta ne. Sai ku yi tsħre zuwa ga ayyukan alhħri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku gabã ɗaya. Lalle ne Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne.
149Kuma daga inda ka fita, to, sai ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma lalle tabbas, shi ne gaskiya daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa ba.
150Kuma daga inda ka fita, to, ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma inda kuke duka, to, ku jũyar da fuskõkinku a wajensa, dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kanku, fãce waɗanda suka yi zãlunci daga gare su. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõrõNa kuma dõmin In cika ni´imaTa a kanku, kuma tsammãninku zã ku shiryu.
151Kamar(2) yadda Muka aika Manzo a cikinku, daga gare ku, yana karanta ãyõyinMu a gare ku kuma yana tsarkake ku, kuma yana sanar da ku Littãfi da hikima, kuma yana sanar da ku abin da ba ku kasance kuna sani ba.
152Sabõda haka, ku tuna Ni, In tunã ku, kuma ku yi gõdiya gare Ni, kuma kada ku butulce Mini.
153Ya ku waɗanda(3) suka yi ĩmãni! Ku nħmi taimako da haƙuri game da salla. Lalle ne, Allah na tãre da mãsu haƙuri.
154Kada ku ce ga waɗanda(1) ake kashħwa a cikin hanyar Allah: "Matattu ne." ôa, rãyayyu ne, kuma amma bã ku sansancħwa.
155Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa daga dũkiya da rãyuka da ´ya´yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri.
156Waɗanda suke idan wata masĩfa ta sãme su, sai su ce: "Lalle ne mũ ga Allah muke, kuma lalle ne mũ, zuwa gare Shi, muke kõmãwa."
157Waɗannan akwai albarku a kansu daga Ubangijinsu da wata rahama. Kuma waɗannan sũ ne shiryayyu.
158Lalle ne Safã da Marwa(2) suna daga wurãren ibãdar Allah, to, wanda ya yi hajin Ɗãki kõ kuwa ya yi Umra, to, bãbu laifi a kansa ga ya yi ɗawãfi gare su, su biyu. Kuma wanda ya ƙãra yin wani aikin alhħri to, lalle ne Allah Mai gõdiya ne, Masani.
159Lalle ne waɗanda suke ɓõyħwar abin da Allah Ya saukar da ga hujjõji bayyanannu, da shiriya, daga bãyan Mun bayyana shi ga mutãne, a cikin Littãfi (Alƙur´ãni), waɗannan Allah Yana la´anar su, kuma mãsu la´ana suna la´anar su.
160Sai waɗanda suka tũba,kuma suka gyãra, kuma suka bayyana, to waɗannan Ina karɓar tũba a kansu kuma Nĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
161Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai, waɗannan akwai, a kansu, la´anar Allah da Malã´iku da mutãne gabã ɗaya.
162Suna madawwama a cikinta, bã a sauƙaƙa azãba daga barinsu, kuma ba su zama ana jinkirta musu ba.
163Kuma Ubangijinku Ubangiji(3) Guda ne. Bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Mai rahama, Mai jin ƙai.
164Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da sãɓãwar dare da yini, da jirãge wadaɗnda suke gudana a cikin tħku (ɗauke) da abin da yake amfãnin mutãne, da abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta, kuma Ya wãtsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da jũyãwar iskõki da girgije hõrarre a tsakãnin sama da ƙasa; haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne mãsu yin hankali.
165Kuma akwai daga mutãne wanda yake riƙon kinãye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi ĩmãni ne mafiya tsananin so(1) ga Allah. Kuma dã waɗanda(2) suka yi zãlunci, suna ganin lõkacin da zã su ga azãba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cħwa lalle neAllah Mai tsananin azãba ne.
166A lõkacin da waɗanda aka bi suka barranta daga waɗanda suka bi, kuma suka ga azãba, kuma sabubba suka yanke da su.
167Kuma waɗanda suka bi, suka ce: "Dã lalle ne muna da wata kõmãwa (dũniya) sai mu barranta daga gare su kamar yadda suka barranta daga gare mu (dã ba su riƙi kinãyen ba)." Kamar wancan ne Allah ke nũna musu ayyukansu, suna da nadãmõmi a kansu, kuma ba su zama mãsu fita daga wutar ba.
168Yã ku mutãne!(3) Ku ci daga abin da yake a cikin ƙasa, wanda yake halal, mai dãɗi. Kuma kada ku bi zambiyõyin(4) Shaiɗan. Lalle ne shi, gare ku, maƙiyi ne bayyananne.
169Yana umurnin ku ne kawai da mugun aiki da alfãsha, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba ga Allah.
170Kuma idan aka ce musu: "Ku bi abin da Allah Ya saukar," sai su ce: ôa, muna bin abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma kõ dã ubanninsu bã su hankaltar kõme, kuma bã su shiryuwa?
171Kuma misãlin (mai kiran) waɗanda suka kãfirta kamar misãlin wanda ke yin me! me! ga abin da ba ya ji ne, fãce kira da ƙãra, kurãme, bħbãye, makafi, sabõda haka bã su hankalta.
172Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ci ku sha daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku. Kuma ku gõde wa Allah, idan kun kasance Shi kuke bauta wa.
173Kawai abin da Ya haramta a kanku, mũshe da Jini da nãman alade da abin da aka kurũrũta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsã, wanin ɗan tãwãye, kuma banda mai zãlunci, to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
174Lalle ne waɗannan da suke ɓõye abin da Allah Ya saukar daga Littãfi, kuma suna sayen kuɗi kaɗan da shi; waɗannan bã su cin kome a cikin cikkunansu fãce wuta, kuma Allah bã zai yi musu magana ba a Rãnar Ƙiyãma, kuma bã zai tsarkake su ba, kuma suna da azãba mai raɗaɗi.
175Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, kuma azãba da gãfara. To, me ya yi haƙurinsu a kan Wuta!
176Wancan dõmin lalle ne Allah Ya saukar da Littafi da gaskiya, kuma lalle ne waɗanda suka sãɓã a cikin Littãfin, haƙĩƙa, suna a cikin sãɓãni mai nĩsa.
177Bai zama addini(1) ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã´iku da Littattafan sama da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da salla, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa.
178Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta, a kanku, yin ƙisãsi(2) a cikin kasassu. ɗa da ɗa kuma bãwa da bãwa, kuma mace da mace, to, wanda aka yi rangwamen wani abu gare shi daga ɗan´uwansa to a bi da alhħri da biya zuwa gare, shi da kyautatãwa. Wancan sauƙaƙewa ne daga Ubangijinku, kuma rahama ce. To, wanda ya yi zãlunci a bãyan wancan, to, yana da azãba mai raɗaɗi.
179Kuma kuna da rãyuwa a cikin ƙisãsi, yã ma´abuta hankula; tsammãninku, zã ku yi taƙawa.
180Kuma an wajabta,(3) a kanku idan mutuwa ta halarci ɗayanku, idan ya bar wata dũkiya, wasiyya dõmin mahaifa da dangi bisa ga abin da aka sani; wajabce a kan mãsu taƙawa.
181To, wanda ya musanya masa a bãyan ya ji shi, to, kawai laifinsa yana a kan waɗanda suke musanya shi. Lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani.
182To, wanda ya ji tsõron karkata ko kuwa wani zunubi daga mai wasiyyar, sai ya yi sulhi a tsakãninsu to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
183Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta(1) azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku, zã ku yi taƙawa,
184Kwanuka ƙidãyayyu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuwa yana a kan tafiya, sai (ya biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan waɗanda suke yin sa da wahala akwai fansa; ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙãra alhħri to, shi ne mafi alhħri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alhħri a gare ku idan kun kasance kuna sani.
185Watan Ramalãna ne wanda aka saukar da Alƙur´ãni a cikinsa yana shiriya ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya da rarrabħwa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma dõmin ku cika adadin, kuma dõmin ku girmama Allah a kan Yã shiryar da ku, kuma tsammãninku, zã ku gõde.
186Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirã Ni.(2) Sabõda haka su nħmi karɓawaTa, kuma su yi ĩmãni da Ni: tsammãninsu, su shiryu.
187An halatta a gare ku, a daren azumi, yin jima´i(1) zuwa ga matanku, sũ tufa ne a gare ku, kuma kũ tufa ne a gare su, Allah Yã sani lalle ne ku kun kasance kuna yaudarar kanku. Sabõda haka Yã karɓi tũbarku, kuma Yã yãfe muku. To, yanzu ku rungume su kuma ku nħmi abin da Allah yã rubũta muku. Kuma ku ci kuma ku sha har sĩlĩli fari ya bayyana a gare ku daga sĩlĩli baƙi daga alfijiri, sa´an nan kuma ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku rungume su alhãli kuna mãsu itikãfi a cikin masallãtai. Waɗancan iyãkokin Allah ne: don haka kada ku kusancesu, kamar haka ne Allah Yake bayyana ãyõyinSa ga mutãne: tsammãninsu, zã su yi taƙawa.
188Kada ku ci dukiyõyinku(2) a tsakãninku da ƙarya, kuma ku sãdu da ita zuwa ga mahukunta dõmin ku ci wani yanki daga dũkiyõyin mutãne da zunubi alhãli kuwa kũ, kuna sane.
189Kuma suna tambayar ka(3) daga jirajiran wata. Ka ce: "Su lõkatai ne dõmin mutãne da haji, kuma bã addini ba ne ku je wa gidãje daga bãyansu: kuma amma abin da yake addini shi ne wanda ya yi taƙawa. Kuma ku je wa gidãje daga ƙõfõfinsu, kuma ku bi Allah da taƙawa: tsammãninku, ku ci nasara.
190Kuma ku yãƙi waɗanda(4) suke yãƙinku, a cikin hanyar Allah, kuma kada ku yi tsõkana, lalle ne Allah bã Ya son mãsu tsõkana.
191Kuma ku yãƙe su inda kuka sãme su, kuma ku fitar da su daga inda suka fitar da ku. Kuma fitina ita ce mafi tsanani daga kisa. Kuma kada ku yãƙe su a wurin Masallãci Tsararre (Hurumin Makka) fãce fa idan sun yãƙe ku a cikinsa. To, idan sun yãƙe ku, sai ku yãƙe su. Kamar wancan ne sakamakon kãfirai yake.
192Sa´an nan idan sun hanu, to, lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
193Kuma ku yãƙe(1) su har ya zama wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini ya zama na Allah. Sa´an nan idan sun hanu to bãbu tsõkana fãce a kan azzãlumai.
194Watan alfarma da wani watan alfarma alfarmõmi mãsu dũkar jũna ne. Sabõda haka wanda ya yi tsõkana a kanku, sai ku yi tsokana a kansa da misãlin abin da ya yi tsõkana a kanku. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Yana tãre da mãsu taƙawa.
195Kuma ku ciyar(2) a cikin hanyar Allah. Kuma kada ku jefa kanku da hannayenku, zuwa ga halaka. Kuma ku kyautata; lalle ne, Allah Yana son mãsu kyautatãwa.
196Kuma ku cika(3) hajji da umra dõmin Allah. To idan an kange ku, to, ku bãyar da abin da ya sauƙaƙa na hadaya. Kuma kada ku aske kãwunanku, sai hadaya ta kai wurinta. To, wanda ya kasance majinyaci daga cikinku, kõ kuwa akwai wata cũta daga kansa (ya yi aski) sai fansa (fidiya) daga azumi ko kuwa sadaka ko kuwa yanka. To, idan kuna cikin aminci to, wanda ya ji dãdi da umra zuwa haji, sai ya biya abin da ya sauƙaƙa daga hadaya, sa´an nan wanda bai sãmu ba, sai azumin yini uku a cikin haji da bakwai idan kun kõma, waɗancan gõma ne cikakku. Wancan yana ga wanda iyãlinsa ba su kasance mazaunan Masallãci Tsararre ba. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa Allah Mai tsananin uƙũba ne.
197Hajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji(1) a cikinsu to bãbu jimã´i kuma bãbu fãsiƙanci, kuma bãbu jãyayya a cikin hajji. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, Allah Ya san shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi alhħrin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma´abuta hankula.
198Bãbu laifi a kanku ga ku nħmi falala daga Ubangijinku. Sa´an nan idan kun malãlo daga Arafãt, sai ku yi ta ambatar Allah a wurin Mash´aril Harãmi kuma ku tuna Shi kamar shiriyar da Ya yi muku kuma lalle ne kun kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga ɓatattu.
199Sa´an nan kuma ku malãlo daga inda mutãne suke malalowa. Kuma ku nemi gafara ga Allah. Lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
200To, idan kun ƙãre ayyukan hajji, sai ku ambaci Allah kamar ambatarku ga ubanninku, kõ kuwa mafi tsanani ga ambato. To, daga cikin mutãne akwai wanda yake cħwa: "Ya Ubangjinmu! Ka bã mu a cikin dũniya! Kuma bã ya da wani rabo a cikin Lãhira.
201Kuma daga gare su akwai wanda yake cħwa: "Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar Wuta!"
202Waɗannan suna da rabo daga abin da suka sanã´anta; kuma Allah Mai gaggãwar sakamako da yawa ne.
203Kuma ku ambaci Allah a cikin kwanuka ƙidayayyu.(1) To, wanda ya yi gaggawa a cikin kwana biyu, to, bãbu laifi a kansa, kuma wanda ya jinkirta, to, bãbu laifi a kansa, ga wanda ya yi taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma ku sani cewa lalle ne kũ, zuwa gare Shi ake tãrã ku.
204Kuma akwai daga mutãne(2) wanda maganarsa tana bã ka sha´awa a cikin rãyuwar dũniya, alhãli yanã shaidar da Allah a kan abin da yake cikin zuciyarsa, kuma shi mai tsananin husũma ne.
205Kuma idan ya jũya sai ya yi gaggawa a cikin ƙasa dõmin ya yi ɓarna a cikinta, kuma ya halaka shũka da ´ya´yan dabbõbi. Kuma Allah bã Ya son ɓarna.
206Kuma idan an ce masa: "Ka ji tsõron Allah," sai girman kai da yin zunubi ya ɗauke shi. To abin da yake mai isarsa Jahannama ce. Kuma haƙĩƙa, shimfiɗa tã munana.
207Kuma akwai daga mutãne(3) wanda yake sayar da ransa, dõmin nħman yardar Allah: Kuma Allah Mai tausayi ga bãyi ne.
208Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Ku shiga cikin Musulunci gabã ɗaya; kuma kada ku bi zambiyõyin Shaiɗan; lalle ne shĩ a gare ku maƙiyine, bayyananne.
209To, idan kun karkace daga bayan hujjõji bayyanannu sun zo muku to ku sani cħwa lalle ne Allah, Mabuwãyi ne, Mai hikima.
210Shin suna jira, fãce dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwõyi na girgije, da malã´iku, kuma an hukunta al´amarin? Kuma zuwa ga Allah al´amurra ake mayar da su.
211Ka tambayi Banĩ Isrã´ila, da yawa Muka bã su daga ãyõyi bayyanannu. Kuma wanda ya musanya ni´imar Allah daga bãyan tã je masa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
212An ƙawata rãyuwar dũniya ga waɗanda suka kãfirta, kuma suna izgili daga waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli waɗanda suka yi taƙawa suna bisa gare su, a Rãnar Ƙiyãma. Kuma Allah Yana azurta wanda Yake so, bã da lissãfi ba.
213Mutãne sun kasance al´umma guda. Sai Allah Ya aiki annabãwa suna mãsu bãyar da bishãra kuma mãsu gargaɗi; kuma Ya saukar da Littãfi da gaskiya tãre da su dõmin (Littãfin) ya yi hukunci a tsakãnin mutãnen a cikin abin da suka sãɓã wa jũna a cikinsa. kuma bãbu wanda ya sãɓã, a cikinsa, fãce waɗanda aka bai wa shi daga bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu dõmin zãlunci a tsakãninsu. Sai Allah Ya shiryar da waɗanda suka yi ĩmani ga abin da suka sãɓã a cikinsa daga gaskiya da izninSa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Yake so, zuwa ga hanya madaidaiciya.
214Ko kuna zaton ku shiga Aljanna kuma tun misãlin waɗanda suka shige daga gabãninku bai zo muku ba? Wahalõli da cũta sun shãfe su, kuma aka tsõratar da su har manzonsu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi su ce: "Yaushe taimakon Allah zai zo?" To! Lalle ne, taimakon Allah yana kusa!
215Suna tambayar ka mħne ne zã su ciyar. Ka ce: Abin da kuka ciyar daga alhħri sai ga mahaifa(1) da mafi kusantar dangantaka da marãyu da matalauta da ɗan hanya. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, to, lalle ne, Allah gare shi Masani ne.
216An wajabta(1) yãƙi a kanku, alhãli kuwa shi abin ƙi ne a gare ku, akwai fãtar cħwa ku ƙi wani abu, alhãli shi ne mafi alhħri a gare ku, kuma akwai fãtar cħwa kuna son wani abu alhãli kuwa shi ne mafi sharri a gare ku. Kuma Allah ne Yake sani, kuma kũ ba ku sani ba.
217Suna tambayar ka game da Watan Alfarma: yin yãki a cikinsa. Ka ce: "Yin yãƙi a cikinsa babban zunubi ne, kuma hani daga hanyar Allah, da kuma kãfirci da Shi, da kuma da Masallaci Tsararre, da Kuma fitar da mutãnensa daga gare shi, shi ne mafi girman zunubi a wurin Allah." Kuma fitina ita ce mafi girma daga kisa. Kuma bã su gushħwa suna yãƙinku har su mayar da ku daga barin addininku idan za su iya. Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin addininsa har ya mutu alhãli kuwa yana kãfiri, to, waɗannan ayyukansu sun ɓãci a cikin dũniya da Lãhira. Kuma waɗannan abõkan Wuta ne, sũ a cikinta madawwama ne.
218Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, da waɗanda suka yi hijira kuma suka yi jihãdi a cikin hanyar Allah waɗannan suna fãtar (sãmun) rahamar Allah kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
219Suna tambayar ka game da giya da cãcã.(2) Ka ce: "A cikinsu akwai zunubi mai girma da wasu amfãnõni ga mutãne, kuma zunubinsu ne mafi girma daga amfaninsu." Kuma suna tambayar ka mħne ne zã su ciyar; ka ce: "Abin da ya rage."(3) Kamar wancan ne Allah Yake bayyanawar ãyõyi a gare ku; tsammãninku, kuna tunãni.
220A cikin dũniya da Lãhira. Kuma suna tambayar ka game da marãyu.(1) Ka ce: "Kyautatãwa gare su ne mafi alhħri, kuma idan kun haɗa da su (wajen abinci), to, ´yan´uwanku ne; kuma Allah Yana sanin mai ɓãtãwa daga mai kyautatãwa. Kuma dã Allah Yã so, dã Ya tsananta muku. Lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
221Kuma kada ku auri mãtã(2) mushirikai sai sun yi ĩmãni: Kuma lalle ne baiwa mũmina ita ce mafi alhħri daga ɗiya kãfira, kuma kõ da tã bã ku sha´awa. Kuma kada ku aurar wa maza mushirikai sai sun yi ĩmãni, kuma lalle ne bãwa mũmini shi ne mafi alhħri daga da mushiriki, kuma kõ da yã bã ku sha´awa, waɗannan suna kira ne zuwa ga wuta kuma Allah Yana kira zuwa ga Aljanna da gãfara da izninsa. Kuma Yana bayyana ãyõyinsa ga mutãne; tsammãninsu suna tunãwa.
222Kuma suna tambayar ka game da haila(3) Ka ce: Shi cũta ne. Sabõda haka ku nĩsanci mãta a cikin wurin haila kuma kada ku kusance su sai sun yi tsarki. To, idan sun yi wanka sai ku je musu daga inda Allah Ya umurce ku. Lalle ne Allah Yana son mãsu tũba kuma Yana son mãsu tsarkakħwa.
223Mãtanku gõnaki ne a gare ku,(4) sabõda haka ku je wa gõnakinku yadda kuka so. Kuma ku gabãtar (da alheri) sabõda kanku, ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne kũ mãsu haɗuwa da Shi ne. Kuma ka bãyar da bishãra ga mũminai.
224Kuma kada ku sanya(5) Allah kambu ga rantsuwõyinku dõmin kada ku yi wani alhħri, kuma ku yi taƙawa, kuma ku yi wani gyara tsakãnin mutãne, kuma Allah Mai jĩ ne, Masani.
225Allah ba Ya kãmã ku da laifi sabõda yãsasshiya a cikin rantsuwõyinku. Kuma amma Yana kama ku sabõda abin da zukãtanku(1) suka sanã´anta. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri.
226Ga waɗanda suke yin rantsuwa(2) daga matansu akwai jinkirin watã huɗu. To, idan sun kõma, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
227Kuma idan sun yi niyyar saki, to, lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani.
228Kuma mãtã waɗanda(3) aka saki aurensu, suna jinkiri da kansu tsarki uku. Kuma bã ya halatta a gare su, su ɓõye abin da Allah Ya halitta a cikin mahaifunsu, idan sun kasance suna yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Kuma mazan aurensu su ne mafiya haƙƙi ga mayar da su a cikin wancan, idan sun yi nufin gyãrawa. Kuma sũ mãtan suna da kamar abin da yake a kansu, yadda aka sani. Kuma maza suna da wata daraja a kansu (su mãtan). Kuma Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
229Saki sau biyu(4) yake, sai a riƙa da alh ħri, ko kuwa a sallama bisa kyautatãwa. Kuma ba ya halatta a gare ku (maza) ku karɓe wani abu daga abin da kuka bã su, fãce fa idan su (ma´auran) na tsõron bã zã su tsayar da iyãkõkin Allah ba. Idan kun (danginsu) ji tsõron bã zã su tsayar da iyãkõkin Allah ba, to, bãbu laifi a kansu a cikin abin da ta yi fansa da shi. Waɗancan iyãkõkin Allah ne sabõda haka kada ku kħtare su. Kuma wanda ya ƙħtare iyãkõkin Allah, to waɗannan su ne azzãlumai.
230Sa´an nan idan ya sake ta (na uku), to, bã ta halatta a gare shi, daga bãya, sai tã yi jima´i da wani miji waninsa. Sa´an nan idan (sãbon mijin, watau na biyu) ya sake ta, to, bãbu laifi a kansu ga su kõma wa (auren) jũna,idan sun (mijin farko da matar) yi zaton cħwa zã su tsayar da iyãkõkin Allah, kuma waɗancan dõkõkin Allah ne Yana bayyana su ga mutãne waɗanda suke sani.
231Kuma idan kun saki mãta, sa´an nan suka isa ga ajalinsu (iddarsu), sai ku riƙe su da alhħri ko ku sallame su da alhħri, kuma kada ku riƙe su a kan cũtarwa dõmin ta tsawaita idda. Kuma wanda ya aikata wancan, to, haƙĩƙa, yã zãlunci kansa. Kuma kada ku riƙi ãyõyin Allah da izgili. Kuma ku tuna ni´imar Allah da abin da Ya saukar a kanku na Littãfi da hikima. Yana yi muku wa´azi da shi. Kuma ku bi Allah da takawa kuma ku sani cewa lalle ne Allah ga dukan kõme Masani ne.
232Kuma idan kuka saki mãta, har suka isa ga ajalinsu (iddarsu), to, kada ku (waliyyansu) hana su, su auri mazansu (da suka sake su) idan sun yarda da jũna a tsakãninsu (tsõhon miji da tsõhuwar mãta) da alhħri. Wancan ana yin wa´azi da shi ga wanda ya kasance daga gare ku yana ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Wancan ne mafi mutunci a gare ku, kuma mafi tsarki. Kuma Allah Yana sani, kuma kũ ba ku sani ba.
233Kuma mãsu haifuwa (sakakku)(1) suna shãyar da abin haifuwarsu shħkara biyu cikakku ga wanda ya yi nufin ya cika shãyarwa. Kuma ciyar da su da tufãtar da su yana a kan wanda aka haifar masa da alhħri. Bã a kallafa wa rai fãce iyãwarsa. Bã a cũtar da uwa game da ɗanta, kuma bã a cũtar da uba game da ɗansa, kuma a kan magãji akwai misãlin wancan. To, idan suka yi nufin yãye, a kan yardatayya daga gare su, da shãwartar jũna, to bãbu laifi a kansu. Kuma idan kun yi nufin ku bãyar da ɗiyanku shãyarwa, to, bãbu laifi a kanku idan kun mĩƙa abin da kuka zo da shi bisa al´ãda. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani ne.
234Kuma waɗanda suke mutuwa(1) daga gare ku suna barin mãtan aure, mãtan suna jinkiri da kansu wata huɗu da kwãna goma. To, idan sun isa ga ajalinsu, to, bãbu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu ga al´ãda. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne.
235Kuma bãbu laifi a kanku a cikin abin da kuka gitta(2) da shi daga nħman auren mãtã ko kuwa kuka ɓõye a cikin zukatanku. Allah Ya san cħwa lalle ne ku za ku ambata musu (shi). Kuma amma kada ku yi wa jũna alkawari da shi a ɓõye, fãce dai ku faɗi magana sananniya. Kuma kada ku ƙulla niyyar daurin auren sai littãfin (idda) ya kai ga ajalinsa. Kuma ku sani cħwa lalle ne Allah Yana sanin abin da yake cikin zukatanku, sabõda haka ku ji tsõronsa. Kuma ku sani cewa Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri.
236Kuma bãbu laifi(3) a kanku idan kun saki mãtã matuƙar ba ku shãfe su ba, kuma ba ku yanka musu sadãki ba. Kuma ku bã su kyautar dãɗaɗãwa, a kan mawadãci gwargwadonsa, kuma a kan maƙuntaci gwargwadonsa; dõmin dãɗaɗrwa, da alhħri, wãjibi ne a kan mãsu kyautatãwa.
237Kuma idan kuka sake su daga gabãnin ku shãfe su, alhãli kuwa(4) kun yanka musu sadãki, to, rabin abin da kuka yanka fãce idan sun yãfe, kõ wanda ɗaurin auren yake ga hannunsa ya yãfe. Kuma ku yãfe ɗin ne mafi kusa da taƙawa. Kuma kada ku manta da falala a tsakãninku. Lalle ne Allah ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne.
238Ku tsare(1) lõkatai a kan sallõli da salla mafificiya. Kuma ku tsayu kuna mãsu ƙanƙan da kai ga Allah.
239To, idan kun ji tsõro, to (ku dai yi salla gwargwadon hali) da tafiya ƙasa kõ kuwa a kan dabbobi. Sa´an nan idan kun amince sai ku ambaci Allah, kamar yadda Ya nũna muku abin da ba ku kasance kuna sani ba.
240Kuma waɗanda suke mutuwa(2) daga gare ku, alhãli suna barin mãtan aure, wasiyya ga mãtan aurensu da dãɗaɗãwa zuwa ga shekara guda bãbu fitarwa, to, idan sun fita to bãbu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu daga abin da aka sani, kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.
241Kuma waɗanda aka saki suna da dãɗaɗãwa gwargwadon hãli, wajabce a kan mãsu taƙawa(3) .
242Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ãyõyinSa; tsammãninku, kuna hankalta.
243Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suka fita(4) daga gidãjensu, alhãli kuwa sũ dubbai ne, dõmin tsõron mutuwa? Sai Allah Ya ce musu: "Ku mutu." Sa´an nan kuma Ya rãyar da su, lalle ne Allah, haƙĩƙa Ma´abũcin falala a kan mutãne ne, kuma amma mafi yawan mutãne bã su gõdħwa.
244Kuma ku yi yãƙi a cikin hanyar Allah, kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Mai jĩ ne, Masani.
245Wãne ne wanda(5) zai bai wa Allah rance, rance mai kyau, dõmin Ya riɓanya masa, riɓanyãwa mai yawa? Kuma Allah Shi ne ke damƙewa, kuma yana shimfiɗawa, kuma zuwa a gare Shi ake mayar da ku.
246Shin, ba ka gani ba zuwa ga wasu mashãwarta(1) daga Bani Isrã´ĩla daga bãyan Mũsã, a lõkacin da suka ce ga wani annabi nãsu: "Naɗã mana sarki, mu yi yãƙi a cikin hanyar Allah." Ya ce: "Ashe, akwai tsammãninku idan an wajabta yãƙi a kanku cħwa bã zã ku yi yãƙin ba?" Suka ce: "Kuma mħne ne a gare mu, ba zã mu yi yãƙi ba, a cikin hanyar Allah, alhãli kuwa, haƙiƙa, an fitar da mu daga gidãjenmu da ɗiyanmu?" To, a lõkacin da aka wajabta yãƙin a kansu, suka jũya, sai kaɗan daga gare su. Kuma Allah Masani ne ga azzãlumai.
247Kuma annabinsu(2) ya ce musu: "Lalle ne, Allah ya naɗa muku Ɗãlũta(3) ya zama sarki." Suka ce: "Yãya ne sarauta zã ta kasance a gare shi, a kanmu, alhãli kuwa mũ ne mafi cancanta da sarauta daga gare shi, kuma ba a bã shi wata wadata ba daga dũkiya?" Ya ce: "Lalle ne, Allah Yã zãɓe shi a kanku, kuma Ya ƙãra masa yalwa a cikin ilmi da jiki. Kuma Allah Yana bãyar da mulkinSa ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadaci ne, Masani.
248Kuma annabinsu ya ce musu: "Lalle ne alãmar mulkinSa ita ce akwatin(4) nan ya zo muku, a cikinsa akwai natsuwa daga Ubangijinku da sauran kaya daga abin da Gidan Mũsã da Gidan Hãrũna suka bari malã´iku suna ɗaukarsa. Lalle ne a cikin wancan akwai alãma a gare ku (ta naɗin Ɗãlũta daga Allah ne) idan kun kasance mãsu ĩmãni."
249A lõkacin da Ɗãlũta ya fita(1) da rundunõnin, ya ce: "Lalle ne Allah Mai jarrabarku ne da wani kõgi. To, wanda ya sha daga gare shi, to, ba shi daga gare ni, kuma wanda bai ɗanɗane shi ba to lalle ne shi, yana daga gare ni, fãce, wanda ya kamfata, kamfata guda da hannunsa." Sai suka sha daga gare shi, fãce kaɗan daga gare su. To, a lõkacin da (Ɗãlũta) ya ƙħtare shi, shi da waɗanda suka yi ĩmani tãre da shi, (sai waɗanda suka sha) suka ce: "Babu ĩko a gare mu yau game da Jãlũta da rundunõninsa."Waɗanda suka tabbata cħwa lalle sũ mãsu gamuwa ne da Allah, suka ce: "Da yawa ƙungiya kaɗan ta rinjayi wata ƙungiya mai yawa da iznin Allah, kuma Allah Yana tãre da mãsu haƙuri."
250Kuma a lõkacin da suka(2) bayyana ga Jãlũta da rundunoninsa, suka ce: "Yã Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu kuma Ka tabbatar da sãwayenmu, kuma Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai."
251Sai suka karya su da iznin Allah. Kuma Dãwudu ya kashe Jãlũta, kuma Allah Ya bã shi mulki da hikima kuma Ya sanar da shi daga abin da Yake so. Kuma bã dõmin tunkuɗħwar Allah ga mutãne sãshensu da sãshe ba lalle ne dã ƙasa tã ɓãci; kuma amma Allah Ma´abũcin falala ne a kan tãlikai.
252Waɗancan ayõyin Allah ne: Muna karanta su a kanka da gaskiya: Kuma lalle ne kai, hakĩka, kana daga manzanni.
253Waɗancan manzannin(1) Mun fĩfĩta sãshensu a kan sãshe: Daga cikinsu akwai wanda Allah Ya yi masa magana; kuma Ya ɗaukaka sãshensu da darajõji; kuma Muka bai wa Ĩsã dan Maryama hujjõji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafã shi da Rũhi mai tsarki. Kuma dã Allah Yã so dã waɗanda suke daga bãyansu, bã zã su yi yãƙi ba, daga bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu. Kuma amma sun sãɓa wa jũna, sabõda haka daga cikinsu akwai wanda ya yi ĩmãni, kuma daga cikin su akwai wanda ya kãfirta. Kuma dã Allah Yã so dã bã zã su yãƙi jũna ba, kuma amma Allah Yana aikata abin da Yake nufi.
254Ya ku waɗanda(2) suka yi ĩmãni! Ku ciyar daga abin da Muka arzuta ku daga gabãnin wani yini ya zo bãbu ciniki a cikinsa kuma bãbu abũta, kuma bãbu cħto, kuma kãfirai sũ ne azzãlumai.
255Allah, bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Rãyayye, Mai tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, kuma barci bã ya kãma Shi, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin cħto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu. Kuma bã su kħwayħwa da kõme daga ilminSa, fãce da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma.
256Bãbu tĩlastãwa(3) a cikin addini, haƙĩƙa shiriya tã bayyana daga ɓata; Sabõda haka wanda ya kãfirta da Ɗãgũta kuma ya yi ĩmãni da Allah, to, haƙĩƙa, yã yi riƙo ga igiya amintacciya, bãbu yankħwa agare ta. Kuma Allah Mai ji ne, Masani.
257Allah Shi ne Masõyin waɗanda suka yi ĩmãni; Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske, kuma waɗanda suka kãfirta, masõyansu Ɗãgũtu ne; suna fitar da su daga haske zuwa ga duffai. Waɗannan abokan Wuta ne, sũ a cikinta madawwama ne.
258Shin, ba ka gani(1) ba zuwa ga wanda ya yi hujjatayya da Ibrãhĩm a cikin (al´amarin) Ubangijinsa dõmin Allah Yã bã shi mulki, a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Ubangijina Shi ne Wanda Yake rãyawa kuma Yana matarwa." Ya ce: "Nĩ ina rãyarwa kuma ina matarwa." Ibrãhĩm ya ce: "To, lalle ne Allah Yana zuwa da rana daga gabas: To, ka zo da ita daga yamma." Sai aka ɗimautar da wanda ya kãfirta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
259Kõ kuwa(2) wanda ya shũɗe a kan wata alƙarya, alhãli kuwa tana wõfintacciya a kan gadãjen rħsunanta. Ya ce: "Yaya Allah zai rãyar da wannan a bãyan mutuwarta." Sai Allah Ya matar da shi, shħkara ɗari; sa´an nan kuma ya tãyar da shi. Ya ce: "Nawa ka zauna?" Ya ce: "Na zauna yini ɗaya ko kuwa rabin yini." Ya ce: "A´a kã zauna shħkara ɗari." To, ka dũba zuwa ga abincinka, da abin shanka, (kõwanensu) bai sãke ba, kuma ka dũba zuwa ga jãkinka, kuma dõmin Mu sanya ka wata ãyã ga mutãne. Kuma ka duba zuwa ga ƙasũsuwa yadda Muke mõtsarda su sa´an nan kuma Mu tufãtar da su, da nãma", To, a lõkacin da (abin) ya bayyana a gare shi, ya ce: "Ina sanin cħwa lalle Allah a kan dukan kõme Mai ĩkõn yi ne."
260Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nũna mini yadda Kake rãyar da matattu." Ya ce: "Shin, kuma ba ka yi ĩmãni ba?" Ya ce: "Na´am! Kuma amma dõmin zũciyãta, ta natsu." Ya ce: "To ka riƙi huɗu daga tsuntsãye, ka karkatar da su zuwa gare ka, ka yanka su, sa´an nan kuma ka sanya juzu´i daga gare su a kan kõwane dũtse, sa´an nan kuma ka kira su zã su zo maka gudãne. Kuma ka sani cħwa lalle Allah Mabuwãyi ne, Masani."
261Sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, kamar sifar ƙwãyã ce wadda ta tsirar da zangarniya bakwai, a cikin kõwace zangarniya akwai ƙwãya ɗari. Kuma Allah Yana riɓinyawa ga wanda Ya so. Kuma Allah Mawadãci ne, Masani.
262Waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, sa´an nan kuma bã su biyar wa abin da suka ciyar ɗin da gõri, ko cũta, suna da sakamakonsu a wurin ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba.
263Magana mai kyau da gãfartawa su ne mafi alhħri daga sadaka wadda wata cũtarwa take biyar ta. Kuma Allah Wadatacce ne, Mai haƙuri.
264Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ɓãta sadakõkinku da gõri da cũtarwa, kamar wanda yake ciyar da dũkiyarsa dõmin nũna wa mutãne, kuma bã ya yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. To, abin da yake misãlinsa, kamar falalen dũtse ne, a kansa akwai turɓãya, sai wãbilin hadari(1) ya sãme shi, sai ya bar shi ƙanƙara. Bã su iya amfani da kõme daga abin da suka sanã´anta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne kãfirai.
265Kuma sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyarsu dõmin nħman yardõjin Allah, kuma da tabbatarwa daga kansu, kamar misãlin lambu ne a jigãwa wadda wãbilin hadari ya sãmu, sai ta bãyar da amfãninta ninki biyu To, idan wãbili bai sãme ta ba, sai yayyafi (ya ishe ta). Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Mai gani ne.
266Shin ɗayanku nã son cħwa wani lambu ya kasance a gare shi daga dabĩnai da inabõbi´ marħmari suna gudãna daga ƙarƙashinsa, yana da, a cikinsa daga kõwane ´ya´yan itãce, kuma tsũfa ya sãme shi, alhãli kuwa yana da zũriyya masu rauni sai gũguwa wadda take a cikinta akwai wuta, ta sãme shi, har ta ƙõne? Kamar wancan ne Allah Yana bayyanãwar ãyõyi a gare ku, tsammãninku kuna tunãni.
267Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ciyar daga mai kyaun abin da kuka sanã´anta, kuma daga abin da Muka fitar sabõda ku daga ƙasa, kuma kada ku yi nufin mummuna ya zama daga gare shi ne kuke ciyarwa, alhãli kuwa ba ku zama mãsu karɓarsa ba fãce kun runtse ido a cikinsa. Kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Mawadãci ne, Gõdadde.
268Shaiɗan yana yi muku alƙawarin talauci, kuma yana umurnin ku da alfasha,(1) kuma Allah Yana yi muku alƙawarin gãfara daga gare shi da ƙãri, kuma Allah Mawadãci ne, Masani.
269Yana bãyar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an bã shi alhħri mai yawa. Kuma bãbu mai tunãni fãce ma´abuta hankula.
270Kuma abin da kuka ciyar daga ciyarwa, kõ kuka cika alwãshi daga wani bãkance, to, lalle ne, Allah Yana sanin sa. Kuma azzãlumai bã su da wasu mataimaka.
271Idan kun nũna sadakõki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓõye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alhħri a gareku, kuma Yana kankarħwa, daga barinku, daga miyãgun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne.
272Shiryar da su bã ya a kanka, kuma amma Allah Shi ne Yake shiryar da wanda Yake so, kuma abin da kuka ciyar daga alhħri, to, dõmin kanku ne, kuma bã ku ciyarwa, fãce dõmin nħman yardar Allah, kuma abin da kuke ciyarwa daga alhħri zã a cika lãdarsa zuwa gare ku, alhãli kuwa kũ bã a zãluntarku.
273(Ciyarwar a yĩ ta) ga matalautan(1) nan waɗanda aka tsare a cikin hanyar Allah, ba su iya tafiyar fatauci a cikin ƙasa, jãhilin hãlinsu yana zaton su wadãtattu sabõda kãmun kai kana sanin su da alãmarsu, ba su rõƙon mutãne da nãcħwa. Kuma abin da kuka ciyar daga alhħri, to, lalle Allah gare shi Masani ne.
274Waɗanda suke ciyar da dukiyõyinsu, a dare da yini, ɓõye da bayyane, to suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu. Kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba.
275Wadanda suke cin ribã(1) ba su tashi, fãce kamar yadda wanda da Shaiɗan yake ɗimautarwa daga shafa yake tashi. Wancan, dõmin lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba yake."Kuma Allah Ya halatta ciniki kuma Ya haramta riba. To, wanda wa´azi daga Ubangijinsa, ya je masa, sa´an nan ya hanu, to yana da abin da ya shige, kuma al´amarinsa (ana wakkala shi) zuwa ga Allah. Kuma wanda ya kõma, to, waɗannan sũ ne abõkan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne.
276Allah Yana shãfe albarkar riba, kuma Yana ƙãra sadakõki. Kuma Allah bã Ya son dukan mai yawan kãfirci, mai zunubi.
277Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka, suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba.
278Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage daga riba, idan kun kasance mãsu ĩmãni.
279To, idan ba ku aikata ba to, ku sani fa da akwai yãƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tũba to kuna da asalin dũkiyõyinku, bã ku zãlunta, kuma bã a zãluntar ku.
280Kuma idan ma´abucin wahala ya kasance (mawahalci) to, jinkirtãwa ake yi zuwa ga sauƙin al´amarinsa, kuma dã kun yi sadaka, shi ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kuna sani.
281Kuma ku ji tsõron wani yini wanda ake mayar da ku a cikinsa zuwa ga Allah, sa´an nan kuma a cika wa kõwane rai abin da ya sanã´anta, kuma sũ bã a zãluntar su.
282Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi mu´ãmalar bãyar da bãshi zuwa ga wani ajali ambatacce, sai ku rubũta shi. Kuma wani marubuci ya yi rubũtu a tsakaninku da ãdalci. Kuma kada marubũci ya ki rubũtãwa, kamar yadda Allah Ya sanar da shi, sai ya rubũta. Kuma wanda bãshin yake a kansa sai ya yi shibta, kuma ya ji tsõron Allah, Ubangijinsa, da taƙawa, kuma kada ya rage wani abu daga gare shi. To, idan wanda bãshin yake a kansa yã kasance wãwã ne kõ kuwa rarrauna, kõ kuwa shi bã ya iya shibta, to, sai waliyyinsa ya yi shibtar da ãdalci. Kuma ku shaidar da shaidu biyu daga mazanku, to, idan ba su zama maza biyu ba, to, namiji guda da mãtã biyu, daga waɗanda kuke yarda da su daga shaidun dõmin mantuwar ɗayansu, sai gudarsu ta mazãkũtar(1) da ɗayar. Kuma kada shaidun su ƙi, idan an kira su. Kuma kada ku ƙõsa ga rubũta shi, ƙarami ya kasance kõ babba, zuwa ajalinsa. Wancan ne mafi ãdalci a wurin Allah kuma mafi tsayuwa ga shaida, kuma mafi kusa ga rashin shakkarku. Sai idan ya kasance fatauci ne halartacce wanda kuke għwayarwa da shi hannu da hannu a tsakãninku to bãbu laifi a kanku, ya zama ba ku rubũta shi ba. Kuma ku shaidar idan kun yi sayayya. Kuma kada a wahalarda marubuci, kuma kada a wahalar da shaidu kuma idan kun aikata to, lalle ne, shi fãsiƙanci ne game da ku. Kuma ku bi Allah da takƙawa, kuma Allah Ya sanar da ku. Kuma Allah ga dukan kõme Masani ne.
283Kuma idan kun kasance a kan tafiya, kuma ba ku sami marubũci ba, to, a bãyar da jingina karɓaɓɓiya (ga hannu). To, idan sãshenku ya amince wa sãshe, to, wanda aka amincħ wan nan sai ya bãyar da amãnarsa, kuma ya bi Allah, Ubangijinsa, da taƙawa. Kuma kada ku ɓõye shaida, kuma wanda ya ɓõye ta, to, shi mai zunubin zũciyarsa ne. Kuma Allah ga abin da kuke aikatãwa Masani ne.
284Allah ne, da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma idan kun bayyana abin da yake a cikin zukatanku (na shaida), ko kuka ɓõye shi, Allah zai bincike ku da shi, sa´an nan Ya yi gãfara ga wanda Yake so, kuma Ya azabta wanda Yake so. Kuma Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.(1)
285Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala´ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabħwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã´a; (Muna nħman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take(2) "
286Allah ba Ya kallafa wa rai fãce ikon yinsa, yana da lãdar abin da ya tsirfanta, kuma a kansa akwai zunubin abin da ya yi ta aikatãwa: "Yã Ubangijinmu! Kada Ka kãmã mu, idan mun yi mantuwa, ko kuma mun yi kuskure. Yã Ubangijinmu! Kuma kada Ka aza nauyi a kanmu, kamar yadda Ka aza shi a kan waɗanda suke a gabãninmu. Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu ɗaukar abin da bãbu ĩko gare mu da shi. Kuma Ka yãfe daga gare mu, kuma Ka gãfarta mana, kuma Ka yi jin ƙai gare mu. Kai ne Majibincinmu, sabõda haka Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai."
Chapter 3 (Sura 3)
1A. L̃.M̃.
2Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme.
3Yã sassaukar da Littãfi a gare ka da gaskiya, yana mai gaskatãwa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Yã saukar da Attaura da Linjĩlã.
4A gabãni, suna shiryar da mutãne, kuma Ya saukar da littattafai mãsu rarrabħwa. Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah, suna da azãba mai tsanani. Kuma Allah Mabuwayi ne, Ma´abucin azãbar rãmuwa.
5Lalle ne, Allah bãbu wani abin da ke ɓõyuwa gare Shi a cikin ƙasa, kuma bãbu a cikin sama.
6Shi ne wanda Yake suranta ku a cikin mahaifu yadda Yake so. Bãbu abin bautãwa fãce Shi Mabuwãyi, Mai hikima.
7Shi ne wanda ya saukar da Littãfi a gare ka, daga cikinsa akwai ãyõyi bayyanannu, su ne mafi yawan Littãfin, da wasu mãsu kamã da jũna. To, amma waɗanda yake a cikin zukãtansu akwai karkata sai suna bin abin da yake da kamã da jũna daga gare shi, dõmin nħman yin fitina da tãwĩlinsa. Kuma bãbu wanda ya san tãwĩlinsa fãce Allah. Kuma matabbata a cikin ilmi sunã cħwa: "Mun yi ĩmãni da Shi; dukkansa daga wurin Ubangijinmu yake." Kuma bãbu mai tunãni fãce ma´abũta hankula.
8Yã Ubangijinmu! Kada Ka karkatar da zukãtanmu bãyan har Kã shiryar da mu, kuma Ka bã mu rahama daga gunKa. Lalle ne, Kai, Kai ne Mai yawan kyauta.
9"Yã Ubangijimu! Lalle ne Kai, Mai tãra mutãne ne dõmin wani yini wanda bãbu shakka a gare shi, Lalle ne Allah bã Ya sãɓãwar lõkacin alkawari."
10Lalle ne waɗanda suka kãfirta, dũkiyõyinsu bã su tunkuɗe musu kõme daga Allah, kuma ´ya´yansu bã su tunkuɗħwa, kuma waɗannan, sũ ne makãmashin wuta.
11Kamar ɗabi´ar mutãnen Fir´auna da waɗanda ke a gabãninsu, sun ƙaryata ãyõyinMu, sai Allah Ya kãmã su sabõda zunubansu, kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne.
12Ka ce wa waɗanda suka kãfirta: "Za a rinjãye ku, kuma a tãraku zuwa Jahannama, kuma shimfiɗar tã mũnana!
13"Lalle ne wata ãyã tã kasance a gare ku a cikin ƙungiyõyi biyu da suka haɗu; ƙungiya guda tana yãƙi a cikin hanyar Allah, da wata kãfira, suna ganin su ninki biyu nãsu, a ganin ido. Kuma Allah Yana ƙarfafa wanda Yake so da taimakonSa. Lalle ne a cikin wannan, hakĩƙa, akwai abin kula ga maabũta basĩra.
14An ƙawata wa mutãne son sha´awõyi daga mãtã da ɗiya da dũkiyõyi abũbuwan tãrãwa daga zinariya da azurfa, da dawãki kiwãtattu da dabbõbin ci da hatsi. Wannan shi ne dãɗin rãyuwar dũniya. Kuma Allah a wurinsa kyakkyãwar makõma take.
15Ka ce: Shin kuma, in gaya muku mafi alhħri daga wannan? Akwai gidãjen Aljanna a wurin Ubangiji sabõda waɗanda suka bi Shi da taƙawa, kõguna suna gudãna daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, da mãtan aure tsarkakakku, da yarda daga Allah. Kuma Allah Mai gani ne ga bãyinSa.
16Waɗanda suke cħwa: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne mu, mun yi ĩmãni, sai Ka gãfarta mana zunubanmu kuma Ka tsare mu daga azãbar wuta."
17Mãsu haƙuri, da mãsu gaskiya, da mãsu ƙanƙan da kai, da mãsu ciyarwa da mãsu istingifari a lõkutan asuba.
18Allah Ya shaida cħwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma´abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.
19Lalle ne, addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci. Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su sãɓã ba, fãce a bãyan ilmi ya je musu, bisa zãlunci a tsakãninsu. Kuma wanda ya kãfirta da ãyõyin Allah, to, lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako ne.
20To, idan sun yi musu da kai, sai ka ce: "Nã sallama fuskata ga Allah, kuma wanda ya bi ni (haka)." Kuma ka ce wa waɗanda aka bai wa littãfi da Ummiyyai:(1) "Shin kun sallama?" To, idan sun sallama, haƙĩƙa, sun shiryu kuma idan sun jũya, to, kawai abinda ke kanka, shi ne iyarwa. Kuma Allah Mai gani ne ga bãyinSa.
21Lalle ne waɗanda suke kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe Annabãwa bã da wani hakki ba, kuma suna kashe waɗanda ke umurni da yin ãdalci daga mutãne, to, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
22Waɗannan ne waɗanda ayyukansu suka ɓãci a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wasu mataimaka.
23Shin, ba ka ga waɗanda aka bai wa rabo daga littãfi ba ana kiran su zuwa ga Littãfin Allah dõmin ya yi hukunci a tsakãninsu sa´an nan wata ƙungiya daga cikinsu ta jũya bãya, kuma sunã mãsu bijirħwa?
24Wannan kuwa, dõmin lalle ne su sun ce: "Wutã bã zã ta shãfe mu ba, fãce a ´yan kwãnaki ƙidãyayyu." Kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa na ƙarya ya rũɗħ su a cikin addininsu.
25To, yãya idan Mun tãra su a yini wanda bãbu shakka a cikinsa, kuma aka cikã wa kõwane rai sakamakon abin da ya tsirfanta, alhãli kuwa, sũ bã zã a zãlunce su ba?
26Ka ce:(1) "Yã Allah Mamallakin mulki, Kanã bayar da mulki ga wanda Kake so, Kanã zãre mulki daga wanda Kake so, kuma Kanã buwãyar da wanda Kake so, kuma Kanã ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alhħri yake. Lalle ne Kai, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi ne."
27"Kanã shigar da dare a cikin yini, kuma Kanã shigar da yini a cikin dare, kuma Kana fitar da mai rai daga mamaci, kuma Kanã fitar da mamaci daga mai rai, kuma Kanã azurta wanda Kake so bã da lissafi ba.".
28Kada mũminai su riƙi kãfirai masõya, baicin mũminai. Kuma wanda ya yi wannan, to, bai zama a cikin kõme ba daga Allah, fãce fa dõmin ku yi tsaro daga gare su da ´yar kãriya. Kuma Allah yana tsõratar da ku kanSa. Kuma zuwa ga Allah makõma take.
29Ka ce: "Idan kun ɓõye abin da ke a cikin ƙirãzanku, kõ kuwa kun bayyana shi, Allah Yana sanin sa. Kuma Yana sanin abin da ke a cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah a kan kõwane abu Mai ĩkon yi ne."
30A Rãnar da kõwane rai yake sãmun abin da ya aikata daga alhħri, a halarce, da kuma abin da ya aikata daga sharri, alhãli yana gũrin, dã dai lalle a ce akwai fage mai nĩsa a tsakãninsa da abin daya aikata na sharrin! Kuma Allah Yanã tsõratar da kũ kanSa. Kuma Allah Mai tausayi ne ga bãyinSa.
31Ka ce: "Idan kun kasance kunã son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya sõ ku, kuma Ya gãfarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai."
32Ka ce: "Ku yi ɗã´a ga Allah da Manzo." To, amma idan sun jũya bãya, to, lalle ne Allah bã Ya son kãfirai.
33Lalle ne Allah Yã zãɓi Ãdama da Nũhu da Gidan Ibrãhĩma da Gidan Imrãna a kan tãlikai.
34Zuriyya ce sãshensu(1) daga sãshe, kuma Allah Mai ji ne, Masani.
35A lõkacin da mãtar Imrãna(2) ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ni, nã yi bãkancen abin da ke cikin cikĩna gare Ka; ya zama ´yantacce, sai Ka karɓa daga gare ni. Lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Masani."
36To, a lõkacin da ta haife ta sai ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne nĩ, nã haife ta mace!"Kuma Allah ne Mafi sanin abin da ta haifa." Kuma namiji bai zama kamar mace ba. Kuma nĩ nã yi mata suna Maryamu(3) kuma lalle ne ni, ina nħma mata tsari gare Ka, ita da zũriyarta daga Shaiɗan jħfaffe."
37Sai Ubangijinta Ya karɓe ta karɓa mai kyau. Kuma Ya yabanyartar da ita yabanyartarwa mai kyau, kuma Ya sanya rħnonta ga Zakariyya. Ko da yaushe Zakariyya ya shiga masallãci, a gare ta, sai ya sãmi abinci a wurinta. (Sai kuwa) ya ce: "Yã Maryamu! Daga ina wannan yake gare ki?" (Sai) ta ce: "Daga wurin Allah yake. Lalle ne Allah yana azurta wanda Ya so ba da lissafi ba."
38A can ne Zakariyya ya rõki Ubangijinsa, ya ce: "Ya Ubangijina! Ka bã ni zuriyya mai kyau daga gunKa. Lalle ne Kai Mai jin addu´a Kake."
39Sai malã´iku suka kirãye shi, alhãli kuwa shĩ yanã tsaye yana salla a cikin masallãci. (Suka ce), "Lalle ne Allah yana bã ka bushãra da Yahaya, alhãli yana mai gaskatãwar wata kalma daga Allah, kuma shugaba, kuma tsarkakke kuma annabi daga sãlihai."
40Ya ce: "Yã Ubangijina! Yãya yãro zai sãmu a gare ni, alhãli kuwa, lalle tsũfa ya sãme ni,kuma mãtãta bakarãriya ce?" Allah ya ce, "Kamar hakan ne, Allah yana aikata abin da Yake so."
41Ya ce: "Yã Ubangijinã! Ka sanya mini wata alãma!" (Allah) Ya ce "Alãmarka ita ce ba zã ka iya yi wa mutãne magana ba har yini uku face da ishãra. Sai ka ambaci Ubangijinka da yawa. Kuma ka yi tasbĩhi da marece da sãfe."
42Kuma a lõkacin da malã´iku suka ce: "Ya Maryamu! Lalle ne, Allah Ya zãɓe ki, kuma Ya tsarkake ki, kuma Ya zaɓe ki a kan mãtan tãlikai."
43"Yã Maryamu! Ki yi ƙanƙan da kai ga Ubangijinki, kuma ki yi sujada, kuma ki yi rukũ´i tãre(1) da mãsu rukũ´i."
44Wannan yana daga lãbarun(2) gaibi, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance ba a wurinsu a lõkacin da suke jħfa alƙalumansu (domin ƙuri´a) wãne ne zai yi rħnon Maryam. Kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke ta yin husũma(3) .
45A lõkacin da malã´iku suka ce "Yã Maryamu! Lalle ne Allah Yana bã ki bushãra da wata kalma daga gare Shi; sũnansa Masĩhu ĩsa ɗan Maryama, yana mai daraja a dũniya da Lãhira kuma daga Makusanta.
46"Kuma yana yi wa mutãne magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma lõkacin da yana dattijo, kuma yana daga sãlihai."
47Ta ce: "Yã Ubangijina! Yãya yãro zai kasance a gare ni, alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba?" (Allah) Ya ce: "Kamar wannan ne, Allah yana halittar abin da Yake so. Idan Ya hukunta wani al´amari, sai ya ce masa, "Ka kasance!, Sai yana kasancħwa."
48Kuma Ya sanar da shi rubũtu da hikima da Taurata da injĩla.
49Kuma (Ya sanya shi) manzo zuwa ga Bani Isrãila´ĩla (da sãko, cħwa), Lalle ne, ni haƙĩƙa nã zõ muku da wata ãyã daga Ubangijinku. Lalle ne ni ina halitta muku daga lãka, kamar siffar tsuntsu sa´an nan in hũra a cikinsa, sai ya kasance tsuntsu, da izinin Allah. Kuma ina warkar da wanda aka haifa makãho da kuturu, kuma ina rãyar da matattu, da izinin Allah. Kuma ina gayã muku abin da kuke ci da abin da kuke ajiyħwa acikin gidãjenku. Lalle ne, a cikin wannan akwai ãyã a gare ku, idan kun kasance mãsu yin ĩmãni.
50"Kuma inã mai gaskatãwa ga abin da yake a gabãnina daga Taurata. Kuma (nãzo) dõmin in halatta muku sãshen abin da aka haramta muku. Kuma nã tafo muku da wata ãyã daga Ubangijinku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã.
51"Lalle Allah shi ne Ubangijina, kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan ce hanya madaidaiciya."
52To, a lõkacin da Ĩsa ya gane kãfirci daga gare su, sai ya ce: "Su wãne ne mataimakãna zuwa ga Allah?" Hawãriyãwa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi ĩmani da Allah. Kuma ka shaida cħwa lalle ne mu, mãsu sallamãwa ne.
53"Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida.(1) .
54Kuma (Kãfirai) suka yi mãkirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alhħrin mãsu sãka wa mãkirci.
55A lõkacin da Ubangiji Ya ce: "Ya Ĩsa! Lalle NĨ Mai karɓar ranka ne, kuma Mai ɗauke ka ne zuwa gare Ni, kuma Mai tsarkake ka daga waɗanda suka kãfirta, kuma Mai sanya waɗanda suka bĩ ka a bisa waɗanda suka kãfirta har Rãnar Ƙiyãma. Sa´an nan kuma zuwa gare Ni makõmarku take, sa´an nan in yi hukunci a tsakãninku, a cikin abin da kuka kasance kuna sãɓã wa jũna.
56"To, amma waɗanda suka kãfirta sai In azabta su da azãba mai tsanani, a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wasu mãsu taimako.
57Kuma amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sai (Allah) Ya cikã musu ijãrõrinsu. Kuma Allah bã Ya son azzãlumai.
58"Wannan Muna karanta shi a gare ka (Muhammad) daga ãyõyi, da Tunatarwa mai hikima (Alƙur´ãni)."
59Lalle ne misãlin Ĩsã a wurin Allah kamar misãlin Ãdama ne, (Allah) Yã halitta shi daga turɓãya, sa´an nan kuma Ya ce masa: "Ka kasance: "Sai yana kasancewa.
60Gaskiya daga Ubangijinka take sabõda haka kada ka kasance daga mãsu shakka.
61To, wanda ya yi musu(2) da kai a cikinsa, a bãyan abin da ya zo maka daga ilmi, to ka ce: "Ku zo mu kirãyi, ´yã´yanmu da ´yã´yanku da mãtanmu da mãtanku da kanmu da kanku sa´an nan kuma mu ƙanƙantar da kai sa´an nan kuma mu sanya la´anar Allah a kan maƙaryata."
62Lalle ne wannan, haƙĩƙa, shi ne lãbãri tabbatacce, kuma bãbu wani abin bautawa fãce Allah, kuma lalle ne, Allah, haƙĩƙa,Shi ne Mabuwãyi Mai hikima.
63To, idan sun jũya bãya, to, lalle Allah Masani ne ga maɓannata.
64Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi!(1) Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa(2) a tsakãninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bãya sai ku ce: "ku yi shaida cħwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne."
65Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuke hujjacħwa a cikin sha´anin lbrãhĩma, alhãli kuwa ba a saukar da Attaura da injĩla ba fãce daga bãyansa? Shin bã ku hankalta?
66Gã ku yã waɗannan! Kun yi hujjacħwa a cikin abin da yake kunã da wani ilmi game da shi, to, don me kuma kuke yin hujjacħwa a cikin abin da bã ku da wani ilmi game da shi? Allah yana sani, kuma kũ, ba ku sani ba!
67Ibrãhĩma bai kasance Bayahũde ba, kuma bai kasance Banasãre ba, amma yã kasance mai karkata zuwa ga gaskiya, mai sallamãwa, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba.
68Lalle ne mafi hakkin mutãne da Ibrãhĩma haƙĩƙa, sũ ne waɗanda suka bi shi a (zamaninsa) da wannan Annabi (Muhammadu) da waɗanda suka yi ĩmãni. Kuma Allah ne Majiɓincin mũminai.
69Wata ƙungiya daga Mutãnen Littãfi sun yi gũrin su ɓatar da ku, to, ba su ɓatar da kõwa ba fãce kansu, kuma bã su sansancewa!
70Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuka kãfirta da ãyõyin Allah, alhãli kuwa kũ, kuna shaida (cħwa sũ gaskiya ne)?
71Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuke lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma kuke ɓõye gaskiya, alhãli kuwa kuna sane?
72Kuma wata ƙungiya daga Mutãnen Littãfi ta ce: "Ku yi ĩmãni da abin da aka saukar a kan waɗanda suka yi ĩmãni (da Muhammadu) a farkon yini, kuma ku kãfirta a ƙarshensa; tsammãninsu, zã su kõmõ."
73"Kada ku yi ĩmãni fãce(1) da wanda ya bi addininku." Ka ce: "Lalle ne, shiriya ita ce shiriyar Allah. (Kuma kada ku yi ĩmãni) cħwa an bai wa wani irin abin da aka bã ku, kõ kuwa su yi musu da ku a wurin Ubangijinku." Ka ce: "Lalle ne falala ga hannun Allah take, yana bãyar da ita ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadãci ne, Masani."
74Yanã keɓance wanda Ya so da rahamarSa, kuma Allah Ma´abucin falala ne, Mai girma.
75Kuma daga Mutãnen Littãfi akwai wanda yake idan ka bã shi amãnar kinɗãri(2) , zai bãyar da shi gare ka, kuma daga gare su akwai wanda idan ka bã shi amãnar dĩnari, bã zai bãyar da shi gare ka ba, fãce idan kã dawwama a kansa kanã tsaye. Wannan kuwa, dõmin lalle ne sũ sun ce, "Bãbu laifi a kanmu a cikin Ummiyyai."(3) Suna faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa suna sane.
76Na´am! Wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya yi taƙawa, to, lalle ne Allah yana son mãsu taƙawa.
77Lalle ne waɗanda suke sayen ´yan tamani kaɗan da alkawarin Allah da rantsuwõyinsu, waɗannan bãbu wani rabo a gare su a Lãhira, Kuma Allah bã Ya yin magana da su, kuma bã Ya dũbi zuwa gare su, a Rãnar Ƙiyãma, kuma bã Ya tsarkake su, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
78Kuma lalle ne, daga gare su akwai wata ƙungiya suna karkatar da harsunansu da Littãfi dõmin ku yi zaton sa daga Littãfin, alhãli kuwa bã shi daga Littãfin. Kuma suna cħwa: "Shi daga wurin Allah yake." Alhãli kuwa shi, bã daga wurin Allah yake ba. Sunã faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa sunã sane.
79Ba ya yiwuwa ga wani mutum, Allah Ya bã shi Littãfi da hukunci da Annabci, sa´an nan kuma ya ce wa mutãne: "Ku kasance bãyi gare ni, baicin Allah." Amma (zai ce): "Ku kasance mãsu aikin ibãda da abin da kuka kasance kuna karantar da Littãfin, kuma da abin da kuka kasance kuna karantãwa(1) ."
80Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã´iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)?
81Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa´an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."
82To, waɗanda kuma suka jũya bãya a bãyan wannan, to, waɗannan sũ ne fãsiƙai.
83Shin wanin Addinin Allah suke nħma, alhãli kuwa a gare Shi ne waɗanda ke cikin sama da ƙasa suka sallama wa, a kan sõ da ƙĩ, kuma zuwa gare Shi ake mayar da su?
84Ka ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da Isma´ĩla da Is´hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne."
85Kuma wanda ya nħmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra.
86Yãya Allah zai shiryar da mutãne waɗanda suka kãfirta a bãyan ĩmãninsu, kuma sun yi shaidar cħwa, lalle Manzo gaskiya ne, kuma hujjõji bayyanannu sun je musu? Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
87Waɗannan, sakamakonsu shi ne, lalle a kansu akwai la´anar Allah da mãla´iku da mutãne gabã ɗaya.
88Sunã mãsu dawwama a cikinta, bã a sauƙaƙa azãbar gare su, kuma ba su zama ana yi musu jinkiri ba.
89Fãce waɗanda suka tũba daga bãyan wannan, kuma suka yi gyãra, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne Mai jin ƙai.
90Lalle ne waɗanda suka kãfirta a bãyan ĩmãninsu, sa´an nan kuma suka ƙãra kãfirci bã zã a karɓi tũbarsu ba. Kuma waɗannan sũ ne ɓatattu.
91Lalle ne wanɗanda suka kãfirta, kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai to bã zã a karɓi cike da ƙasa na zinãri daga ɗayansu ba, kõ dã ya yi fansa da shi, waɗannan sunã da azãba mai raɗaɗi, kuma bã su da wasu mataimaka.
92Bã zã ku sãmi kyautatãwa ba, sai kun ciyar daga abin da kuke so. Kuma abin da kuka ciyar, kõ mħne ne, to, lalle ne Allah, gare shi, Masani ne.
93Dukan abinci yã kasance halal ne ga Bani lsrã´ĩla, fãce abinda Isrã´ĩla ya haramta wa kansa daga gabãnin saukar da Attaura. Ka ce: "To, ku zo da Attaura sa´an nan ku karantã ta, idan kun kasance mãsu gaskiya ne.
94"To, wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah daga bãyan wannan, to, waɗannan sũ ne azzãlumai."
95Ka ce: "Allah Ya yi gaskiya, sabõda haka ku bi aƙĩdar Ibrãhĩma mai karkata zuwa ga gaskiya; kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."
96Kuma lalle ne, Ɗaki na farko(1) da aka aza dõmin mutãne, haƙĩƙa, shi ne wanda ke Bakka(2) mai albarka kuma shiriya ga tãlikai.
97A cikinsa akwai ãyõyi bayyanannu; (ga misãli) matsayin Ibrãhĩma. Kuma wanda ya shige shi yã kasance amintacce. Kuma akwai hajjin Ɗãkin dõmin Allah a kan mutãne, ga wanda ya sãmi ĩkon zuwa gare shi, kuma wanda ya kafirta to lalle Allah Mawadãci ne daga barin tãlikai.
98Ka ce: "Ya kũ Mutãnen Littãfi! Don me kuke kãfirta da ãyõyin Allah, alhãli kuwa Allah Mai shaida ne a kan abin da kuke aikatãwa?"
99Ka ce: "Ya ku Mutãnen Littãfi! Don me kuke taushe wanda ya yi ĩmani, daga hanyar Allah, kuma kunã nħman ta zama karkatacciya, alhãli kuwa kunã mãsu shaida? Kuma Allah bai gushe daga abin da kuke aikatãwa ba yana Masani."
100Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi ɗã´aga wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littãfi, zã su mayar da ku kãfirai a bãyan ĩmãninku!
101Kuma yãyã kuke kãfircħwa alhãli kuwa anã karanta ãyõyin Allah a gare ku, kuma a cikinku akwai manzonSa? Kuma wanda ya nħmi tsari da Allah, to, an shiryar da shi zuwa ga hanya miƙaƙƙiya.
102Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, a kan hakkin binsa da taƙawa, kuma kada ku mutu fãce kuna mãsu sallamawa (Musulmi).
103Kuma ku yi daidami da igiyar Allah gabã ɗaya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da kuka kasance maƙiya sai Ya sanya sõyayya a tsakãnin zukãtanku sabõda haka kuka wãyi gari, da ni´imarSa, ´yan´uwa. Kuma kun kasance a kan gãɓar rãmi na wutã sai Ya tsãmar da ku daga gare ta. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayõyinSa, tsammãninku, zã ku shiryu.
104Kuma wata jama´a daga cikinku, su kasance suna kira zuwa ga alhħri, kuma suna umurni da alhħri, kuma suna hani daga abin da ake ƙi. Kuma waɗannan, sũ ne mãsu cin nasara.
105Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka rarrabu kuma suka sãɓã wa jũna, bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu kuma waɗannan sunã da azãba mai girma.
106A rãnar da wasu fuskõki suke yin fari kuma wasu fuskõki suke yin baƙi (zã a ce wa waɗanda fuskokinsu suke yin baƙin): "Shin kun kãfirta a bayan ĩmãninku? Don haka sai ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kasance kuna yi na kãfirci."
107Kuma amma waɗanda fuskõkinsu suka yi fari, to sũ suna cikin rahamar Allah kuma, su a cikinta, madawwama, ne.
108Waɗannan ãyõyin Allah ne, muna karanta su a gare ka da gaskiya, kuma Allah bã Ya nufin wani zãlunci ga tãlikai.
109Kuma abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa na Allah ne, kuma zuwa gare Shi ake mayar da al´amurra.
110Kun kasance mafi alhħrin al´umma wadda aka fitar ga mutãne kuna umurni da alhħri kuma kunã hani daga abin da ake ƙi, kuma kunã ĩmãni da Allah. Kuma dã Mutãnen Littãfi sun yi ĩmãni, lalle ne, dã (haka) yã kasance mafi alhħri a gare su. Daga cikinsu akwai mũminai, kuma mafi yawan su fãsiƙai ne.
111Bã zã su cũce ku ba, fãce dai tsangwama. Kuma idan sun yãƙe ku zã su jũya muku bãya, sa´an nan kuma bã zã a taimake su ba.
112An dõka ƙasƙanci a kansu a inda duk aka sãme su fãce da wani alkawari daga Allah, da alkawari daga mutãne. Kuma sun kõma da fushi daga Allah, kuma aka dõka talauci a kansu. Wannan kuwa dõmin sũ, lalle sun kasance suna kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe annabãwa, bã da wani haƙƙi ba. Wannan kuwa dõmin sãɓãwar da suka yi ne, kuma sun kasance suna yin ta´adi.
113Ba su zama daidai ba; daga Mutãnen Littafi akwai wata al´umma wadda take tsaye, suna karãtun ayõyin Allah a cikin sã´õ´in dare, alhãli kuwa sunã yin sujada.
114Suna ĩmãni da Allah da Yinin Lãhira, kuma suna umurni da abin da aka sani kuma suna hani daga abin da ba a sani ba, kuma sunã gaugãwa a cikin alhħrai. Kuma waɗannan suna cikin sãlihai.
115Kuma abin da suka aikata daga alhħri, to, bã zã a yi musu musunsa ba. Kuma Allah Masani ne ga mãsu taƙawa.
116Lalle ne waɗanda suka kãfirta, dũkiyõyinsu kõ ɗiyansu bã zã su wadatar musu da kõme ba daga Allah kuma waɗannan abõkan wuta ne, sũ, a cikinta, madawwama ne.
117Misãlin abin da suke ciyarwa, a cikin wannan rãyuwar dũniya, kamar misãlin iska ce (wadda) a cikinta akwai tsananin sanyi, ta sãmi shukar wasu mutãne waɗanda suka zãlunci kansu, sai ta halakar da ita. Allah bai zãlunce su ba, amma kansu suka kasance sunã zãlunta.
118Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi abõkan asĩri daga waninku, ba su taƙaita muku ɓarna. Kuma sun yi gũrin abin da zã ku cũtu da shi. Haƙĩka, ƙiyayya tã bayyana daga bãkunansu, kuma abin da zukãtansu ke ɓõyħwa ne mafi girma. Kuma lalle ne, Mun bayyana muku ãyõyi, idan kun kasance kunã hankalta.
119Gã ku yã waɗannan! Kunã son su bã su son ku, kuma kuna ĩmãni da Littãfi dukansa. Kuma idan sun haɗu da ku sukan ce "Mun yi ĩmani". Kuma idan sun kaɗaita sai su ciji yãtsu a kanku don takaici. Ka ce "Ku mutu da takaicinku. Lalle ne, Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙirãza."
120Idan wani alhħri ya shãfe ku sai ya baƙanta musu rai, kuma idan wata cũtar ta shãfe ku sai su yi farin ciki da ita. Kuma idan kun yi haƙuri kuma kuka yi taƙawa, ƙullinsu bã ya cũtar ku da kõme. Lalle ne, Allah ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa ne.
121Kuma a lõkacin(1) da ka yi sauko daga iyãlanka kana zaunar da mũminai a wurãren zama dõmin yãƙi, kuma Allah Mai ji ne, Masani.
122A lõkacin da ƙungiyõyi(1) biyu daga gare ku suka yi niyyar su karye, kuma Allah ne Majiɓincinsu, don haka, ga Allah mũminai sai su dogara.
123Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a Badar, alhãli kuwa kunã mafiya rauni, sabõda haka ku bi Allah da taƙawa tsammãninku, kuna gõdħwa.
124A lõkacin da kake cħwa ga mũminai, "Shin bai ishe ku ba, Ubangijinku Ya taimake ku da dubu uku daga malã´iku saukakku?"
125"Na´am! Idan kuka yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, kuma suka zo muku da gaugawarsu, irin wannan, Ubangijinku zai ƙãre ku da dubu biyar daga malãiku mãsu alãma."
126Kuma Allah bai sanya shi(2) ba, fãce dõmin bushãra a gare ku, kuma dõmin zukãtanku su natsu da shi. Taimako bai kasance ba fãce daga wurin Allah, Mabuwãyi, Mai hikima.
127Dõmin Ya katse wani għfe daga waɗanda suka kãfirta ko kuma Ya ƙasƙantã su, har su jũya, suna mãsu ruɓushi.
128Bãbu kõme a gare ka game da al´amarin (shiryar da su banda iyar da manzanci). Ko Allah Ya karɓi tũbarsu, kõ kuwa Ya yi musu azãba, to lalle ne sũ, mãsu zãlunci ne.
129Allah ne da mulkin abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, yana gãfarta wa wanda Yake so, kuma yana azabta wanda Yake so, kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
130Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ci riba ninkininki, riɓanye, kuma ku bi Allah da taƙawa, tsammãninku zã ku ci nasara.
131Kuma ku ji tsõron wutã wadda aka yi tattali dõmin kãfirai.
132Kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, tsammaninku a yi muku rahama.
133Kuma ku yi gaugawa zuwa ga nħman gãfara daga Ubangijinku da wata Aljanna wadda fãɗinta (dai dai da) sammai da ƙasa ne, an yi tattalinta dõmin mãsu taƙawa.
134Waɗanda suke ciyarwa a cikin sauƙi da tsanani kuma suke mãsu haɗiyħwar fushi, kuma mãsu yãfe wa mutãne laifi. Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa.
135Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfãsha ko suka zãlunci kansu sai su tunã da Allah, sabõda su nħmi gãfarar zunubansu ga Allah. Kuma wãne ne ke gãfara ga zunubai, fãce Allah? Kuma ba su dõge a kan abin da suka aikata ba, alhãli kuwa suna sane.
136Waɗannan sakamakonsu gãfara ce daga Ubangijinsu, da Gidajen Aljanna (waɗanda) ƙõramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Kuma mãdalla da ijãrar mãsu aiki.
137Lalle ne misãlai sun shũɗe a gabãninku, sai ku yi tafiya a cikin ƙasa sa´an nan ku dũba, yãyã ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance.
138Wannan bayãni ne ga mutãne, kuma shiryuwa ce da wa´azi ga mãsu taƙawa.
139Kuma kada ku yi rauni, kuma kada ku yi baƙin ciki, alhãli kuwa kũ ne mafiya ɗaukaka, idan kun kasance mãsu ĩmãni.
140Idan wani mĩki ya shãfe ku, to, lalle ne, wani mĩki kamarsa ya shãfi mutãnen, kuma waɗancan kwãnaki Muna sarrafa su a tsakãnin mutãne dõmin Allah Ya san waɗanda suka yi ĩmãni kuma Ya sãmi mãsu shahãda daga gare ku. Kuma Allah ba Ya son azzãlumai.
141Kuma dõmin Allah Ya ɗauraye waɗanda suka yi ĩmãni,kuma Ya ƙõƙe kãfirai.
142Ko kun yi zaton ku shiga Aljanna alhãli kuwa Allah bai wãda sanin waɗanda suka yĩ jihãdi daga gare ku ba, kuma Ya san mãsu haƙuri?
143Kuma lalle ne, haƙĩƙa kun kasance kuna gũrin mutuwa tun a gabãnin ku haɗu da ita, to lalle ne kun gan ta,(1) alhãli kuwa kuna kallo.
144Kuma Muhammadu bai zama ba face manzo lalle ne manzanni sun shũɗe a gabãninsa. Ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, zã ku jũya a kan dugaduganku? To, wanda ya jũya a kan dugadugansa, bã zai cũci Allah da kõme ba. Kuma Allah zai sãka wa mãsu gõdiya.
145Kuma bã ya yiwuwa ga wani rai ya mutu fãce da iznin Allah, wa´adi ne mai ƙayyadadden ajali. Kuma wanda yake nufin sakamakon dũniya Muna bã shi daga gare ta. Kuma wanda ke nufin samakon Lãhira Muna bã shi daga gare ta. Kuma zã Mu sãka wa mãsu godiya.
146Kuma da yawa wani Annabi wanda ya yi yãƙi, akwai jama´a mãsu yawa tãre da shi, sa´an nan ba su yi laushi ba ga abin da ya same su a cikin hanyar Allah, kuma ba su yi rauni ba kuma ba su sad da kai ba. Kuma Allah yana son mãsu haƙuri.
147Kuma bãbu abin da ya kasance maganarsu fãce faɗarsu cħwa: "Ya Ubangijinmu! Ka gãfarta mana zunubanmu da ɓarnarmu a cikin al´amarinmu, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai."
148Allah Yã sãka musu da sakamakon dũniya da kuma kyakkyawan sakamakon Lãhira. Kuma Allah yana son mãsu kyautatãwa.
149Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi ɗa´aga waɗanda suka kãfirta zã su mayar da ku a kan dugãduganku, har ku jũya kunã mãsu hasãra.
150ôa, Allah ne Majiɓincinku kuma ShĨ ne Mafi alhħrin mataimaka.
151Zã Mu jħfa tsõro a cikin zukãtan waɗanda suka kãfirta sabõda shirkin da suka yi da Allah gãme da abin da bai saukar da wani dalili ba game da shi. Kuma makõmarsu wuta ce, kuma tir da mazaunin azzãlumai!
152Kuma lalle ne haƙĩƙa Allah Yã yi muku gaskiya ga wa´adinSa, a lokacin da kuke kashe su da izninSa har zuwa lõkacin da kuka kãsa(1) , kuma kuka yi jãyayya a cikin al´amarin, kuma kuka sãɓã a bãyan (Allah) Ya nũna muku abin da kuke so. Daga cikinku akwai wanda yake nufin duniya kuma daga cikinku akwai wanda ke nufin Lãhĩra. Sa´an nan kuma Ya jũyar da ku daga gare su, dõmin Ya jarrabe ku. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Ya yãfe muku laifinku. Kuma Allah Ma´abucin falala ne ga mũminai.
153A lõkacin da kuke hawan dũtse, gudãne. Kuma ba ku karkata a kan kõwa ba, alhãli kuwa Manzon Allah nã kiran ku a cikin na ƙarshenku.(2) Sa´an nan (Allah) Ya sãkã muku da baƙin ciki a tãre da wani baƙin ciki. Domin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi baƙin cikin a kan abin da ya sãme ku. Kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa.
154Sa´an nan kuma (Allah) Ya saukar da wani aminci a gare ku daga bãyan baƙin cikin; gyangyaɗi yanã rufe wata ƙungiya daga gare ku, kuma wata ƙungiya, lalle ne, rãyukansu sun shagaltar da su, suna zaton abin da bã shi ne gaskiya ba, a game da Allah, irin zaton jahiliyya, suna cħwa: "Ko akwai wani abu a gare mu dai daga al´amarin?" Ka ce, "Lalle ne al´amari dukansa na Allah ne." Suna ɓõyħwa a cikin zukatansu, abin da bã su bayyana shi a gare ka. Suna cħwa: "Da munã da wani abu daga al´amarin dã ba a kashe mu ba a nan."Ka ce: "Kõ dã kun kasance a cikin gidãjenku, dã waɗanda aka rubũta musu kisa sun fita zuwa ga wurãren kwanciyarsu;" kuma (wannan abu yã auku ne) dõmin Allah Ya jarrabi abin da ke cikin ƙirãzanku. Kuma dõmin Ya tsarkake abin da ke cikin zukãtanku. Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙirãza.
155Lalle ne waɗanda suka jũya daga gare ku a ranar haɗuwar jama´a biyu, shaiɗan kawai ne ya talãlãɓantar da su, sabõda sãshen abin da suka tsirfanta. Kuma lalle ne haƙĩƙa, Allah Ya yãfe laifi daga gare su. Lalle Allah ne Mai gãfara Mai haƙuri.
156Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku kasance kamar waɗanda suka kãfirta kuma suka ce wa ´yan´uwansu idan sun yi tafiya a cikin ƙasa kõ kuwa suka kasance a wurin yãƙi: "Dã sun kasance a wurinmu dã ba su Mutu ba, kuma dã ba a kashe su ba." (Wannan kuwa) Dõmin Allah Ya sanya waccan magana ta zama nadãma a cikin zukãtansu. Kuma Allah ne Yake rãyarwa kuma Yake matarwa. Kuma Allah, ga abin da kuke aikatãwa, Mai gani ne.
157Kuma lalle ne idan aka kashe ku a cikin hanyar Allah, ko kuwa kuka mutu, haƙĩƙa, gãfara daga Allah da rahama ne mafi alhħri daga abin da suke tãrãwa.
158Kuma lalle ne idan kun mutu ko kuwa aka kashe ku, haƙĩƙa, zuwa ga Allah ake tãra ku.
159Sabõda wata rahama ce daga Allah ka yi sanyin hali a gare su. Kuma dã kã kasance mai hushi mai kaurin zuciya, dã sun wãtse daga għfenka. Sai ka yãfe musu laifinsu, kuma ka nħma musu gãfara, kuma ka yi shãwara(1) da su a cikin al´amarin. Sa´an nan kuma idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka dõgara ga Allah, lalle ne, Allah Yana son mãsu tawakkali.
160Idan Allah Ya taimake ku, to, bãbu marinjayi a gare ku. Kuma idan Ya yarɓe ku, to, wãnħ ne wanda yake taimakon ku bãyanSa? Kuma ga Allah sai mũminai su dõgara.
161Kuma bã ya yiwuwa ga wani annabi ya ci gulũlu.(2) Wanda ya ci gulũlu zai je da abin da ya ci na gulũlun, a Rãnar Ƙiyama. Sa´an nan a cika wa kõwane rai sakamakon abin da ya tsirfanta. Kuma sũ, bã zã a zãlunce su ba.
162Shin fa, wanda ya bĩbiyi yardar Allah, yana zama kamar wanda ya kõma da fushi daga Allah kuma makomarsa Jahannama ce? Kuma tir da makõma ita!
163Sũ, darajõji(3) ne a wurin Allah, kuma Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatawa.
164Lalle ne haƙĩƙa Allah Yã yi babbar falala(4) a kan mũminai, dõmin Yã aika a cikinsu, Manzo daga ainihinsu yana karanta ãyõyinSa a gare su, kuma yana tsarkake su, kuma yana karantar da su Littãfi da hikima, kuma lalle, sun kasance daga gabãni, haƙĩƙa suna cikin ɓata bayyananniya.
165Shin kuma a lõkacin(5) da wata masĩfa, haƙĩƙa, ta sãme ku alhãli kuwa kun sãmar da biyunta, kun ce: "Daga ina wannan yake?" Ka ce: "Daga wurin rãyukanku(6) yake." Lalle ne, Allah, a kan dukan kõme, Mai ĩkon yi ne.
166Kuma abin da ya sãme ku a rãnar haɗuwar jama´a biyu, to, da izinin Allah ne, kuma dõmin (Allah) Ya san mũminai (na gaskiya).
167Kuma dõmin Ya san waɗanda suka yi munãfunci, kuma an ce musu: "Ku zo ku yi yãƙi a cikin hanyar Allah, kõ kuwa ku tunkuɗe."(1) Suka ce: "Dã mun san (yadda ake) yãƙi dã mun bĩ ku." Sũ zuwa ga kãfirci a rãnar nan, sun fi kusa daga gare su zuwa ga ĩmãni. Sunã cħwa da bãkunansu abin da bã shi ne a cikin zukãtansu ba. Allah ne Mafi sani ga abin da suke ɓõyewa.
168Waɗanda suka ce wa ´yan´uwansu kuma suka zauna abinsu: "Dã sun yi mana ɗã´a, dã ba a kashe su ba." Ka ce: "To, ku tunkuɗe mutuwa daga rãyukanku, idan kun kasance mãsu gaskiya."
169Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a cikin hanyar Allah matattu ne. A´a, rãyayyu ne su, a wurin bangijinsu.(2) Ana ciyar da su.
170Suna mãsu farin ciki sabõda abin da Allah Ya bã su daga falalarSa, kuma suna yin bushãra ga waɗanda ba su risku da su ba, daga bayansu; "Bãbu tsõro a kansu kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba."
171Suna yin bushãra sabõda wata ni´ima daga Allah da wata falala. Kuma lalle ne, Allah bã Ya tozartar da ijãrar mũminai.
172Waɗanda suka karɓa(3) kira zuwa ga Allah da ManzonSa, daga bãyan mĩki ya sãme su. Akwai wata lãda mai girma ga waɗanda suka kyautata(4) yi daga gare su, kuma suka yi taƙawa.
173Waɗanda mutãne(5) suka ce musu: "Lalle ne, mutãne sun tãra (rundunõni) sabõda ku, don haka ku ji tsõrnsu. Sai (wannan magana) ta ƙara musu ĩmãni, kuma suka ce: "Mai isarmu Allah ne kuma mãdalla da wakili Shĩ."
174Sa´an nan suka jũya da wata ni´ima daga Allah da wata falala, wata cũta ba ta shãfe su ba, kuma suka bi yardar Allah. Kuma Allah ne Ma´abucin falala Mai girma.
175Wancan, Shaiɗan ne kawai yake tsõratar da, ku masõyansa. To, kada ku ji tsõronsu, ku ji tsõro Na idãn kun kasance mãsu ĩmãni.
176Kuma waɗannan da suke gaugãwa a cikin kãfirci kada su ɓãta maka rai. Lalle ne su, bã zã su cũci Allah da kõme ba. Allah yanã nufin cħwa, bã zai sanya musu wani rabo ba a cikin Lãhira kuma suna da wata azãba mai girma.
177Lalle ne, waɗanda suka sayi kãfirci da ĩmani, ba zã su cũci Allah da kõme ba. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
178Kuma kada waɗanda suka kãfirta su yi zaton cħwa, lalle ne jinkirin da Muke yi musu alhħri ne ga rãyukansu. Munã yi musu jinkirin ne dõmin su ƙãra laifi kawai kuma suna da azãba mai wulãƙantarwa.
179Allah bai kasance yana barin mũminai a kan abin da kuke kansa ba, sai(1) Ya rarrabe mummũna daga mai kyau. Kuma Allah bai kasance Yanã sanar da ku gaibi ba.(2) Kuma amma Allah Yana zãɓen wanda Ya so daga manzanninSa.(3) Sabõda haka ku yi ĩmãni da Allah da manzanninSa Kuma idan kun yi ĩmãni kuma kuka yi taƙawa, to, kunã da lãdã mai girma.
180Kuma kada waɗannan da suke yin rõwa da abin da Allah Ya bã su daga falalarSa su yi zaton shĩ ne mafi alhħri a gare su. A´a, shĩ mafi sharri ne a gare su. Zã a yi musu saƙandami da abin da suka yi rõwa da Shi a Rãnar Ƙiyãma. Kuma ga Allah gãdon sammai da ƙasa yake, kuma Allah, ga abin da kuke aikatãwa, Masani ne.
181Lalle ne, haƙĩƙa Allah Yã ji maganar waɗanda suka ce: "Lalle ne, Allah faƙĩri ne, mũ ne wadãtattu." za mu rubũta abin da suka faɗa, da kisan da suka yi wa Annabãwa bã da wani haƙƙi ba kuma Mu ce: "Ku ɗanɗani azãbar gõbara!
182"Wannan (azãbar) kuwa sabõda abin da hannuwanku suka gabãtar ne. Kuma lalle ne Allah bai zama mai zãlunci ga bãyinsa ba."
183Waɗanda suka ce: "Lalle ne Allah Yã yi alkawari zuwa gare mu, kada mu yi ĩmãni sabõda wani Manzo sai yã zo mana da Baiko wadda wuta za ta ci." Ka ce: "Lalle ne wasu manzanni sun je muku, a gabãnĩna, da hujjõji bayyanannu, kuma da abin da kuka faɗa, to, don me kuka kashe su, idan kun kasance mãsu gaskiya?"
184To, idan sun ƙaryata ka, to lalle ne, an ƙaryata wasu manzanni a gabãninka, sun je musu da hujjõji bayyanannu da littattafai, da kuma Littafi mai haske.
185Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma ana cika muku ijãrõrinku kawai ne a Rãnar Ƙiyãma. To, wanda aka nĩsantar daga barin wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to, lalle ne yã tsĩra. Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba fãce jin dãɗin rũɗi.
186Lalle ne zã a jarraba(1) ku a cikin dũkiyarku da rãyukanku, kuma lalle ne kuna jin cũtarwa mai yawa daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku da kuma waɗanda suka yi shirki. Kuma idan kun yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, to lalle ne, wannan yana daga manyan al´amurra.
187Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin waɗanda aka bai wa(1) Littãfi, "Lalle ne kuna bayyana shi ga mutãne, kuma bã zã ku ɓõye shi ba." Sai suka jħfar da shi a bãyan bãyansu, kuma suka sayi ´yan kuɗi kaɗan da shi. To, tir da abin da suke saye!
188Kada lalle ka yi zaton waɗanda suke yin farin ciki da abin da suka bãyar, kuma suna son a yabe su da abin da ba su aikatã ba. To, kada lalle ka yi zaton su da tsĩra daga azãba. Kuma suna da azãba mai raɗadi.
189Kuma ga Allah mulkin sammai da ƙasa yake. Kuma Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne.
190Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da sãɓãwar dare da yini akwai ãyõyi ga ma´abũta hankali.
191Waɗanda suke ambatar Allah a tsaye da zaune da a kan sãsanninsu, kuma suna tunãni a kan halittar sammai da ƙasa: "Yã Ubangijinmu! Ba Ka halitta wannan a kan banza ba. TsarkinKa! Sabõda haka Ka tsare mu daga azãbar wuta.
192"Ya Ubangijinmu! Lalle ne Kai, wanda Ka shigar a cikin wuta to, haƙĩƙa, Ka tozarta shi kuma bãbu wasu mataimaka ga azzãlumai.
193"Yã Ubangijinmu! Lalle ne mũ mun ji Mai kira yanã kira zuwa ga ĩmãni cħwa, ´Ku yi ĩmãni da Ubangijinku.´ Sai muka yi ĩmãni. Yã Ubangijinmu! Sabõda haka Ka gãfarta mana zunubanmu, kuma Ka kankare miyãgun ayyukanmu daga gare mu. Kuma Ka karɓi rãyukanmu tãre da mutãnen kirki.
194"Yã Ubangijinmu! Ka bã mu abin da Ka yi mana wa´adi (alkawari) a kan manzanninKa, kuma kada Ka tozarta mu a Rãnar Ƙiyãma. Lalle ne Kai, bã Ka sãɓãwar alkawari."
195Sabõda haka Ubangijinsu Ya karɓa musu cħwa, "Lalle ne Nĩ bã zan tozartar da aikin wani mai aiki ba daga gare ku, namiji ne ko kuwa mace, sãshenku daga sãshe. To, waɗanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidãjensu, kuma aka cũtar da su a cikin hanyaTa, kuma suka yi yãƙi, kuma aka kashe su, lalle ne zan kankare musu miyagun ayyukansu, kuma lalle ne zan shigar da su gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙoramu ke gudãna daga ƙarƙashinsu, a kan sakamako daga wurin Allah. Kuma a wurinSa akwai kyakkyawan sakamako.
196Kada jujjuyawar waɗanda suka kãfirta a cikin garũruwa ta rũɗe ka.
197Jin dãɗi ne kaɗan sa´an nan makõmarsu Jahannama ce, kuma tir da shimfiɗa ita!
198Amma waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa sunã da Gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙoramu ke gudãna a ƙarƙashinsu suna madawwama a cikinsu, a kan liyãfa daga wurin Allah, kuma abin da ke wurin Allah ne mafi alhħri ga barrantattu.
199Kuma lalle ne daga Mutãnen Littãfi(1) haƙĩƙa akwai wanda yake yin ĩmãnĩ da Allah da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar zuwa gare su, sunã mãsu tawãlu´i ga Allah, bã su sayen tamani kaɗan da ãyõyin Allah. Waɗannan suna da ijãrarsu a wurin Ubangijinsu. Lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako da yawa ne.
200Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Ku yi haƙuri kuma ku yi dauriya, kuma ku yi zaman dãko, kuma ku yi taƙawa, tsammãninku zã ku ci nasara.(2)
Chapter 4 (Sura 4)
1Ya ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, ma´auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza mãsu yawa da mãtã. Kuma ku bi Allah da taƙawa Wanda kuke rõƙon jũna da (sũnan), shi, da kuma zumunta(1) . Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku, Mai tsaro ne.
2Kuma ku bai wa marãyu dũkiyõyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dũkiyõyinsu zuwa ga dũkiyõyinku. Lalle shi, yã kasance zunubi ne mai girma.
3Kuma idan kun ji tsõron bã zã ku yi ãdalci ba a cikin marãyu,(2) to, (akwai yadda zã a yi) ku auri abin da ya yi muku dãɗi daga mãtã; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa´an nan idan kun ji tsõron bã zã ku yi ãdalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi ba.
4Kuma ku bai wa mãtã sadãkõkĩnsu da sauƙin bãyarwa. Sa´an nan idan suka yãfe muku wani abu daga gare shi, da dãɗin rai, to, ku ci shi da jin dãɗi da sauƙin haɗiya.
5Kada ku bai wa wãwãye(3) dũkiyarku, wadda Allah Ya sanya ta a gare ku, kunã mãsu tsayuwa (ga gyãranta). Kuma ku ciyar da su a cikinta, kuma ku tufãtar da su, kuma ku gaya musu magana sananniya ta alhħri.
6Kuma ku jarraba marãyu, har a lõkacin da suka isa aure. To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku mĩƙa musu dũkiyõyinsu. Kada ku cĩ ta da ɓarna, kuma da gaggawa kãfin su girma. Kuma wanda yake wadãtacce, to, ya kãma kãnsa, kuma wanda yake faƙĩri, to, ya ci, gwargwadon yadda ya kamata. To, idan kun mĩƙa musu dũkiyõyinsu, sai ku shaidar a kansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai bincike.
7Maza suna da rabo(1) daga abin da iyãye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, kuma mãtã suna da rabo daga abin da iyãye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, daga abin da ya ƙaranta daga gare shi kõ kuwa ya yi yawa, rabo yankakke.
8Kuma idan ma´abũta zumunta da marãyu da matalauta suka halarci rabon, to, ku azurta su daga gare shi, kuma ku faɗa musu magana sananniya ta alhħri.
9Kuma waɗanda suke dã sun bar(2) zuriyya mãsu rauni a bãyansu, zã su ji tsõro a kansu, su yi sauna, sa´an nan su bi Allah da taƙawa, kuma su faɗi magana madaidaiciya.
10Lalle ne, waɗanda suke cĩn dũkiyar marãyu da zãlunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani.
11Allah Yanã yi muku wasiyya a cikin ´ya´yanku; namiji yanã da rabon mãtã biyu. Idan sun kasance mãtã ne fiye da biyu kuwa, to, suna da biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari, kuma idan ta zama guda ce (kawai) to, tana da rabi. Kuma iyãyensa biyu kõwane ɗaya daga cikinsu yanã da ɗaya daga kashi shida ɗin abin da ya bari idan wani rħshe ya kasance gare shi, to, idan rħshe bai kasance gare shi ba, kuma iyãyensa ne (kawai) suka gãje shi, to, uwa tanã da sulusi (ɗaya daga cikin kashi uku). Sa´an nan idan ´yan´uwa sun kasance gare shi, to, uwarsa tana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida) daga bayan wasiyya wadda ya yi kõ kuwa bãshi. Ubanninku da ´yã´yan ku, ba ku sani ba, wannensu ne mafi kusantar amfani, a gare ku. Yankawa daga Allah. Lalle ne, Allah Yã kasance Masani Mai hikima.
12Kuma kunã da rabin abin da mãtanku na aure suka bari idan rħshe bai kasance gare su ba. Sa´an nan idan rħshe ya kasance gare su, to, kunã da rubu´i (ɗaya daga cikin kashi huɗu) daga abin da suka barin, daga bãyan wasiyya wadda suka yi kõ kuma bãshi. (Sũ) kuma suna da rubu´i daga abin da kuka bari idan rħshe bai kasance ba gare ku, idan kuwa rħshe ya kasance gare ku, to, sunã da sumuni (ɗaya daga cikin kashi takwas) daga abin da kuka bari, daga bãyan wasiyya wadda kuka yi kõ kuwa bãshi. Idan wani namiji ya kasance ana gãdon sa bisa kalãla, ko kuwa wata mace alhãli kuwa yana da ɗan´uwa kõ ´yar´uwa(1) to, kõwane ɗaya daga cikinsu yana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida), sai idan sun kasance mafi yawa daga wannan, to, sũ abõkan tãrayya ne a cikinsulusi (ɗaya bisa uku), daga bãyan wasiyya wadda aka yi kõ kuma bãshi. Bã da yana mai cũtarwa ba, ga wasiyya, daga Allah. Kuma Allah Masani ne Mai haƙuri.
13Waɗancan iyãkõkin Allah ne. Wanda ya yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, (Allah) zai shigar da shi gidãjen Aljanna (waɗanda) ɗõramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, kuma wannan shi ne rabo babba.
14Kuma wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa, kuma ya ƙħtare iyãkõkinSa, zai shigarda shi wuta, yana madawwami a cikinta, kuma yana da wata azãba mai walãkantarwa.
15Kuma waɗanda suka je wa alfãsha daga mãtanku, to, ku nħmi Shaidar mutãne huɗu daga gare ku a kansu. To, idan sun yi shaida, sai ku tsare su a cikin gidãje har mutuwa ta karɓi rãyukansu, ko kuwa Allah Ya sanya wata hanya a gare su.(1)
16Kuma waɗanda (mazã biyu) suka je mata(2) daga ku, to, ku cũtar da su, sa´an nan idan sun tũba kuma suka kyautata hãlãyensu, sai ku kau da kai da ga barinsu. Lalle ne Allah Yã kasance Mai kaɓar tũba ne, Mai jin ƙai
17Abar da take tũba kawai ga Allah, ita ce ga waɗanda suke aikatãwar mugun aiki da jãhilci sa´an nan su tũba nan kusa(3) to, waɗannan Allah Yanã karɓar tũ barsu kuma Allah Yã kasance Masani ne, Mai hikima.
18Bã tũba ba ce ga waɗanda suke aikatãwar mũnanan ayyuka har idan mutuwa ta halarci ɗayansu ya ce: "Lalle ne ni, na tũba yanzu," kuma bã tũba ba ce ga waɗanda suke mutuwa alhãli kuwa sunã kãfi rai Waɗannan mun yi musu tattalin wata azãba mai raɗaɗi
19Ku waɗanda suka yi ĩmãni! Bã ya halatta a gare ku, ku gãji mãtã a kan tĩlas kuma kadaku hana su aure dõmin ku tafi da sãshen abin da kuka ba su, fãce idan suka zo da wata alfãsha(4) bayya nanniya kuma ku yi zamantakħwa da su da alhħri sa´an nan idan kun ƙĩ su, to akwai tsammãnin ku ƙi wani abu alhãli kuwa Allah Ya sanya wani alhħri mai yawaa cikinsa.
20Kuma idan kun yi nufin musanya mãta a matsayin wata mãta, alhãli kuwa kun bai wa ɗayarsu ƙinɗari(1) to kada ku karɓi kõme daga gare, shi, shin, zã ku karɓe shi da ƙarya da zunubi bãyyananne?
21Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa, sãshenkuyã sãdu zuwa ga sãshe, kuma sun riƙi alkawari(2) mai kauri daga gare ku?
22Kuma kada ku auri abin da ubanninku suka aura daga mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne shi, ya kasance alfãsha da abin ƙyãma. Kuma ya mũnana ya zama hanya.
23An haramta muku uwãyenku, da ´yã´yanku, da ´yan´uwanku mãtã, da goggonninku, da innoninku, da ´yã´yan ɗan´uwa, da ´ya´yan ´yar´uwa, da uwãyenku waɗanan da suka shãyar da ku mãma, da ´yan´uwanku mãtã na shan mãma, da uwãyen mãtanku, da agõlolinku waɗanda suke cikin ɗãkunanku daga mãtanku, waɗanda kuka yi duhũli da su, kuma idan ba ku yi duhũli da sũ ba, to, bãbu laifi(3) a kanku, da mãtan ´yã´yanku waɗanda, suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin ´yan´uwa biyu mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne, Allah Yã kasance Mai gãfara ne Mai jin ƙai.
24Da tsararrun auren(1) wasu maza, fãce dai abin da hannuwanku suka mallaka. (Ku tsare) Littãfin Allah a kanku. Kuma an halatta muku abin da yake bayan wancan. Ku nħma da dukiyõyinku, kunã mãsu yin aure, bã mãsu yin zina ba. sa´an nan abin da kuka ji daɗi da shi daga gare su, to, ku bã su ijãrõrinsu bisa farillar sadãki. Bãbu laifia gare ku ga abin da kuka yi yardatayya(2) da shi a bãyan farillar sadãki. Lalle ne Allah Yã kasance Masani ne, Mai hikima.
25Kuma wanda(3) bai sãmi wadãta ba daga cikinku bisa ga ya auri ´ya´ya mũminai, to, (ya aura)daga abin da hannuwanku na dãma suka mallaka, daga kuyanginku mũminai. Kuma Allah ne Mafi sani ga ĩmãninku, sãshenku daga(4) sãshe. Sai ku aurħ su da izinin mutãnensu. Kuma ku bã su ijãrõrinsu bisa ga abin da aka sani, suna mãsu kamun kai bã mãsu zina ba, kuma bã mãsu riƙon abõkai ba. To, idan aka aure su, sai kuma suka zo da wata alfãsha, to, akwai a kansu rabin abin da ko a kan, ´ya´ya daga azãba. wancan (auren kuyanga) ga wanda ya ji tsõron wahala ne daga gare ku. Kuma ku yi haƙuri shi ne mafi alhħri a gare ku. Kuma Allah Mai gãfara ne Mai jin ƙai.
26Allah Yanã nufin Ya bayyana muku, kuma Ya shiryar da ku hanyõyin waɗanda suke a gabãninku kuma Ya karɓi tũbarku. Kuma Allah Masani ne Mai hikima.
27Kuma Allah Yanã nufin Ya karɓi tũbarku. Kuma waɗanda suke bin sha´awõyi suna nufin ku karkata, karkata mai girma.
28Allah Yana nufin Ya yi muku sauƙi, kuma an halitta mutum yana mai rauni.
29Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ci dũkiyõyinku a tsakãninku da yaudara,(1) fãce idan ya kasance daga fatauci ne, bisa yardatayya daga gare ku. Kuma kada ku kashe kãnku. Lalle ne Allah Yã kasance, game da ku, Mai jin ƙai ne.
30Wanda ya aikata wancan bisa ta´adi da zãlunci, to, zã Mu ƙõne shi da Wuta. Kuma wannan yã kasance ga Allah (abu ne) mai sauƙi.
31Idan kuka nĩsanci manyan abubuwan da ake hana ku aikatãwa, to, zã Mu kankare mũnanan ayyukanku daga gare ku, kuma Mu shigar da ku mashiga ta karimci.
32Kuma kada ku yi gurin abin da Allah Ya fifita sãshenku da shi a kan sãshe; maza suna da rabo daga abin da suka tsirfanta, kuma mãtã suna da rabo daga abin da suka tsirfanta. Ku rõƙi Allah daga falalarSa. Lalle ne Allah Yã kasance ga dukkan kõme, Masani.
33Kuma ga kõwa, Mun sanya magada daga abin da mahaifa da mafiya kusancin zumunta suka bari. Kuma waɗanda rantsuwõyinku suka ƙulla(2) ku bã su rabonsu. Lalle ne, Allah Yã kasance, a kan dukkan kõme, Mahalarci.
34Maza mãsu tsayuwa ne(1) a kan mãtã, sabõda abin da Allah Ya fifita sãshensu da shi a kan sãshe kuma sabõda abin da suka ciyar daga dũkiyõyinsu. To, sãlihan mãtã mãsu ɗã´a ne, mãsu tsarħwa ga gaibi sabõda abin da Allah Ya tsare. Kuma waɗanda kuke tsõron bijirewarsu, to, ku yi musu gargaɗi, kuma ku ƙaurace musu a cikin wurãren kwanciya, kuma ku dõke su. Sa´an nan kuma, idan sun yi muku ɗa´a, to, kada ku nħmi wata hanya a kansu. Lalle ne Allah Yã kasance Maɗaukaki, Mai girma.
35Kuma idan kun ji tsõron sãɓãwar tsakãninsu to ku aika da wani mai sulhu daga mutãnensa da wani mai sulhu daga mutãnenta.(2) Idan sun yi nufin gyãrãwa, Allah zai daidaita tsakãninsu (ma´auran). Lalle ne Allah Yã kasance Masani Mai jarrabãwa.
36Kuma ku bauta wa(3) Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi, kuma ga mahaifa ku yi kyautatãwa, kuma ga ma´abũcin zumunta da marãyu da matalauta, da maƙwabci ma´abũcin kusanta, da maƙwabci manĩsanci, da abõki a għfe da ɗan hanya, da abin da hannuwanku na dãma suka mallaka. Lalle ne Allah bã Ya son wanda ya kasance mai tãƙama, mai yawan alfahari.
37Waɗanda suke yin rõwa, kuma sunã umurnin mutãne da yin rõwa, kuma suna ɓõyewar abin da Allah Ya bã su na falalarSa. Kuma Mun yi tattali, sabõda kãfirai, azãba mai walãkantarwa.
38Kuma waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu dõmin nũna wa mutãne, kuma bã su yin ĩmãni da Allah, kuma bã su yin ĩmãnida Rãnar Lãhira, kuma wanda Shaiɗan ya kasance abõkin haɗi a gare shi, to, yã mũnana ga abõkin haɗi.
39Kuma mħne ne a kansu, idan sun yi ĩmãni da Allah, kuma da Rãnar Lãhira, kuma sun ciyar da abin da Allah Yã azurtã su, kuma Allah Ya kasance, gare su, Masani?
40Lalle ne, Allah bã Ya zãluncin gwargwadon nauyin zarra, idan ta kasance alhħri ce, zai riɓanya ta, kuma Ya kãwo daga gunsa ijãra mai girma.
41To, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al´umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!
42A rãnar nan, waɗanda suka kãfirta kuma suka sãɓã wa Manzo, sunã gũrin dã an baje ƙasa dasu, kuma bã su ɓõye wa Allah wani labãri.
43Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kusanci salla alhãli kuwa kuna mãsu mãye,(1) sai kun san abin da kuke faɗa kuma haka idan kuna mãsu janaba, fãce mai ƙħtare hanya, har ku yi wanka. Kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya ko kuwa wani daga cikinku, idan ya zo daga gayaɗi, kõ kuwa kun shãfi mãtã ba ku sãmi ruwa ba, to ku nufi, fuskar ƙasa mai kyau, ku yi shãfa ga fuskokinku da hannuwanku(2) . Lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfħwa Mai gãfara.
44Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda aka bai wa rabo daga Littafi, suna sayen ɓata, kuma suna nħman ku ɓace daga hanya?
45Kuma Allah ne Mafi sani ga maƙiyanku, kuma Allah Yã isa Ya zama Majibinci, kuma Yã isa Ya zama Mataimaki.
46Daga waɗanda suka tũba (Yahũdu), akwai wasu sunã karkatar da magana daga wurãrenta suna cħwa: "Mun jiya(1) kuma mun ƙiya, kuma ka jiya a wani wurin jiyãwa, kuma rã´ina (da ma´anar ´ruɓaɓɓe´), ka tsare mu," dõmin karkatarwa da harsunansu, kuma dõmin sũkã a cikin addini. Kuma dã lalle sũ, sun ce: "Mun jiya kuma mun yi ɗa´a, kuma ka saurãra kuma ka dãkata mana," haƙĩƙa, dã ya kasance mafi alhħri a gare su, kuma mafi daidaita; amma Allah Yã la´anħ su, sabõda kãfircinsu don haka bã zã su yi ĩmãni ba, sai kaɗan.
47Yã kũ waɗanda aka bai wa Littãfi! Ku yi ĩmãni da abinda Muka saukar, yana mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku, tun gabanin Mu shãfe wasu fuskõki, sa´an nan Mu mayar da su a kan bãyayyakinsu, ko Mu la´ane su kamar yadda Muka la´ani masu Asabar. Kuma umurnin Allah ya kasance abin aikatãwa.
48Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma.
49Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke tsarkake kansu? ôa, Allah ne Yake tsarkake wanda Yake so. Kuma ba za a zalunce su da zaren gurtsun dabĩno ba.
50Ka dũba yadda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah! Kuma shi ya isa ga zama zunubi bayyananne.
51Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka bai wa rabõ da ga Littafi suna ĩmãni da gunki da Shaiɗan(2) kuma suna cħwa ga waɗanda suka kãfirta: "Waɗannan ne mafiya shiriya daga waɗanda suka yi ĩmãni ga hanya"?
52Waɗannan ne waɗanda Allah Ya la´ane su, kuma wanda Allah Ya la´ana to bã zã ka sãmi mataimaki a gare shi ba.
53Ko suna da rabõ ne daga mulki? To, a sa´an nan bã zã su iya bai wa mutãne hancin gurtsun dabino ba.
54Ko suna hãsadar mutãne(1) ne a kan abin da Allah Ya bã su daga falalarSa? To, lalle ne, Mun bai wa gidan Ibrãhĩm Littãfi da hikima kuma Mun bã su mulki mai girma.
55To, daga cikinsu akwai wanda ya yi ĩmãni da shi, kuma daga cikinsu akwai wanda ya kange daga gare shi. Kuma yã isa Jahannama ta hũru da shi.
56Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ayõyinMu za Mu ƙõne su da wuta, kõ da yaushe fãtunsu suka nuna, sai Mu musanya musu wasu fãtun, dõmin su ɗanɗani azãba. Lalle ne Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima.
57Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, zã Mu shigar da su gidãjen Aljanna, (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã dawwamammu a cikinsu har abada suna da, a cikinsu, mãtan aure mãsu tsarki, Kuma Munã shigar da su a wata inuwa matabbaciyar lumshi.
58Lalle ne Allah Yanã umurnin ku ku bãyar da amãnõni zuwa ga mãsu sũ.(2) Kuma idan kun yi hukunci a tsakãnin mutãne, ku yi hukunci da ãdalci. Lalle ne Allah mãdalla da abin da Yake yi muku wa´azi da shi. Lalle ne Allah Yã kasance Mai ji ne, Mai gani.
59Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ɗã´a ga Allah, kuma ku yi ɗã´a ga ManzonSa, da ma´abũta al´amari daga cikinku.(3) Idan kun yi jãyayya a cikin wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da ManzonSa idan kun kasance kunã ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Wannan ne mafi alhħri, kuma mafi kyau ga fassara.
60Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke riyãwar cħwa sunã ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka da abin da aka saukar daga gabãninka, sunã nufin su kai ƙãra zuwa ga Ɗãgũtu(1) alhãli kuwa, lalle ne, an umurce su da su kãfirta da shi, kuma Shaiɗan yanã nħman ya ɓatar da su, ɓatarwa mai nĩsa.
61Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo" zã ka ga munãfukai(2) sunã kange mutãne daga gare ka, kangħwa.
62To, yaya, idan wata masĩfa ta sãme su, sabõda abin da hannuwansu suka gabãtar sa´an nan kuma su je maka sunã rantsuwa da Allah cħwa, "Ba mu yi nufin kõme ba sai kyautatawa da daidaitãwa."?
63Waɗannan ne waɗanda Allah Ya san abin da ke cikin zukãtansu. Sabõda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka yi musu gargaɗi, kuma ka gaya musu, a cikin sha´anin kansu, magana mai nauyi da fasãha.
64Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba fãce dõmin a yi masa ɗã´a da izinin Allah. Kuma dã dai lalle sũ a lõkacin da suka zãlunci kansu,(3) sun zo maka sa´an nan suka nħmi gãfarar Allah kuma Manzo ya nħma musu gãfara, haƙĩƙa, dã sun sãmi Allah Mai karɓar tũba Mai jin ƙai.
65To, a´aha! Ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi ĩmãni ba, sai sun yarda da hukuncinka ga abin da ya sãɓa a tsakãninsu, sa´an nan kuma ba su sãmi wani ƙunci a cikin zukãtansu ba, daga abin da ka hukunta, kuma su sallama sallamãwa.
66Kuma dã dai lalle Mũ, Mun wajabta musu cħwa, "Ku kashe kanku, ko kuwa ku fita daga gidãjenku," dã ba su aikata shi ba, fãce kaɗan daga gare su. Kuma dã dai lalle sũ sun aikata abin da ake yi musu gargaɗi da shi, haƙĩƙa, dã yã kasance mafi alhħri daga gare su, kuma mafi tsanani ga tabbatarwa.
67Kuma a sa´an nan, haƙĩƙa, dã Mun bã su, lãda mai girma, daga gunMu.
68Kuma lalle ne, dã Mun shiryar da su hanya madaidaiciya.
69Kuma waɗannan da suka yi ɗã´a ga Allah da Mazonsa, to, waɗannan sunã tãre da waɗanda Allah Ya yi ni´ima a kansu, daga annabãwa da mãsu yawan gaskatãwa, da masu shahãda(1) da sãlihai. Kuma waɗannan sun kyautatu ga zama abõkan tafiya.
70Waccan falalar daga Allah take, kuma Allah Yã isa zama Masani.
71Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku riƙi shirinku(2) sa´an nan ku fitar da hari jama´a jama´a ko ku fitar da yaƙi gaba ɗaya.
72Kuma lalle ne daga cikinku akwai mai fãsarwa(3) . To idan wata masĩfa ta sãme ku, sai ya ce: "Lalle ne, Allah Ya yi mini ni´ima dõmin ban kasance mahalarci tãre da su ba."
73Kuma lalle ne idan wata falala daga Allah ta sãme ku haƙĩƙa, tabbas, yanã cħwa, kamar wata sõyayya ba ta kasance a tsakãninku da shi ba: "Yã kaitona! Dã na zama tãre da su dai, dõmin in rabonta da rabõ mai girma!"
74Sai waɗanda suke sayar da rayuwar dũniya su karɓi ta Lãhira su yi yãƙi, a cikin hanyar Allah. Kuma wanda ya yi yãki a cikin hanyar Allah to a kashe shi ko kuwa ya rinjãya, sa´an nan zã Mu ba shi ijãra mai girma.
75Kuma mħne ne ya sãme ku, bã ku yin yãƙi a cikin hanyar Allah, da waɗanda aka raunanar daga maza da mata da yãra sunã cewa: "Yã Ubangijinmu! Ka fitar da mu daga wannan alƙarya wadda mutãnenta suke da zãlunci, kuma Ka sanya mana majiɓinci daga gunKa, kuma Ka sanya mana mataimaki daga gunKa."?
76Waɗanda suka yi ĩmãni, sunã yãki a cikin hanyar Allah, kuma waɗanda suka kãfirta sunã yãƙi a cikin hanyar Ɗãgũtu (Shaiɗan). To, ku yãƙi majiɓintan Shaiɗan. Lalle ne kaidin Shaiɗan yã kasance mai rauni.
77Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka ce musu: "Ku kange hannuwanku, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka."? To a lõkacin da aka wajabta musu yãƙi sai ga wani ɓangare daga cikinsu sunã tsõron mutãne kamar tsõron Allah kõ kuwa mafi tsanani ga tsõron, kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Don me Ka wajabta yãƙi a kanmu? Me ya hana Ka jinkirta mana zuwa ga wani ajali na kusa?"Ka ce: "Jin dãɗin dũniya kaɗan ne, kuma Lãhira ce mafi alhħri ga wanda ya yi taƙawa. Kuma bã a zãluntar ku da sĩlĩlin hancin gurtsun dabĩno!
78"Inda duk kuka kasance, mutuwa zã ta riske ku, kuma kõ da kun kasance ne a cikin gãnuwõyi ingãtattu!"Kuma idan wani alhħri ya sãme su sai su ce: "Wannan daga wurin Allah ne," kuma idan wata cũta ta sãme su, sai su ce: "Wannan daga gare ka ne."Ka ce: "Dukkansu daga Allah ne." To, me ya sãmi waɗannan mutãne, bã su kusantar fahimtar magana?
79Abin da ya sãme ka daga alhħri, to, daga Allah yake, kuma abin da ya sãme ka daga sharri, to, daga kanka yake, kuma Mun aike ka zuwa ga mutãne, (kana) Manzo, kuma Allah Yã isa ga zama shaida.
80Wanda ya yi ɗã´a ga Manzo, to, haƙĩƙa, yã yi ɗã´a ga Allah. Kuma wanda ya jũya bãya, to, ba Mu aike ka ba don ka zama mai tsaro a kansu.
81Kuma sunã cħwa, "Dã´a" sa´an nan idan sun fita daga wurinka, sai wata ƙungiya daga cikinsu ta kwãna da niyyar wanin abin da take faɗa, alhãli kuwa Allah na rubũta abin da suke kwãna da niyyarsa. Sabõda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka dõgara ga Allah, kuma Allah Yã isa ya zama wakĩli.
82Shin, bã su kula da Alƙur´ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũna mai yawa?
83Kuma idan wani al´amari(1) daga aminci ko tsõro ya je musu, sai su wãtsa shi. Dã sun mayar da shi zuwa ga Manzo da ma´abũta al´amari daga gare su, lalle ne, waɗanda suke yin bincikensa, daga gare su, zã su san shi. Kuma bã dõmin falalar Allah bã a kanku da rahamarSa, haƙĩƙa, dã kun bi Shaiɗan fãce kaɗan.
84Sabõda haka, ka(2) yi yãƙi a cikin hanyar Allah, ba a kallafa maka ba, face a kanka, kuma ka kwaɗaitar da mũminai. Akwai tsammãnin Allah Ya kange gãfin waɗanda suka kãfirta, kuma Allah ne Mafi tsananin gãfi, kuma Mafi tsananin azabtãwa.
85Wanda ya yi(3) cħto, cħto mai kyau, zai sãmi rabo daga gare shi, kuma wanda ya yi cħto,cħto mummũna, zai sãmi ma´auni daga gare shi, Kuma Allah Yã kasance, a kan dukkan kõme, Mai ƙayyade lõkaci.
86Kuma idan an gaishe(4) ku da wata gaisuwa, to, ku yi gaisuwa da abin da yake mafi kyau daga gare ta, kõ kuwa ku mayar da ita. Kuma Allah Yã kasance a kan dukkan kõme Mai lissãfi.
87Allah bãbu abin bautawa face Shi. Lalle ne haƙĩƙa Yana tãra(1) ku har zuwa ga Yinin Ƙiyãma bãbu shakka a cikinsa. Kuma wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga 1ãbãri.
88To, mħne ne ya sãme(2) ku a cikin munãfukai kun zama ƙungiya biyu, alhãli kuwa Allah ne Ya mayar da su sabõda abin da suka tsirfanta? Shin, kunã nufin ku shiryar da wanda Allah Ya ɓatar ne? Kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmi wata hanya ba zuwa gare shi.
89Suna gũrin ku kãfirta kamar yadda suka kãfirta, dõmin ku kasance daidai. Sabõda haka kada ku riƙi wasu masõya daga cikinsu, sai sun yõ hijira a cikin hanyar Allah. Sa´an nan idan sun jũya, to, ku kãmã su kuma ku kashe su inda duk kuka sãme su. Kuma kada ku riƙi wani masõyi daga gare su ko wani mataimaki.
90Fãce dai waɗanda suke sãduwa zuwa ga wasu mutãne waɗanda a tsakãninku da su akwai alkawari, kõ kuwa waɗanda suke sun je muku (domin) ƙirãzansu sun yi ƙunci ga su yãke ku, kõ su yãƙi mutãnensu. Kuma dã Allah Yã so lalle ne, dã Yã bã su ĩko a kanku, sa´an nan, haƙĩka, su yãke ku. To, idan sun nĩsance ku sa´an nan ba su yãƙe ku ba, kuma suka jħfa sulhu zuwa gare ku, to, Allah bai sanya wata hanya ba, a gare ku, a kansu.
91Za ku sãmi wasu(3) sunã nufin su amintar da ku kuma su amintar da mutãnensu, kõ da yaushe aka mayar da su ga fitina, sai a dulmuyã su a cikinta. To, idan ba su nĩsance ku ba, kuma sun jħfa sulhu zuwa gare ku, kuma sun kange hannuwansu, to, ku kãmã su, kuma ku kashe su inda duk kuka kãmã su, kuma waɗannan, Mun sanya muku dalĩli bayyananne a kansu.
92Kuma bã ya kasancħwa(1) ga mũmini ya kashe wani mũmini, fãce bisa ga kuskure. Kuma wanda ya kashe mũmini bisa ga kuskure, sai ya ´yanta wuya mũmina tare da mĩƙa diyya ga mutãnensa, f?ce idan sun bari sadaka. Sa´an nan idan (wanda aka kashe) ya kasance daga wasu mutãne maƙiya a gare ku, kuma shi mũmini ne, sai ya ´yanta wuya mũmina. Kuma idan ya kasance daga wasu mutãne ne (waɗanda) a tsakãninku da tsakãninsu akwai alkawari, sai ya bãyar da diyya ga mutãnensa, tare da ´yanta wuya mũmina. To, wanda bai sãmi (wuyan ba) sai azumin watanni biyu jħre, dõmin tũba daga Allah. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.
93Kuma wanda ya kashe wani mũmini da ganganci,(2) to, sakamakonsa Jahannama, yana madawwami a cikinta kuma Allah Yã yi fushi a kansa, kuma Ya la´ane shi, kuma Ya yi masa tattalin azãba mai girma.
94Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi tafiya (a cikin ƙasa), dõmin jihãdi, to, ku nħmi bãyani.(3) Kuma kada ku ce wa wanda ya jĩfa sallama zuwa gare ku: "Bã Musulmi kake ba." Kunã nħman hãjar rãyuwar dũniya, to, a wurin Allah akwai ganimõmi mãsu yawa. Kamar wannan ne kuka kasance a gabãnin ku musulunta, sa´an nan Allah Ya yi muku falala. Sabõda haka ku zan nħman bayãni.Lalle ne Allah Yã kasance, ga abin da kuke aikatãwa, Masani.
95Mãsu zama(1) daga barin yãƙi daga mũminai, wasun ma´abũta larũra da mãsu jihãdi a cikin hanyar Allah da dũkiyõyinsu da rãyukansu, bã su zama daidai. Allah Yã fĩfĩta mãsu jihãdi da dũkiyoyinsu da rãyukansu a kan mãsu zama, ga daraja. Kuma dukansu Allah Yã yi musu alkawari da abu mai kyau(2) . Kuma Allah yã fĩfĩta mãsu jihãdi a kan mãsu zama da lãda mai girma.
96Darajõji daga gare Shi da gãfara da rahama. Kuma Allah Yã kasance Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
97Lalle ne, waɗanda malã´ĩku(3) suka karɓi rãyukansu, (alhãli) sunã mãsu zãluntar kansu,sun ce (musu): "A cikin me kuka kasance?" (Su kuma) suka ce: "Mun kasance waɗanda aka raunana a cikin ƙasa." Suka ce: "Ashe ƙasar Allah ba ta kasance mayalwaciya ba, dõmin ku yi hijira a cikinta?" To, waɗannan makõmarsu Jahannama ce. Kuma tã mũnana ta zama makõma.
98Fãce waɗanda aka raunana daga maza da mãtã da yãra waɗanda bã su iya yin wata dabãra, kuma bã su shiryuwa ga hanya.
99To, waɗannan akwai tsammãnin Allah Ya yãfe laifi daga gare su, kuma Allah Yã kasance Mai yãfħwa ne, Mai gãfara.
100Kuma wanda ya yi hijira a cikin hanyar(4) Allah, zai sãmu, a cikin ƙasa, wurãren jũyãwa mãsu yawa da yalwa. Kuma wanda ya fita daga gidansa yana mai hijira zuwa ga Allah da ManzonSa, sa´an nan kuma mutuwa ta riske shi, to, lalle ne, lãdarsa tã auku ga Allah, Kuma Allah Yã kasance, a gare ku, Mai gãfara, Mai jin ƙai.
101Kuma idan kun yi tafiya a cikin ƙasa to, bãbu laifi a kanku ku rage(5) daga salla idan kun ji tsõron waɗanda suka kãfirta su fitine ku. Lalle ne kãfirai sun kasance, a gare ku, maƙiyi bayyananne.
102Kuma idan kã kasance a cikinsu, sai ka tsayar musu da salla, to, wata ƙungiya daga gare su ta tsaya tãre da kai, kuma sai su riƙe makãmansu. Sa´an nan idan sun yi salla, to, sai su kasance daga bãyanku. Kuma wata ƙungiya ta dabam (ta) waɗanda ba su yi sallar ba, ta zo, sa´an nan su yi sallar tãre da kai. Kuma su riƙi shirinsu da makãmansu. Waɗanda suka kãfirta sun yi gũrin dã dai kuna shagala daga makamanku da kãyanku dõmin su karkata a kanku, karkata guda. Kuma bãbu laifi, a kanku idan wata cũta daga ruwan sama ta kasance a gare ku, kõ kuwa kun kasance mãsu jinya ga ku ajiye makãmanku kuma dai ku riƙi shirinku. Lalle ne, Allah Yã yi tattali, ga kãfirai, azãba mai walakantarwa.
103Sa´an nan idan kun ƙãre salla, to ku ambaci Allah tsaye da zaune da a kan sãsanninku. Sa´an nan idan kun natsu, to, ku tsayar da Salla. Lalle ne salla tã kasance a kan mũminai, farilla mai ƙayyadaddun lõkuta.
104Kuma kada ku sassauta a cikin nħman mutãnen idan kun kasance kuna jin zõgi, to, lalle sũ ma, suna jin zõgi kamar yadda kuke jin zõgi. Kuma kuna tsammãni, daga Allah, abin da bã su tsammãni. Kuma Allah Yã kasance Masani Mai hikima.
105Lalle ne, Mũ, Mun saukar(1) , zuwa gare ka, Littãfi da gaskiya, dõmin ka yi hukunci a tsakãnin mutãne da abin da Allah Ya nũna maka, kuma kada ka kasance mai husũma dõmin mãsu yaudara.
106Kuma ka nħmi Allah gãfara. Lalle ne Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
107Kuma kada ka yi jãyayya dõmin tunkuɗe wa waɗanda suka yaudari kansu. Lalle ne Allah ba Ya son wanda ya kasance mai yawan hã´inci mai yawan zunubi.
108Suna nħman ɓõyewa daga mutãne kuma bã su nħmanɓõyewa daga Allah, alhãli kuwa Shi Yana tãre da su a lõkacin da suke kwãna da niyyar yin abin da bã Ya yarda da shi daga maganar. Kuma Allah Yã kasance ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa.
109Gã ku, yã waɗannan(1) ! Kun yi jidãli, dõmin tunkuɗe musu (kunya) a cikin rãyuwar dũniya, to, wane ne zai yi jidali domin tunkuɗe musu a Rãnar Ƙiyãma? Ko kuwa wãne ne zai kasance wakĩli a kansu?
110Kuma wanda ya aikata cũta kõ kuwa ya zãlunci kansa, sa´an nan kuma ya nħmi Allah gãfara, zai sãmi Allah Mai gãfara, Mai jin ƙai.
111Kuma wanda ya yi tsirfar zunubi, to yanã tsirfarsa ne a kan kansa kawai. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.
112Kuma wanda ya yi tsiwirwirin kuskure ko kuwa zunubi sa´an nan kuma ya jħfi wani barrantacce da shi, to, lalle ne yã tattali ƙirƙiren ƙarya da zunubi bayyananne.
113Kuma bã dõmin falalar Allah ba, a kanka, da rahamarSa, haƙĩƙa, dã wata ƙungiya daga gare su ta himmatu ga su ɓatar da kai. Kuma bã su ɓatarwa fãce kansu, kuma bã su cũtar ka daga kõme, Kuma Allah Yã saukar da Littãfi da hikima gare ka, kuma Ya sanar da kai abin da ba ka kasance kã sani ba. Kuma falalar Allah tã kasance mai girma a gare ka.
114Bãbu wani alhħri a cikin mãsu yawa daga gãnawarsu(1) fãce wanda ya yi umurni da wata sadaka kõ kuwa wani alhħri kõ kuwa gyãra a tsakãnin mutãne. Wanda ya aikata haka dõmin nħman yardõdin Allah to zã Mu bã shi lãda mai girma.
115Kuma wanda ya sãɓã wa(2) Manzo daga bãyan shiriya tã bayyana a gare shi, kuma ya bi wanin hanyar mũminai, zã Mu jiɓintar masa abin da ya jiɓinta, kuma Mu ƙõne shi da Jahannama. Kuma tã mũnana ta zama makõma.
116Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan, ga wanda Yake so. Kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ɓace ɓata mai nĩsa.(3)
117Bã su kiran kõwa, baicin Shi, fãce mãtã kuma bã su kiran kõwa fãce Shaiɗan, mai tsaurin kai.
118Allah Yã la´ane shi. Kuma ya ce: "Lalle ne, zã ni riƙi rabõ yankakke(4) , daga bãyinKa.
119"Kuma lalle ne, inã ɓatar da su, kuma lalle ne inã sanya musu gũri, kuma lalle ne ina umurnin su dõmin su kãtse(5) kunnuwan dabbõbi, kuma lalle ne inã umurnin su dõmin su canza halittar Allah." Kuma wanda ya riƙi Shaiɗan majiɓinci, baicin Allah, to, haƙĩƙa yã yi hasara, hasara bayyananniya.
120Yanã yi musu alkawari, kuma yanã sanya musu gũri, alhãli Shaiɗan bã ya yi musu wani wa´adĩn kõme face ruɗi.
121Waɗannan matattararsu Jahannama ce, kuma bã sãmun makarkata daga gare ta.
122Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, zã mu shigar da su gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, sunã mãsu dawwama a cikinsu har abada bisa ga wa´adin Allah tabbatacce. Wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga magana?
123(Al´amari) bai zama gũrace- gũracenku ba, kuma(1) ba gũrace- gũracen Mutãnen Littãfi ba ne. Wanda ya aikata mummunan aiki zã a sãka masa da shi kuma bã zai sãmi wani masõyi ba, baicin Allah, kuma bã zai sãmi mataimaki ba.
124Kuma wanda ya yi aiki daga ayyukan ƙwarai, namiji ne ko kuwa mace, alhãli kuwa Yanã mũmini, to, waɗannan sunã shiga Aljanna kuma bã zã a zãlunce su da gwargwadon hancin gurtsun dabĩno ba.
125Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi(2) .
126Kuma Allah ke da(3) (mallakar) abin da ke cikin sammai da kuma abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Yã kasance, ga dukkan, kõme, Mai kħwayewa.
127Sunã yi maka fatawa a cikin sha´anin mãtã. Ka ce: "Allah Yanã bayyana fatawarku a cikin sha´aninsu, da abin da ake karantãwa a kanku a cikin Littãfi, a cikin sha´anin marãyun mãtã waɗanda ba ku bã su abin da aka rubũta musu(4) (na gãdo) ba, kuma kunã kwaɗayin ku aurħ su, da sha´anin waɗanda aka raunana daga yãra, da sha´anin tsayuwarku ga marãyu da ãdalci. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, to, lalle ne, Allah Yã kasance Masani a gare shi."
128Kuma idan wata mace ta ji tsõron ƙiyo daga mijinta kõ kuwa bijirħwa to, bãbu laifi a kansu su yi sulhu a tsakãninsu, sulhu (mai kyau). Kuma yin sulhu ne mafi alhħri. Kuma an halartar wa rayũka yin rõwa. Kuma idan kun kyautata, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne, Allah Yã kasance, ga abin da kuke aikatãwa, Masani.
129Kuma bã zã ku iya yin ãdalci ba a tsakanin(1) mãtã kõ dã kun yi kwaɗayin yi. Sabõda haka kada ku karkata, dukan karkata, har ku bar ta kamar wadda aka rãtaye. Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
130Kuma idan sun rabu, Allah zai wadãtar da kõwanne daga yalwarSa. Kuma Allah Yã kasance Mayalwaci, Mai hikima.
131Kuma Allah ne da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun yi wasiyya ga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku, da kũ, cħwa ku bi Allah da taƙawa, kuma idan kun kãfirta, to, lalle ne, Allah Yanã da abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa. Kuma Allah Yã kasance wadãtacce, Gõdadde.
132Kuma Allah ne da mulkin abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa, kuma Allah Yã isa Ya zama wakĩli.
133Idan Yã so, zã Ya tafi da ku, yã kũ mutãne! kuma Ya zo da wasu. Allah Yã kasance a kan haka, Mai ĩkon yi ne.
134Wanda ya kasance(2) Yanã nufin sakamakon dũniya, to, a wurin Allah sakamakon dũniya da Lãhira yake. Kuma Allah Yã kasance Mai ji, Mai gani.
135Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayuwa da ãdalci, mãsu shaida(1) sabõda Allah, kuma kõ dã a kanku ne kõ kuwa, mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida kõ a kansa) ya kasance mawadãci kõ matalauci, to, Allah ne Mafi cancanta da al´amarinsu. Sabõda haka, kada ku bĩbiyi son zũciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, kõ kuwa kuka kau da kai, to lalle ne Allah Yã kasance Masani ga abin da kuke aikatãwa.
136Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni(2) da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã´ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa.
137Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, sa´an nan kuma suka kãfirta, sa´an nan kuma suka yi ĩmani, sa´an nan kuma suka kãfirta sa´an nan kuma suka ƙãra kãfirci, Allah bai kasance Yanã gãfarta musu ba, kuma bã zai shiryar da su ga hanya ba.
138Ka yi wa munãfukai bushãra da cħwa lalle ne sunã da azãba mai raɗaɗi.
139Waɗanda suke riƙon kãfirai masõya, baicin mũminai. Shin sunã nħman izza ne a wurinsu? To, lalle ne izza ga Allah take gabã ɗaya.
140Kuma lalle ne Yã sassaukar(3) muku a cikin Littãfi cħwa idan kun ji ãyõyin Allah, anã kãfirta da su, kuma anã izgili da su, to, kada ku zauna tãre da sũ, sai sun shiga cikin wani lãbãri. Lalle ne kũ, a lõkacin nan misãlinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tãra munãfukai da kãfirai ne a cikin Jahannama gabã ɗaya.
141Waɗanda suke jiran dãko game da ku; har idan wata nasara daga Allah ta kasance a gare ku, sai su ce: "Ashe, ba mu kasance tãre da kũ ba?" Kuma idan wani rabo ya sãmu ga kãfirai sai su ce: "Ashe ba mu rinjãye ku ba, kuma muka tsare ku daga mũminai?" To,Allah ne Yake yin hukunci tsakãninku a Rãnar Ƙiyãma, kuma Allah bã zai sanya hanya ba ga kãfirai a kan mũminai.
142Lalle ne munãfukai sunã yaudarħwa da Allah, alhãli kuwa Shi ne mai yaudararsu; kuma idan sun tãshi zuwa ga salla, sai su tãshi sunã mãsu kasãla. Suna nũnawa mutãne, kuma ba su ambatar Allah sai kaɗan.
143Mãsu kai-kawo ne a tsakãnin wancan; bã zuwa ga waɗannan ba, kuma bã zuwa ga waɗannan ba. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bã za ka sãmar masa wata hanya ba.
144Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi kãfirai masõya, baicin mũminai. Shin, kunã nufin ku sanyã wa Allah dalĩli bayyananne a kanku?
145Lalle ne, manãfukai sunã a magangara mafi ƙasƙanci daga wuta. Kuma bã zã ka sãma musu mataimaki ba.
146Sai waɗanda suka tũba, kuma suka gyãra, kuma suka nħmi fakuwa ga Allah, kuma suka tsarkake addininsu dõmin Allah, to, waɗannan sunã tãre da mũminai, kuma Allah zai bai wa mũminai lãda mai girma.
147Mħne ne Allah zai amfãna da yi maku azãba idan kun gõde, kuma kun yi ĩmãni? Allah Yã ksance Mai gõdiya Masani.
148Allah bã Ya son bayyanãwa da mũnãna daga magana(1) fãce ga wanda aka zãlunta. Kuma Allah Yã kasance Mai ji, Masani.
149Idan kun bayyana alhħri, kõ kuwa kuka ɓõye shi, kõ kuwa kuka yãfe laifi daga cũta, to, lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfewa, Mai ikon yi.
150Lalle ne, waɗanda suke kãfirta da Allah da ManzonSa kuma sunã nufin su rarrabe(2) a tsakãnin Allah da manzanninSa, kuma sunã cħwa: "Munã ĩmãni da sãshe, kuma munã kãfirta da sãshe." Kuma sunã nufin su riƙi hanya a tsakãnin wannan.
151Waɗannan sũ ne kãfirai sõsai, kuma Mun yi tattali, dõmin kãfirai, azãba mai walãkantarwa.
152Kuma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da manzanninSa, kuma ba su rarrabe a tsakãnin kõwa ba daga gare su, waɗannan zã Mu bã su ijãrõrinsu, kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
153Mutãnen Littãfi sunã tambayar ka ka saukar da wani littãfi daga sama, a kansu, to, lalle ne sun tambayi Mũsã mũfã girma daga wannan, suka ce: "Ka nũna mana Allah bayyane." Sai tsãwa ta kãmã su sabõda zãluncinsu, sa´an nan kuma suka riƙi maraƙi (abin bautãwa) bãyan hujjoji bayyanannu sun je musu. Sa´an nan Muka yãfe laifi daga wancan. Kuma Mun bai wa Mũsã dalĩli bayyananne.
154Kuma Muka ɗaukaka dũtse sãma da su, sabõda alkawarinsu, kuma Muka ce musu: "Ku shiga ƙõfar kunã mãsu tawãli´u," Kuma Muka ce musu: "Kada ku ƙħtare haddi a cikin Asabat," kuma Muka riƙi alkawari mai kauri daga gare su."
155To, sabõda warwarħwarsu ga alkawarinsu, da kãfirtarsu da ãyõyin Allah, da kisansu ga Annabãwa, bã da hakki ba, da maganarsu: "Zukãtanmu sunã cikin rufi." ôa, Allah ne Ya yunƙe a kansu sabõda kãfircinsu, sabõda haka bã zã su yi ĩmãni ba fãce kaɗan.
156Kuma sabõda kãfircinsu da faɗarsu, a kan Maryama, ƙiren ƙarya mai girma.
157Da faɗarsu(1) : "Lalle ne mu, mun kashe Masĩhu ĩsã ɗan Maryama Manzon Allah," alhãli kuwa ba su kashe shi ba, kuma ba su kħre shi ba, kuma amma an kamanta shi ne a garħ su. Lalle ne waɗanda suka sãɓã wa jũna a cikin sha´aninsa lalle ne, sunã shakka daga gare shi, bã su da wani ilmi fãce bin zato kuma ba su kashe shi ba bisa ga yaƙĩni.
158ôa, Allah Ya ɗauke shi zuwa garħ Shi, kuma Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima.
159Kuma bãbu kõwa daga Mutãnen Littafi(2) , fãce lalle yanã ĩmãni da shi a gabãnin mutuwarsa, kuma a Rãnar Ƙiyãma yana kasancħwa mai shaida, a kansu.
160To, sabõda zãlunci daga waɗanda suka tũba (Yahũdu) Muka haramta musu abũbuwa masu dãɗi waɗanda aka halatta su a gare su, kuma sabõda taushħwarsu daga hanyar Allah da yawa.
161Da karɓarsu ga riba, alhãli kuwa an hana su daga gare ta, da cin su ga dũkiyar mutãne daƙarya. Kuma Muka yi tattali, dõmin kãfirai, azãba mai raɗaɗi.
162Amma tabbatattu(3) a cikin ilmi daga gare su, da mũminai, suna ĩmani da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, madalla da masu tsai da salla, da mãsu bãyar da zakka, da mãsu ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Waɗannan zã Mu bã su lãda mai girma.
163Lalle ne Mu, Mun(1) yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nũhu da annabãwa daga bãyansa. Kuma Mun yi wahayi zuwa ga Ibrãhĩma da Ismã´ĩla da Is´hãƙa da Yaƙũbu da jĩkõki da ĩsa da Ayũba da Yũnusa da Hãruna da Sulaimãn. Kuma Mun bai wa Dãwũda zabũra.
164Da wasu Manzanni, haƙĩ ƙa, Mun bã da lãbarinsu a gare ka daga gabãni, da wasu manzanni waɗanda ba Mu bã da lãbãrinsu ba a gare ka, kuma Allah Yã yi magana da Mũsã, magana sõsai.
165Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima.
166Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã´iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida.
167Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka kange (wasu mutãne) daga hanyar Allah, haƙĩƙa, sun ɓace, ɓata mai nĩsa.
168Lalle ne waɗanda suka kãfirta, kuma suka yi zãlunci, Allah bai kasance Yana yi musu gãfara ba, kuma bã Ya shiryar da su ga hanya.
169Fãce hanyar Jahannama, sunã mãsu dawwama a cikinta har abada, kuma wannan yã kasance, ga Allah, mai sauƙi.
170Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa, Manzo yã je muku da gaskiya daga Ubangijinku. Sabõda haka ku yi ĩmãni yã fi zama alhħri a gare ku. Kuma idan kun kãfirta, to, Allah Yanã da abin da ke cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.
171Yã Mutãnen Littãfi! Kada ku zurfafã a cikin addininku. Kuma kada ku faɗa, ga Allah, fãce gaskiya. Abin da aka sani kawai, Masĩhu ĩsa ɗan Maryama Manzon Allah ne, kuma kalmarSa, yã jħfa ta zuwa ga Maryama, kuma rũhi ne daga gare Shi. Sabõda haka, ku yi ĩmãni da Allah da manzanninSa, kuma kada ku ce, "Uku". Ku hanu (daga faɗin haka) yã fi zama alhħri a gare ku. Abin da aka sani kawai, Allah Ubangiji ne Guda. TsarkinSa yã tabbata daga wani abin haifuwa ya kasance a gare Shi! Shĩ ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Yã isa Ya zama wakĩli.
172Masĩhu bã ya ƙyãmar ya kasance bãwa ga Allah, kuma haka malã´ikun nan makusanta. Kuma wanda ya yi ƙyãmar bautarSa kuma yi yi girman kai, to, zai tãra su zuwa gare shi gabã ɗaya.
173To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, to zã Ya cika musu ijãrõrinsu, kuma Yanã ƙãra musu daga falalarSa. Kuma amma waɗanda suka yi ƙyãma, kuma suka yi girman kai, to, zã Ya yi musu azãba, azãba mai raɗɗi kuma bã su samun wani masõyi dõmin kansu, baicin Allah, kuma bã su samun mataimaki.
174Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa wani dalĩli daga Ubangijinku yã je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku.
175To, amma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah kuma suka faku a gare Shi, to, zai shigar da su cikin wata rahama daga gare Shi da wata falala, kuma Ya shiryar da su zuwa gare Shi ga tafarki madaidaici.
176Sunã yi maka fatawa.(1) Ka ce: "Allah Yanã bayyana muku fatawa a cikin ´Kalãla."´ Idan mutum ya halaka, ba shi da rħshe kuma yana da ´yar´uwa, to, tana da rabin abin da ya bari, kuma shi yana gãdon ta, idan wani rħshe bai kasance ba a gare ta. Sa´an nan idan (´yan´uwa mãtã) suka kasance biyu, to suna da kashi biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari. Kuma idan sun kasance, ´yan´uwa, maza da mãtã to namiji yana da misãlin rabon mãtã biyu. Allah Yana bayyanawa a gare ku, dõmin kada ku ɓace. Kuma Allah ne, Masani ga dukan kõme.
Chapter 5 (Sura 5)
1Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! ku cika alkawurra. An halatta muku dabbobin jin dãɗi fãce abin da ake karantãwa a kanku, bã kunã mãsu halattar da farauta ba alhãli kuwa kunã mãsu harama. Lalle ne, Allah Yanã hukunta abin da yake nufi.
2Ya kũ waɗanda suka yi ĩmãni! kada ku halattar da ayyukan ibãdar Allah game da hajji, kuma da watã mai alfarma, kuma da hadaya, kuma da rãtayar raƙuman hadaya, kuma da mãsu nufin Ɗãki mai alfarma, sunã neman falala daga Ubangijinsu da yarda. Kuma idan kun kwance harama, to, ku yi farauta. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutãne ta ɗauke ku, dõmin sun kange ku daga Masallãci Mai alfarma, ga ku yi zãlunci. Kuma ku taimaki junã a kan aikin ƙwarai da taƙawa. Kuma kada ku taimaki juna a kan zunubi da zãlunci, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
3An haramta muku mũshe da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da mãƙararriya da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya, da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce abin da kuka yanka, da abin da aka yanka a kan gunki (shĩ ma an haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na cãca wannan fãsiƙanci ne. A yau waɗanda suka kãfirta sun yanke ƙauna daga addininku. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõroNa. A yau Nã kammalã muku addininku, Kuma Nã cika ni´imaTa a kanku, Kuma Nã yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku. To, wanda aka sanya wa lalũra a cikin yunwa mai tsanani, bã yana mai karkata zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
4Suna tambayar ka cewa mene ne aka halatta musu? Ka ce: "An halatta muku abũbuwa mãsu dãɗi da abin da kuka sanar (farauta) daga mãsu yin mĩki, kunã mãsu sakinsu daga hannuwanku, kunã sanar da su daga abin da Allah Ya sanar da ku. To, ku ci daga abin da suka kama sabõda ku, kuma ku ambaci sunan Allah a kansa, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai gaugawar sakamako da yawã ne.
5A yau an halatta muku abũbuwa mãsu dãɗi kuma abincin waɗanda aka bai wa Littãfi(1) halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da mãtã mãsu kãmun kai daga muminai da mãtã ´yã´ya daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku idan kun je musu da sadãkõkinsu, kuna mãsu yin aure, ba masu yin zina ba, kuma bã mãsu riƙon abõkai ba. Kuma wanda ya kãfirta da ĩmãni to, lalle ne aikinsa yã ɓãci, kuma shĩ, a cikin Lãhira, yanã daga mãsu hasãra.
6Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni ! idan kun tãshi(1) zuwa ga salla, to, ku wanke fuskõkinku da hannuwanku zuwa ga magincirõri, kuma ku yi shãfa ga kãnunku, kuma ku (wanke) ƙafãfunku zuwa idãnun sãwu biyu. Kuma idan kun kasance mãsu janaba, to, ku yi tsarki, kuma idan kun kasance majinyata, kõ kuwa a kan tafiya, kõ kuwa ɗaya daga gare ku ya zo daga k?shi, kõ kuka yi shãfayyar junã da mãtã, sa´an nan ba ku sãmi ruwa ba to ku yi nufin wuri(2) mai kyau, sa´an nan ku yi shãfa ga fuskõkinku da hannuwanku daga gare shi. Allah bã Ya nufi dõmin Ya sanya wani ƙunci a kanku, kuma amma Yanã nufi dõmin Ya cika ni´imarSa a kanku, tsammãninku kunã gõdewa.
7Kuma ku tuna ni´imar Allah akanku da alkawarinku wanda Ya ɗaure ku da shi, a lõkacin da kuka ce: "Mun ji kuma mun yi ɗã´a Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Masani ne ga abin da ke a cikin zukata."
8Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayin daka dõmin Allah mãsu shaida da ãdalci. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku a kan bã zã ku yi ãdalci ba. Ku yi ãdalci Shĩ ne mafi kusa ga taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa.
9Allah Yã yi wa´adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Sunã da wata gãfara da lãda mai girma.
10Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryatã, game da ãyõyinMu, waɗannan su ne abõkan wuta.
11Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da wasu mutãne suka yi niyyar su shimfiɗa hannuwansu zuwa gare ku(1) sai Ya kange hannuwansu daga gare ku, kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma sai muminai su dogara ga Allah kawai.
12Kuma lalle Allah Yã riƙi alkawarin Banĩ lsrã´ ĩla kuma Muka ayyana wakilai gõma shã biyu(2) daga gare su kuma Allah Ya ce: "Lalle ne Nĩ, Inã tãre da ku, haƙĩƙa, idan kun tsayar da salla, kuma kun bãyar da zakka, kuma kun yi ĩmani da manzannĩNa, kuma kuka taimake su, kuma kuka bai wa Allah rance mai kyau, haƙĩƙa, Inã kankare laifukanku daga gare ku, kuma haƙĩƙa, Inã shigar da ku gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sanã gudãna a ƙarƙashinsu, sa´an nan wanda ya kãfirta a bãyan wannan daga gare ku, to, lalle ne, yã ɓace daga tsakar hanya."
13To, sabõda warwarewarsu ga alkawarinsu Muka la´ane su, kuma Muka sanya zukãtansu ƙeƙasassu, sunã karkatar da magana daga wurãrenta, kuma suka manta da wani yanki daga abin da aka tunãtar da su da shi, kuma bã zã ka gushe ba kana tsinkãyar yaudara daga gare su fãce kaɗan daga gare su. To, ka yãfe laifi daga gare su, kuma ka kau da kai. Lalle ne, Allah Yanã son mãsu kyautatãwa.
14Kuma daga waɗanda suka ce: "Lalle ne mu Nasãra ne" Mun riƙi alkawarinsu, sai suka manta da wani yanki daga abin da aka tunãtar da su da shi, sai Muka shushuta adãwa da ƙeta a tsakãninsu har ya zuwa ga Rãnar Ƙiyãma. Kuma Allah zai bã su lãbari da abin da suka kasance sunã sanã´antawa.
15Yã Mutãnen littãfi! Lalle ne, ManzonMu yã je muku, yanã bayyana muku abu mai yawa daga abin da kuka kasance kunã ɓõyewa daga Littãfi, kuma yanã rangwame daga abu mai yawa. Haƙĩƙa, wani haske da wani Littafi mai bayyanãwa yã je muku daga Allah.
16Dashĩ, Allah Yanã shiryar da wanda ya bi yardarsa zuwa ga hanyõyin aminci, kuma Yanã fitar da su daga duffai zuwa ga haske da izninsa, kuma Yanã shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya.
17Lalle haƙĩƙa waɗanda suka ce: "Lalle Allah Shĩ ne Masĩhu ɗan Maryama," sun kãfirta. Ka ce: "To, wane ne ke iya mallakar wani abu daga Allah, idan Yã nufi Ya halakar da Masĩhu ɗanMaryama da uwarsa da wanda yake a cikin ƙasa gabã ɗaya?" Kuma Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, Yanã halitta abin da Yake so. Kuma Allah a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne.
18Kuma Yahudu da Nasãra sun ce: "Mu ne ɗiyan Allah, kuma masõyansa." Ka ce: "To, don me Yake yi muku azãba da zunubanku? ôa ku mutãne ne daga waɗanda Ya halitta, Yanã gãfartãwa ga wanda Yake so, kuma Yanã azabta wanda Yake so. Kuma Allah ne da mulkin sammai da ƙasa da abin da ke tsakãninsu kuma zuwa gare shi makomã take."
19Yã Mutãnen Littãfi! Lalle ManzonMu yã je muku yanã bayyana muku, a kan lõkacin fatara daga manzanni, dõmin kada ku ce: "wani mai bayar da bushãra bai zo mana ba, kuma haka wani mai gargaɗi bai zo ba." To, haƙĩƙa, mai bãyar da bushãra da mai gargaɗi sunje muku. Kuma Allah ne, a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi.
20Kuma a lõkacin da Musa ya ce wa mutãnensa: "Yã ku mutãnena! Ku tuna ni´imar Allah a kanku; dõmin Yã sanya annabãwa a cikinku, kuma Yã sanya ku sarãkuna, kuma Yã bã ku abin da bai bai wa kõwa ba daga tãlikai."
21"Yã mutãnena! Ku shiga ƙasar nan, abar tsarkakewa, wadda Allah Ya rubuta sabõda ku, kuma kada ku kõma da bãya, har ku juya kunã mãsu hasara."
22Suka ce: "Ya Musã! Lalle ne, a cikinta akwai wasu mutãne mãsu ƙarfi kuma lalle ne bã zã mu shige ta ba sai sun fice daga gare ta, to, idan sun fice daga gare ta, to, lalle ne mu, masu shiga ne."
23Wasu maza biyu(1) daga waɗanda suke tsõron Allah, Allah Yã yi ni´ima a kansu, suka ce: "Ku shiga gare su, daga ƙõfar, dõmin idan kuka shige shi, to, lalle ne ku, mãsu rinjãya ne, kuma ga Allah sai ku dogara idan kun kasance muminai."
24Suka ce: "Ya Musa! Lalle ne mu, bã za mu shige ta ba har abada matuƙar sun dawwama a cikinta sai ka tafi kai da Ubangijinka dõmin ku yi yãƙi. Lalle ne mu, munã a nan zaune."
25Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, bã ni mallakar kõwa fãce kaina da ɗan´uwãna, sai Ka rarrabe a tsakãninmu da tsakãnin mutãne fãsiƙai."
26(Allah) Ya ce: "To, lalle ne ita abar haramtãwa ce a gare su, shekara arba´in, sunã yin ɗimuwa a cikin ƙasa.(1) Sabõda haka kada ka yi baƙin ciki a kan mutãne fãsiƙai."
27Kuma karantã musu(2) lãbãrin ɗiya biyu(3) na Ãdamu, da gaskiya, a lõkacin da suka bãyar da baiko, sai aka karɓa daga ɗayansu kuma ba a karɓa daga ɗayan ba, ya ce: "Lalle ne zan kashe ka." (Ɗayan kuma) ya ce: "Abin sani dai, Allah Yana karɓã daga mãsu taƙawa ne."
28"Lalle ne idan ka shimfiɗa hannunka zuwa gare ni dõmin ka kashe ni, ban zama mai shimfiɗa hannuna zuwa gare ka ba dõmin in kashe ka. Lalle ne nĩ inã tsõron Allah Ubangijin tãlikai.
29"Lalle ne nĩ inã nufin ka kõma da zunubina game da zunubinka, har ka kasance daga abõkan wuta. Kuma wannan shĩ ne sakamakon azzãlumai."
30Sai ransa ya ƙawãtar masa kashewar ɗan´uwansa, sai kuwa ya kashe shi, sa´an nan ya wayi gari daga mãsu hasãra.
31Sai Allah Ya aiki wani hankãka, yanã tõno a cikin ƙasa dõmin ya nuna masa yadda zai turbuɗe gãwar ɗan´uwansa. Ya ce: "Kaitõna! Nã kãsa in kasance kamar wannan hankãka dõmin in turbuɗe gãwar ɗan´uwana?" Sai ya wãyi gari daga mãsu nadãmã.
32Daga sababin wannan,(1) Muka rubuta a kan Banĩ lsrã´ĩla cewa, lalle ne wanda ya kashe rai bã da wani rai ba, ko ɓarna a cikin ƙasa, to kamar yã kashe mutãne duka ne, kuma wanda ya rãya rai, to, kamar yã rãyar da mutãne ne gabã ɗaya. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, ManzanninMu sun je musu da hujjõji bayyanannu, sa´an nan kuma lalle ne, mãsu yawa daga gare su, a bãyan wannan, haƙĩƙa, mãsuɓarna ne a cikin ƙasa.
33Abin sani kawai sakamakon(2) waɗanda suke Yãƙin Allah da Manzonsa, kuma sunã aiki a cikin ƙasa dõmin ɓarna a kashe su ko kuwa a kere su, kõ kuwa a kakkãtse hannuwansu da ƙafãfunsu daga sãɓãni, ko kuwa a kõre su daga ƙasa. Wannan gare su wulakanci ne a cikin rãyuwar duniya, kuma a Lãhira sunã da wata azãba mai girma.
34Fãce fa waɗanda suka tuba tun a gabãnin ku sãmi ĩko akansu, to, ku sani cewa lalle ne, Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
35Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku nemi tsari zuwa gare shi, kuma ku yi jihãdi(3) a cikin hanyarsa, tsammãninku, za ku ci nasara.
36Lalle ne waɗanda suka kãfirta, lalle dã sunã da abin da ke a cikin ƙasa gabã ɗaya da misãlinsa tãre da shi, dõmin su yi fansa da shi daga azãbar Rãnar Ƙiyãma, bã a karɓarsa daga gare su, kuma sunã da azãba mai raɗadi.
37Sunã nufin su fita ne daga wuta, kuma ba su zama mãsu fita daga gare ta ba, kuma sunã da azãba zaunanniya.
38Kuma ɓarãwo da ɓarauniya sai ku yanke hannuwansu, bisa sakamako ga abin da suka tsirfanta, a kan azãba daga Allah. Kuma Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
39To, wanda ya tuba a bãyan zãluncinsa, kuma ya gyãra (halinsa), to, lalle ne Allah Yanã karɓar tubarsa. Lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
40Shin, ba ka sani ba cewa lalle ne, Allah Shi ne da mulkin sammai da ƙasa, Yanã azãbtar da wanda Yake so, kuma Yanã yin gãfara ga wanda yake so, kuma Allah a dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne?
41Yã kai Manzo! Kada waɗanda suke tseren gaugawa a cikin kãfirci su ɓãta maka rai, daga waɗanda suka ce: "Mun yi ĩmãni" da bãkunansu, alhãli zukatansu ba su yi ĩmãnin ba, kuma daga waɗanda suka tuba (watau Yahudu) mãsu yawan saurare ga wasu mutane na dabam waɗanda ba su je maka ba, sunã karkatar da zance daga bãyan wurarensa, sunã cewa: "Idan an bã ku wannan, to, ku karɓa, kuma idan ba a bã ku shĩ ba, to, ku yi sauna."Kuma wanda Allah Ya yi nufin fitinarsa, to bã zã ka mallaka masa kõme ba, daga Allah. Waɗannan ne waɗanda Allah bai yi nufin Ya tsarkake zukãtansu ba. Sunã da kunya a cikin duniya, kuma sunã da wata azãba mai girma a cikin 1ãhira.
42Mãsu yawan saurãre(1) ga ƙarya ne, mãsu yawan ci ga haram, to, idan sun zo maka, sai ka yi hukunci a tsakãninsu kõ ka bijira daga gare su. Kuma idan ka bijira daga gare su, to, bã zã su cuce ka da kõme ba, kuma idan ka yi hukunci, to, sai ka hukunta a tsakãninsu da ãdalci. Lalle ne, Allah Yanã son mãsu ãdalci.
43Kuma yãya suke gabãtar da kai ga hukunci, alhãli a wurinsu akwai Attaura, a cikinta akwai hukuncin Allah, sa´an nan kuma sunã karkacewa a bãyan wannan? waɗannan bã muminai ba ne!
44Lalle ne Mu, Mun saukar da Attaura, a cikinta akwai shiriya da haske Annabãwa waɗanda suke sun sallamã, sunã yin hukunci da ita ga waɗanda suka tuba (Yahudu), da mãlaman tarbiyya, da manyan malamai ga abin da aka neme su da su tsare daga Littãfin Allah, kuma sun kasance, a kansa, mãsu bã da shaida. To, kada ku ji tsõron mutãne kuma ku ji tsõroNa kuma kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da ãyoyiNa. wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne kafirai.
45Kuma Mun rubuta a kansu, a cikinta cewa, lalle (anã kashe) rai sabõda rai, kuma (anã ɗebe) idõ sabõda idõ, kuma (ana katse) hanci sabõda hanci, kuma kunne sabõda kunne kuma haƙori sabõda haƙõri kuma a raunuka a yi sakayya. To, wanda ya yi sadaka da shi, to, shi kaffãra ce a gare shi. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne azzãlumai.
46Kuma Muka biyar a kan gurãbansu da Ĩsa ɗan Maryama, yãnã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma Muka bã shi Injĩla a cikinsa akwai shiriya da haske, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma shi shiriya ne da wa´azi ga mãsu taƙawa.
47Kuma sai mutãnen injĩla su yi hukunci da abin da Allah ya saukar a cikinta. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah ya saukar, to, waɗannan su ne fãsiƙai.
48Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa. sai ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya(1) . Ga kõwanne daga gare ku Mun sanya sharĩa da hanya (ta bin ta). Kuma dã Allah Yã so, dã Yã sanya ku al´umma guda, kuma amma dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku. Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri. Zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya. Sa´an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã sãɓãwa a cikinsa.
49Kuma ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyinsu, kuma ka yi saunar su fitine ka daga sãshen abin da Allah Ya saukar zuwa gare ka. To, idan sun juya bãya, to, ka sani cewa, kawai Allah yana nufin Ya sãme su da masĩfa ne sabõda sãshen zunubansu. Kuma lalle ne, mãsu yawa daga mutãne, haƙĩƙa, fãsiƙai ne.
50Shin, hukuncin Jãhiliyya(2) suke nema? Kuma wane ne mafi kyau ga hukunci daga Allah sabõda mutãne waɗanda suke yin yaƙĩni (tabbataccen ĩmãni)?
51Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi Yahudu da Nasãra majiɓinta. Sãshensu majiɓinci ne ga sãshe. Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, lalle ne shĩ, yanã daga gare su. Lalle Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
52Sai ka ga waɗanda a cikin zukatansu akwai cuta, sunã tseren gaugawa a cikinsu, sunã cewa: "Munã tsõron kada wata masĩfa ta sãme mu." To, akwai tsammãnin Allah Ya zo da buɗi, kõ kuwa wani umurni daga wurinSa, har su wãyi gari a kan abin da suka ɓõye a cikin zukatansu, sunã mãsu nadãmã.
53Kuma waɗanda suka yi ĩmãni sunã cewa: "Shin, waɗannan ne waɗanda suka yi rantsuwa da Allah iyãkar rantsuwõyinsu, cewa su, lalle sunã tãre da ku?" Ayyukansu sun ɓãci, sabõda haka suka wãyi gari sunã mãsu hasãra.
54Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! wanda ya yi ridda daga gare ku daga addininSa, to, Allah zai zo da wasu mutãne, Yanã son su kuma sunã son Sa, mãsu tawãlu´i a kan muminai mãsu izza a kan kãfirai. Sunã yin, jihãdi a cikin hanyar Allah, kuma bã su tsõron zargin wani mai zargi. Waccan falalar Allah ce, Yanã bãyar da ita ga wanda Yake so. Kuma Allah Mayalwaci ne, Mai ilmi.
55Abin sani kawai, majiɓincinku Allah ne da ManzonSa da waɗanda suka yi ĩmãni,waɗanda suke sunã tsayar da salla kuma sunã bãyar da zakka kuma sunã ruku´i,
56Kuma wanda ya jiɓinci Allah da ManzonSa da waɗanda suka yi ĩmãni, to, ƙungiyar Allah sune mãsu rinjãya.
57Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi waɗanda suka riƙi addininku bisa izgili da wãsa, daga waɗanda aka bai wa Littãfi daga gabãninku da kãfirai, masõya, Kuma ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai.
58Kuma idan kuka yi kira zuwa ga salla, sai su riƙe ta bisa izgili da wãsa. Wannan dõmin lalle ne su, mutãne ne (waɗanda) bã su hankalta.
59Ka ce: "Ya Mutãnen Littãfi! Shin, kunã ganin wani laifi daga gare mu? Fãce dai dõmin mun yi ĩmãni da Allah da abin da aka Saukar zuwa gare mu da abin da aka saukar daga gabãni, kuma dõmin mafi yawanku fãsiƙai ne."
60Ka ce: "Shin, in gaya muku mafi sharri daga wannan, dõmin sakamako(1) daga wurin Allah? wanda Allah Ya la´ane shi kuma Ya yi fushi da shi, kuma Ya sanya daga gare su birai da aladai, kuma ya bauta wa Ɗãguta. Waɗannan ne mafiya sharrin wuri, kuma mafiya ɓata daga tsakar hanya."
61Kuma idan sun zo muku sai su ce: "Mun yi ĩmãni." Alhãli kuwa haƙĩƙa, sun shigo da kãfirci,kuma su lalle ne, sun fita da shi, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da suka kasance sunã ɓõyewa.
62Kuma kana ganin mãsu yawa daga gare su, sunã tseren gaugawa a cikin zunubi da zãlunci da cinsu ga haram. Haƙĩƙa, tir da abin da suka kasance suna aikatãwa.
63Don me Malaman Tarbiyya(2) da manyan malamai (na Yahudu) ba su hanã su daga faɗarsu ga zunubi da cinsu ga haram ba? Haƙiƙa, tir daga abin da suka kasance sunã sanã´antãwa.
64Kuma Yahudu suka ce: "Hannun Allah abin yi wa ƙuƙumi ne.(3) " An sanya hannuwansu a cikin ƙuƙumi! Kuma an la´ane su sabõda abin da suka faɗa. ôa, hannuwanSa biyu shimfiɗaɗɗu ne, Yanã ciyarwa yadda Yake so. Kuma lalle ne abin da aka saukar zuwa gare ka yanã ƙãra wa mãsu yawa daga gare su, girman kai da kãfirci. Kuma Mun jefa a tsakãninsu, ƙiyayya da ƙeta, zuwa Rãnar Ƙiyãma, kõ da yaushe suka hura wata wuta dõmin yãƙi, sai Allah Ya bice ta. Sunã aiki a cikin ƙasa dõmin ɓarna, alhãli kuwa Allah bã Ya son mãsu fasãdi.
65Kuma dã dai lalle Mutãnen Littãfi sun yi ĩmãni, kuma sun yi taƙawa, haƙĩƙa, dã Mun kankare miyãgun ayyukansu daga gare su, kuma dã Mun shigar da su gidãjen Aljannar Ni´ima.
66Kuma dã dai lalle su, sun tsayar da Attaura da Injĩla da abin da aka saukar zuwa gare su daga Ubangijinsu, haƙĩƙa, dã sun ci daga bisansu da kuma daga ƙarƙashin ƙafãfunsu. Daga gare su akwai wata al´umma mai tsakaitãwa kuma mãsu yawa daga gare su, abin da suke aikatawa yã munana.
67Yã kai Manzo! Ka iyar da(1) abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka. Kuma idan ba ka aikata ba, to, ba ka iyar da manzancinSa ba ke nan. Kuma Allah Yanã tsare ka daga mutãne. Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai.
68Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ba ku zama a kan kõme ba, sai kun tsayar da Attaura da Injĩla da abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku."Kuma lalle ne, abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, yanã ƙara wa mãsu yawa daga gare su girman kai da kãfirci. To, kada ka yi baƙin ciki a kan mutãne kãfirai.
69Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni da waɗanda sukatuba (Yahũdu) da Karkatattu da Nasãra, wanda ya yi ĩmãni da Allahda Rãnar Lãhira, kuma ya aikata aiki na ƙwarai, to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su zamo sunã baƙin ciki ba.
70Lalle ne haƙĩƙa Mun riƙi alkawarin Bani Isrã´ĩla, kumaMun aiki manzanni zuwa gare su, ko da yaushe wani manzo ya je musu da abin da rãyukansu bã su so, wani ɓangare sun ƙaryata, kuma wani ɓangare sunã kashewa, ,
71Kuma suka yi zaton cewa wata fitina bã zã ta kasance ba sai Suka makanta, kuma suka kurubta, sa´an nan Allah Ya karɓi tuba a gare su, sa´an nan suka makanta kuma suka kurunta mãsu yawa daga gare su, alhãli Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatãwa.
72Lalle ne haƙĩƙa waɗanda(1) suka ce: "Lalle ne Allah, shĩne Masĩhu, ɗan Maryama," sun kãfirta. Alhãli kuwa Masĩhu yã ce: "Yã Banĩ Isrã´ĩla! Ku bauta wa Allah Ubangijina, kuma Ubangijinku." Lalle ne shĩ, wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne, Allah Yã haramta masa Aljanna. Kuma bãbu wasu mataimaka ga azzãlumai.
73Lalle ne, haƙĩƙa, waɗanda suka ce: "Allah na ukun uku ne," sun kãfirta, kuma babu wani abin bautãwa fãce Ubangji Guda. Kuma idan ba su hanu daga abin da suke faɗa ba, haƙĩƙa, wata azãba mai raɗaɗi tãnã shãfar waɗanda suka kãfirta daga gare su.
74shin fã, bã su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gãfara, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?
75Masĩhu ɗan Maryama bai zama ba fãce Manzo ne kawai, haƙĩƙa, manzanni sun shige dage gabãninsa, kuma uwarsa siddika(2) ce. Sun kasance sunã cin abinci. Ka duba yadda Muke bayyana musu ãyõyi. Sa´an nan kuma ka duba yadda ake karkatar da su.
76Ka ce: "Ashe kunã bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya mallakar wata cuta sabõda ku kuma haka wani amfani(3) alhãli kuwa Allah Shi ne Mai ji, Masani?"
77Ka ce: "Yã ku Mutanen Littãfi! Kada ku zurfafa a cikin addininku, abin da bã gaskiya ba, kuma kada ku bĩbiyi son zuciyõyin waɗansu mutãne waɗanda suka riga suka ɓace a gabãni, kuma suka ɓatar da wasu mãsu yawa, kuma suka ɓace daga tsakar hanya."
78An la´ani waɗanda suka kãfirta daga Banĩ Isrã´ĩla a kan harshen Dãwuda da Ĩsa ɗan Maryama. wannan kuwa sabõda sãɓãwar da suka yi ne, kuma sun kasance suna ta´addi(1) .
79Sun kasance bã su hana juna daga abin ƙi, wanda suka aikata. Haƙĩƙa abin da suka kasancesunã aikatãwa yã munana.
80Kana ganin mãsu yawa daga gare su, sunã jiɓintar waɗanda suka kãfirta. Haƙĩƙa tir da abin da rãyukansu suka gabãtar sabõda su, watau Allah Yã yi fushi da su, kuma a cikin azãba su mãsu dawwama ne
81Kuma dã sun kasance sunã ĩmãni da Allah da Annabi da abin da aka saukar zuwa gare shi, dã ba su riƙe su masõya ba. Kuma amma mãsu yawa daga gare su, fãsiƙai ne.
82Lalle ne kana sãmun mafiya tsananin mutãne a adãwa ga waɗanda suka yi ĩmãni,Yahudu ne da waɗanda suka yi shirki. Kuma lalle ne kanã sãmun mafiya kusantarsu a sõyayya ga waɗanda suka yi ĩmãni su ne waɗanda suka ce: "Lalle mu ne Nasãra." Wancan kuwa sabõda akwai Ƙissawa da ruhubãnãwa(2) daga cikinsu. Kuma lalle ne su, bã su yin girman kai.
83Kuma idan suka ji abin da aka saukar zuwa ga Manzo, kanã ganin idanunsu sunã zubar da hawãye, sabõda abin da suka sani daga gaskiya, sunã cewa: "Yã Ubangijinmu! Mun yi ĩmãni, sai ka rubuta mu tãre da mãsu shaida.
84"Kuma mene ne yake gare mu, bã zã mu yi ĩmãni da Allah ba, da kuma abin da ya zo mana daga gaskiya, kuma munã gurin Ubangijinmu Ya shigar da mu tãre da mutãne sãlihai?"
85Sabõda haka, Allah Yã sãkã musu, dõmin abin da suka faɗa da gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu, kuma wannan ne sakamakon mãsu kyautatãwa.
86Kuma waɗanda suka kãfirta kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗancan ne abõkan Wuta.
87Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku haramta abubuwa mãsu dãɗi da Allah Ya halatta muku, kuma kada ku ƙetare haddi. Lalle ne, Allah bã Ya son mãsu ƙetare haddi.(1)
88Kuma ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, halat mai daɗi, kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake ku, mãsu ĩmãni ne da shi.
89Allah bã Ya kãmã ku sabõda yãsassa(2) a cikin rantsuwõyinku, kuma amma Yanã kãmã ku da abin da kuka ƙudurta rantsuwõyi (a kansa). To, kaffãrarsa ita ce ciyar da miskĩni gõma daga matsakaicin abin da kuke ciyar da iyãlanku, kõ kuwa tufãtar da su, kõ kuwa ´yantãwar wuya. Sa´an nan wanda bai sãmu ba, sai azumin kwãna uku. Wannan ne kaffãrar rantsuwõyinku, idan kun rantse. Kuma ku kiyãye rantsuwoyinku. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ãyoyinsa, tsammãninku kunã gõdewa.
90Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri´a,(1) ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa la´alla ku ci nasara.
91Abin sani kawaĩ Shaiɗan yanã nufin ya aukar da adãwa da ƙeta a tsakãninku, a cikin giya da cãca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku mãsu hanuwa ne?
92Ku yi ɗã´a ga Allah, kuma ku yi ɗã´a ga Manzo, kuma ku kiyãye. To, idan kun jũya, to, ku sani abin da kawai yake kan ManzonMu, iyarwa bayyananniya.
93Bãbu laifi a kan waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, a cikin abin da suka ci, idan sun yi taƙawa kuma suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sa´an nan suka yi taƙawa kuma suka yi ĩmãni,sa´an nan kuma suka yi taƙawa kuma suka kyautata.(2) Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa.
94Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle ne, Allah zai jarraba ku da wani abu, daga farauta, hannuwanku da mãsunku sunã sãmun sa dõmin Allah Ya san wanda yake tsoron Sa a fake. To, wanda ya yi ta´addi a bãyan wannan, to, yanã da azãba mai raɗaɗi.
95Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kashe farauta alhãli kunã mãsu harama.(3) Kuma wanda ya kashe shi daga gare ku, yanã mai ganganci, sai sakamako misãlin abin da ya kashe, daga dabbõbin ni´ima, ma´abuta ãdalci biyu daga cikinku sunã yin hukunci da shi. Ya zama hadaya mai isa ga Ka´aba ko kuwa kaffãra da abincin miskĩnai ko kuwa a matsayinsa ya yi azumi dõmin ya ɗanɗani masifar al´amarinsa. Allah Yã yafe laifi daga abin da ya gabãta. Kuma wanda ya kõma, to, Allah zai yi azãbar rãmuwa daga gare shi, kuma Allah Mabuwãyi ne, ma´abũcin azabãr rãmuwa.
96An halatta muku farautar ruwa da abincinsa dõmin jin dãɗi a gare ku, kuma dõmin matafiya. Kuma an haramta farautar tudu a kanku, matuƙar kun dawwama mãsu harama. Kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake zuwa gare Shi ne ake tãra ku.
97Allah Ya sanya Ka´aba Ɗaki Tsararre, ma´aunin addini ga mutane, kuma Yã sanya watã Mai alfarma da hadaya da rãtayõyin Allah Yã san abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma cewa lalle Allah, ga dukkan, kõme, Masani(1) ne.
98Ku sani cewa lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne, kuma lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
99Bãbu abin da yake a kan Manzo, sai iyarwa, kuma Allah Yanã sanin abin da kuke bayyanãwa da abin da kuke ɓõyewa.
100Ka ce: "Mummuna da mai kyau bã su daidaita, kuma kõ dã yawan mummuan yã bã ka sha´awa. Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, yã ma´abuta hankula ko la´alla zã ku ci nasara."
101Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yi tambaya ga abubuwa, idan an bayyana muku (hukuncinsu) su ɓãta muku rai. Kuma idan kuka yi tambaya a gare su a lõkacin(2) da ake saukar da Alƙur´ãni, zã a bayyana maku. Allah Yã yãfe laifi daga gare su, Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri.
102Lalle ne wasu mutãne sun tambaye su daga gabãninku, sa´an nan kuma suka wãyi gari da su sunã kãfirai.
103Kuma Allah bai sanya wata bahĩra ba, kuma haka sã´iba, kuma haka wasĩla, kuma haka hãmi,(3) amma waɗanda suka kãfirta, su suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma mafi yawansu bã su hankalta.
104Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo," sai su ce: "Mai isarmu shi ne abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma kõ dã ubanninsu sun kasance bã su sanin kõme kuma bã su shiryuwa?
105Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku lazimci(1) rãyukanku, wanda ya ɓace bã zai cuce ku ba idan kun shiryu, zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya. Sa´an nan Ya bã ku lãbari ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
106Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Shaidar(2) tsakãninku, idan mutuwa ta halarci ɗayanku, a lõkacin wasiyya, maza biyu ne ma´abuta ãdalci daga gare ku, kõ kuwa wasu biyu daga wasunku idan kun tafi a cikin ƙasa sa´an nan masĩfar mutuwa ta sãme ku. Kunã tsare su daga bãyan salla har su yi rantsuwa da Allah; idan kun yi shakka: "Bã mu sayen kuɗi da shi, kõ dã ya kasance ma´abucin zumunta kuma bã mu ɓõye shaidar Allah. Lalle ne mu, a lõkacin, haƙĩƙa, munã daga mãsu zunubi."
107To, idan aka gane cewa lalle sũ, sun cancanci zunubi to sai wasu biyu su tsayu matsayinsu daga waɗanda suka karɓa daga gare su, mutãne biyu mafiya cancanta, sa´an nan su yi rantsuwa da Allah: "Lalle ne shaidarmu ce mafi gaskiya daga shaidarsu, kuma ba mu yi zãlunci ba. Lalle mu, a lõkacin haƙĩƙa, munã daga azzãlumai."
108Wannan ne mafi kusantar su zo da shaida a kan fuskarta kõ kuwa su yi tsõron a tũre rantsuwõyi a bãyan rantsuwõyinsu. Kuma ku bi Allah da taƙawa kuma ku saurara, kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai.
109A ranar da Allah Yake tãra manzanni sa´an nan Ya ce: "Mene ne aka karɓa muku?" (Zã) su ce: "Bãbu ilmi a gare mu. Lalle ne Kai, Kai ne Masanin abubuwan fake."(1)
110A lõkacin da Allah Ya ce: "Yã Ĩsã ɗan Maryama! Ka tuna ni´ima Ta a kanka, kuma a kan mahaifiyarka, a lõkacin da Na ƙarfafa ka da Rũhul Ƙudusi, kanã yiwa mutãne magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma kanã dattijo. Kuma a lõkacin da Na sanar da kai rubutu da hikima da Attaura da Injĩla, kuma a lõkacin da kake yin halitta daga lãkã kamar surar tsuntsu da izinĩNa, sa´an nan ka hura a cikinta sai ta zama tsuntsu da izinĩNa, kuma kanã warkar da haifaffen makaho da kuturu, da izinĩNa, kuma a lõkacin da kake fitar da matattu da izinĩNa, kuma a lõkacin da Na kange Banĩ Isrã´ĩla daga gare ka, a lõkacin da ka je musu da hujjõji bayyanannu, sai waɗanda suka kãfirta daga cikinsu suka ce: ´Wannan bã kõme ba ne, fãce sihiri bayyananne.´
111"Kuma a lõkacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawãriyãwa(2) cewa ku yi ĩmãni da Ni, kuma da ManzoNa. Suka ce: "Mun yi ĩmãni, kuma ka shaida da cewa lalle mu, mãsu sallamãwa ne."
112A lõkacin da Hawarãyãwa suka ce: "Ya Ĩsa ɗan Maryam! shin, Ubangijinka Yanã iyãwa Ya saukar da kaɓaki a kanmu daga samã?" (Ĩsã) Ya ce: "Ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai."
113Suka ce: "Munã nufin mu ci daga gare shi ne, kuma zukãtanmu su natsu kuma mu san cewa lalle ne, kã yi mana gaskiya, kuma mu kasance daga mãsu shaida a kansa."
114Ĩsã ɗan Maryam ya ce: "Yã Allah. Ubangijinmu! Ka saukar da kaɓaki a kanmu daga sama dõmin ya zama ĩdi ga na farkonmu da na ƙarshenmu, kuma ya zama ãyã daga gare Ka. Ka azurta mu, kuma Kai ne Mafĩfĩcin mãsu azurtawa."
115Allah Ya ce: "Lalle ne Nĩ mai saukar da shi ne a kanku sa´an nan wanda ya kãfirta daga gare ku, to, lalle ne Nĩ, Inã azabta shi, da wata azãba wadda bã Ni azabta ta ga kõwa daga tãlikai."
116Kuma a lõkacin da Allah Ya ce: "Yã Ĩsã ɗan Maryama! Shin, kai ne ka ce wa mutãne, ´Ku riƙe ni, ni da uwata, abubuwan bautãwa biyu, baicin Allah?" (Ĩsã) Ya ce: "Tsarkinka yã tabbata! Bã ya kasancewa a gare ni, in faɗi abin da bãbu wani hakki a gare ni. Idan nã kasance nã faɗe shi, to lalle Ka san shi, Kanã sanin abin da ke a cikin raina, kuma bã ni sanin abin da ke a cikin ranka. Lalle ne Kai Masanin abubuwan fake ne."
117"Ban faɗa musu ba fãce abin da Ka umurce ni da shi; watau: ´Ku bauta wa Allah Ubangijina kuma Ubangijinku;´ kuma nã kasance mai shaida a kansu matuƙar nã dawwama a cikinsu, sa´an nan a lõkacin da Ka karɓi raina(1) Kã kasance Kai ne mai tsaro a kansu, kuma Kai, a kan dukkan kõme, Halartacce ne.
118"Idan Ka azabta su, to lalle ne su, bãyinKa ne, kuma idan Ka gãfarta musu, to, lalle ne Kai ne Mabuwayi Mai hikima."
119Allah Ya ce: "Wannan ce rãnar da mãsu gaskiya, gaskiyarsu take amfãninsu. Sunã da gidãjen Aljanna, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu har abada. Allah Yã yarda da su, kuma sun yarda da Shi. wannan ne babban rabo mai girma."
120Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a cikinsu kuma shi, a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne.
Chapter 6 (Sura 6)
1Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya halitta sammai da ƙasa, kuma Ya sanya duffai da haske(1) , sa´an nan kuma waɗanda suka kãfirta, da Ubangijinsu suke karkacewa.
2Shi ne wanda Ya halitta ku daga lãkã, sa´an nan kuma Ya yanka ajali alhãli wani ajali ambatacce yanã wurinSa. Sa´an nan kuma ku kunã yin shakka.
3Kuma Shĩ ne Allah a cikin sammai, kuma a cikin ƙasa Yanã sanin asĩrinku da bayyanenku, kuma Yanã sanin abin da kuke yi na tsirfa.
4Kuma wata ãyã daga Ubangijinsu ba zã ta jħ musu ba, fãce su kasance, daga gare ta, mãsu bijirħwa.
5Sabõda haka, lalle sun ƙaryata (Manzo) game da gaskiya, a lõkacin da ta jħ musu, to lãbãrun abin da suka kasance sunã izgili da shi, zã su jħ musu.
6Shin, ba su gani ba, da yawa Muka halakar da wani ƙarni daga gabãninsu, Mun mallaka musu, a ckikin ƙasa, abin da ba Mu mallaka muku ba kuma Muka saki sama a kansu tanã ta zuba, kuma Muka sanya kõguna sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sa´an nan Muka halakã su sabõda zunubansu kuma Muka ƙãga halittar wani ƙarni na dabam daga bayansu?
7Kuma dã Mun sassaukar da wani littãfi, zuwa gare ka, a cikin takarda, sa´an nan suka taɓa shi da hannuwansu, lalle dã waɗanda suka kãfirta sun ce: "Wannan bai zama ba, face sihiri bayyananne."
8Suka ce: "Don me ba a saukar da wani malã´ika ba a gare shi?" To dã Mun saukar da malã´ika haƙĩƙa dã an hukunta al´amarin(2) sa´an nan kuma ba zã a yi musu jinkiri ba.
9Kuma dã Mun sanya malã´ika ya zama manzo lalle ne dã Mun mayar da shi mutum, kuma dã Mun rikita musu abin da suke rikitãwa.
10Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili da manzanni daga gabaninka, sai waɗanda suka yi izgilin, abin da suka kasance sunã izgili da shi ya fãɗa musu.
11Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa´an nan kuma ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance."
12Ka ce: "Na wãne ne abin da yake a cikin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Na Allah ne." Yã wajabta rahama ga kanSa. Lalle ne Yanã tãra ku zuwa ga Rãnar Ƙiyãma, babu shakka a gare Shi. Waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, to, sũ ba zã su yi ĩmani ba."
13"Kuma Shĩ ne da mallakar abin da ya yi kawaici a cikin dare da yini, kuma Shi ne Mai ji, Masani."
14Ka ce: "Shin, wanin Allah nike riƙo majiɓinci, (alhãli Allah ne ) Mai ƙãga halittar sammai da ƙasa, kuma Shi, Yanã ciyarwa, kuma ba a ciyar da Shi?" Ka ce: "Lalle ne nĩ, an umurce ni da in kasance farkon wanda ya sallama, kuma kada lalle ku kasance daga mãsu shirki."
15Kace: "Lalle ne nĩ inã tsõron azãbar Yini Mai girma, idan nã sãɓã wa Ubangijina."
16"Wanda aka jũyar da shi daga gare shi, a wannan Rãnar, to, lalle ne,( Allah) Yã yi masa rahama, Kuma wannan ne tsĩra bayyananniya."
17"Idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, babu mai kuranyħwa gare ta, fãce Shĩ, kuma idanYa shãfe ka da wani alhħri to shĩ ne, a kan kõme, Mai ĩkon yi."
18"Kuma Shĩ ne mai Tanƙwasa a kan bayinSa, kuma Shi ne Mai hikima, Masani."
19Ka ce: "Wane abu ne mafi girma ga shaida?" Ka ce: "Allah ne shaida a tsakãnina da tsakaninku. Kuma an yiwo wahayin wannan Alƙur´ãni dõmin in yi muku gargaɗi da shi, da wanda lãbãri ya kai gare shi. Shin lalle ne ku, haƙĩƙa, kunã shaidar cħwa, lalle ne tãre da Allah akwai wasu abũbuwan bautawa?" Ka ce: "Bã zan yi shaidar ( haka) ba." Ka ce: "Abin sani, Shi ne Abin bautãwa Guda kumã lalle ne nĩ barrantacce ne daga abin da kuke yi na shirki."
20Waɗanda Muka bã su Littãfi sunã sanin sa(1) kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, to, sũ bã su yin ĩmãni.
21Wãne ne mafi zãlunci daga wanda yake ƙirƙira karya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata game da ãyõyinsa? Lalle ne shĩ, azzalumai bã zã su ci nasara ba.
22Kuma rãnar da Muka tãra su gabã ɗaya, sa´an nan Mu ce wa waɗanda suka yi shirki: "Inã abõkan tãrayyarku waɗanda kuka kasance kunã riyãwa?"
23Sa´an nan kuma fitinarsu ba ta kasance ba, fãce dõmin sun ce: "Munã rantsuwa da Allah Ubangijinmu, ba mu kasance mãsu yin shirki ba."
24Ka dũba yadda suka ƙaryata kansu! Kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙira ƙaryarsa, ya ɓace daga gare su.
25Kuma daga cikinsu akwai wanda yake saurãre gare ka. Kuma Mun sanya abũbuwan rufi a kan zukãtansu dõmin kada su fahimcħ shi kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi. Kuma idan sun ga kõwace ãyã bã zã su yi ĩmãni da ita ba har idan sunjħ maka sunã jãyayya da kai, waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Wannan bai zama ba fãce tãtsũniyõyin mutãnen farko."
26Kuma sunã hanãwa daga gare shi, kuma sunã nĩsanta daga gare shi, kuma bã su halakarwa, fãce kansu, kuma bã su sansancħwa.
27Kuma dã kanã gani, a lõkacin da aka tsayar da su a kan wuta, sai suka ce: "Yã kaitõnmu! Dã ana mayar da mu, kuma bã zã mu ƙaryata ba daga ãyõyin Ubangijinmu, kuma zã mu kasance Daga mũminai."
28ôaha, abin da suka kasance suna ɓõyħwa, daga gabãni, ya bayyana a gare su. Kuma dã an mayar da su, lalle dã sun kõma ga abin da aka hana su daga barinsa. Kuma lalle ne sũ, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
29Kuma suka ce: "Ba ta zama ba, fãce rayuwarmu ta duniya, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
30Kuma dã kana gani, a lõkacin da aka tsayar da su ga UbangiJinsu, Ya ce: "Ashe wannan bai zama gaskiya ba?" Suka ce: "Nã´am, muna rantsuwa da Ubangijinmu!" Ya ce: "To ku ɗanɗani azaba sabõda abin da kuka kasance kuna yi na kãfirci."
31Lalle ne waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasara, har idan Sa´a ta je musu kwatsam, sai su ce: "Yã nadãmarmu a kan abin da muka yi sakaci a cikinta!" Alhãli kuwa su suna ɗaukar kayansu masu nauyi a kan bayayyakinsu. To, abin da suke ɗauka yã mũnana.
32Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba, fãce wãsa da shagala, kuma lalle ne, Lãhira ce mafi alhħri ga waɗanda suka yi taƙawa. Shin, ba za ku yi hankali ba?
33Lalle ne Muna sani cewa haƙĩƙa, abin da suke faɗa yana ɓãta maka rai. To, lalle ne su, bã su ƙaryata ka (a cikin zukatansu ) kuma amma azzãlumai da ãyõyin Allah suke musu.
34Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an ƙaryata manzanni daga gabãninka, sai suka yi haƙuri a kan abin da aka ƙaryata su, kuma aka cũtar da su, har taimakonMu ya je musu, kuma babu mai musanyãwa ga kalmõmin Allah. Kuma lalle ne (abin da yake natsar da kai) ya zo maka daga lãbãrin (annabãwan) farko.
35Kuma idan yã kasance cewa finjirewarsu tã yi nauyi a gare ka, to, idan kana iyãwa, ka nemi wani ɓullõ a cikin ƙasa, kõ kuwa wani tsãni a cikin sama dõmin ka zo musu da wata ãyã, ( sai ka yi). Kuma dã Allah Yã so haƙĩƙa dã Yã tãra su a kan shiriya. Sabõda haka, kada lalle ka kasance daga jãhilai.
36Abin sani kawai, waɗanda suke saurare ne suke karɓãwa, kuma matattu Allah Yake tãyar da su, Sa´an nan kuma zuwa gare Shi ake mayar da su.
37Kuma suka ce: "Don me ba a saukar da ãyã ba, a kansa, daga Ubangjinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Mai ĩko ne a kan Ya saukar da ãyã, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba."
38Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa kuma bãbu wani tsuntsu wanda yake tashi da fukafukinsa fãce al´umma ne misãlanku. Ba Mu yi sakacin barin kõme ba a cikin Littãfi, sa´an nan kuma zuwa ga Ubangjinsu ake tãra su.
39Kuma waɗanda suka ƙaryata gameda ãyõyinMu, kurãme ne kuma bebãye, acikin duffai. Wanda Allah Ya so Yanã ɓatar da shi, kuma wanda Ya so zai sanya shi a kan hanya madaidaiciya.
40Ka ce: "Shĩn, kun gan ku, idan azãbar Allah ta zo muku, kõ Sã´ar Tashin Kiyãma ta zo muku, shin wanin Allah kuke kira, idan dai kun kasance mãsu gaskiya?"
41"ôa, Shĩ dai kuke kira sai Ya kuranye abin da kuke kira zuwa gare Shi, idan Ya so, kuma kunã mantãwar abin da kuke yin shirkin tãre da shi."
42Kuma lalle Mun aika zuwa ga al´ummai daga gabãninka, sai Muka kãmã su da tsanani da cũta, tsammãninsu zã su ƙanƙan da kai,
43To, don me, a lõkacin da tsananinMu ya jħ musu ba su yi tawãlu´i ba? Kuma amma zukatansu sun ƙħƙashe kuma shaiɗan yã ƙawãta musu abin da suka kasance sunã aikatãwa.
44Sa´an nan kuma a lõkacin da suka manta da abin da aka tunãtar da su da shi, sai Muka bũɗe, a kansu, ƙõfõfin dukkan kõme, har a lõkacin da suka yi farin ciki da abin da aka ba su, Muka kãmã su, kwatsam, sai gã su sun yi tsuru tsuru.
45Sai aka katse ƙarshen mutãnen, waɗanda suka yi zãlunci. Kuma gõdiya tã tabbata ga Allah Ubangijin tãlikai.
46Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya riƙe jinku, da gannanku, kuma Ya sanya hãtimi a kan zukãtanku, wane abin bauttãwa ne, wanin Allah, zai jħ muku da shi?" Ka dũba yadda Muke sarrafa ãyõyi, sa´an nan kuma sũ, sunã finjirħwa.
47Ka ce: "Shin, kun gan ku, idan azãbar Allah ta jħ muku, kwatsam, kõ kuwa bayyane, shin, anã halakarwa, fãce dai mutãne azzãlumai?"
48Kuma bã Mu aikãwa da manzãnni fãce mãsu bayar da bushãra, kuma mãsu gargaɗi. To, wanda ya yi ĩmãni kuma ya gyãra aiki, to, babu tsõro a kansu, kuma ba su yin baƙin ciki.
49Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, azãba tanã shãfar su sabõda abin da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci.
50Ka ce: "Ba zan ce muku, a wurina akwai taskõkin Allah ba. Kuma ba ni sanin gaibi, kuma ba ni gaya muku cħwa ni malã´ika ne. Ba ni bi, fãce abin da ake yiwo wahayi zuwa gare ni." Ka ce: "Shin, makãho da mai gani sunã daidaita? Shin fa, ba ku yin tunãni?"
51Kuma ka yi gargaɗi da shi ga waɗanda suke jin tsõron a tãra su zuwa ga Ubangijinsu, ba su da wani masõyi baicinSa, kuma babu mai cħto, tsammãninsu, sunã yin taƙawa.
52Kuma kada ka kõri waɗanda(1) suke kiran Ubangijinsu sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa, babu wani abu daga hisãbinsu a kanka, kuma babu wani abu daga hisãbinka a kansu, har ka kõre su ka kasance daga azzãlumai.
53Kuma kamar wannan ne, Muka fitini sãshensu da sãshe, dõmin su ce: "Shin waɗannan ne Allah Ya yi falala a kansu daga tsakãninmu?" Shin, Allah bai zama Mafi sani ba ga mãsu gõdiya?
54Kuma idan waɗanda suke yin ĩmãni da ãyõyinMu suka jħ maka, sai ka ce: "Aminci ya tabbata a gareku; Ubangjinku Ya wajabta rahama ga kanSa, cħwa lalle ne wanda ya aikata aibi da jãhilci daga cikinku, sa´an nan kuma ya tũba daga bãyansa, kuma ya gyãra, to, lalle Shi, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai."
55Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, kuma dõmin hanyar mãsu laifi ta bayyana.
56Ka ce: "Lalle ne ni, an hana ni in bauta wa waɗanda kuke kira daga baicin Allah." Ka ce: "Ba ni bin son zũciyõyinku, (dõmin in nã yi haka) lalle ne, nã ɓace. A sa´an nan, kuma ban zama daga shiryayyu ba."
57Ka ce: "Lalle ne inã kan hujja daga Ubangjina, kuma kun ƙaryata (ni) game da Shi; abin da kuke nħman gaugãwarsa, bã ya wurina, hukunci kuwa bai zama ba fãce, ga Allah, Yanã bãyar da lãbãrin gaskiya, kuma shĩ ne mafi alhħrin mãsu rarrabħwa."
58Ka ce: "Lalle ne, dã a wurina akwai abin da kuke nħman gaugãwa da shi, haƙĩƙa dã an hukunta al´amarin, a tsakãnina da tsakãninku, kuma Allah Shĩ ne Mafi sani ga azzũlumai."
59Kuma a wurinSa mabũdan(1) gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙħƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa.
60Kuma Shĩ ne wanda Yake karɓar(1) rãyukanku da dare, kuma Yanã sanin abin da kuka yãga da rãna, sa´an nan Yanã tãyar da ku a cikinsa, dõmin a hukunta ajali ambatacce sa´an nan kuma zuwa gare shi makõmarku take, sa´an nan kuma Ya ba ku lãbari da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
61Kuma Shĩ ne Mai rinjãya bisa ga bãyinSa, kuma Yanã aikan mãsu tsaro a kanku, har idan mutuwa ta jħ wa ɗayanku, sai manzanninMu su karɓi ransa alhãli su ba su yin sakaci.
62Sa´an nan kuma a mayar da su zuwa ga Allah Ubangjinsu na gaskiya. To! A gare shi hukunci yake, kuma Shi ne Mafi gaugãwar mãsu bincike.
63Ka ce: "Wane ne Yake tsĩrar da ku daga duhũhuwan tudu da ruwa, kunã kiran Sa bisa ga ƙanƙan da kai kuma a ɓõye: ´Lalle ne idan Ka tsĩrar da mu daga wannan (masĩfa), haƙĩƙa, muna kasancħwa daga mãsu gõdiya?´"
64Ka ce: "Allah ne Yake tsĩrar da ku daga gare ta, kuma daga dukan baƙin ciki sa´an nan kuma ku, kunã yin shirki!"
65Ka ce: "Shĩ ne Mai ĩko a kan Ya aika da wata azãba a kanku daga bisanku, kõ kuwa daga ƙarƙashin ƙafãfunku, kõ kuwa Ya gauraya ku ƙungiyõyi, kuma Ya ɗanɗanã wa sãshenku masĩfar sãshe." "Ka dũba yadda Muke sarrafa ãyõyi, tsammãninsu sunã fahimta!"
66Kuma mutãnenka sun ƙaryata (ka) game da Shi, alhãli kuwa Shi ne gaskiya. Ka ce: "Nĩ ban zama wakĩli a kanku ba."
67"Akwai matabbata ga dukan lãbãri, kuma zã ku sani."
68Kuma idan kã ga waɗanda suke kũtsawa a cikin ãyõyinMu, to, ka bijire daga gare su, sai sun kũtsa a cikin wani lãbãri waninsa. Kuma imma dai shaiɗan lalle ya mantar da kai, to, kada ka zauna a bayan tunãwa tãre da mutãne azzãlumai.
69Kuma babu wani abu daga hisãbinsu (mãsu kutsãwa a cikin ayõyin Allah (a kan mãsu taƙawa amma akwai tunãtarwa (a kansu), tsãmmãninsu (mãsu kutsawar) zã su yi taƙawa.
70Kuma ka bar waɗanda suka riƙi addĩninsu abin wãsa(1) da wargi alhãli rãyuwar dũniya tã rũɗe su, kuma ka tunãtar game da shi (Alƙur´ãni): Kada a jħfa rai a cikin halaka sabõda abin da ya tsirfanta; ba shi da wani majiɓinci baicin Allah, kuma babu wani mai cħto; kuma, kõ ya daidaita dukan fansa, ba zã a karɓa ba daga gare shi. Waɗancan ne aka yanke wa tsammãni sabõda abin da suka tsirfanta; sunã da wani abin shã daga ruwan zãfi, da wata azãba mai raɗaɗi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci.
71Ka ce: "Shin, zã mu yi kiran abin da bã ya amfãninmu, baicin Allah, kuma bã ya cũtar damu, kuma a mayar da mu a kan dugãduganmu, a bayan Allah Yã shiryar da mu kamar wanda shaiɗãnu suka kãyar da shi a cikin ƙasa, yanã mai ɗĩmuwa, yanã da abõkai sunã kiran sa zuwa ga shiriya, ´Ka zo mana´"(2) Kace: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya. Kuma an umurce mu, mu sallama wa Ubangijin tãlikai."
72"Kuma (an ce mana): Ku tsai da salla kuma ku bĩ shi (Allah) da taƙawa kuma Shi ne wanda Yake zuwa gare Shi ake tãra ku."
73Kuma Shĩ ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da mulkinSa, kuma a Rãnar da Yake cħwa: "Ka kasance," sai abu ya yi ta kasancħwa. MaganarSa ce gaskiya, kuma gare Shi mulki yake a Rãnar da ake bũsa a cikin ƙaho. Masanin fake da bayyane ne, Kuma Shi ne Mai hikima Masani.
74Kuma a lõkacin da Ibrãhĩma ya ce wa ubansa Ãzara: "Shin, kanã riƙon gumãka abũbuwan bautãwa? Lalle nĩ, inã ganin ka kai da mut?nenka, a cikin ɓata bayyananniya."
75Kuma kamar wancan ne, Muke nũna wa Ibrãhĩma mulkin sammai da ƙasa, kuma dõmin ya kasance daga mãsu yaƙĩni.
76To, a lõkacin da dare ya rufe a kansa, ya ga wani taurãro, ya ce: "Wannan ne, ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da ya faɗi, ya ce: "Ba ni son mãsu fãɗuwa."
77Sa´an nan a lõkacin da ya ga watã yanã mai bayyana, ya ce: "Wannan ne Ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da ya fãɗi, ya ce: "Lalle ne idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haƙĩƙa, inã kasancħwa daga mutãne ɓatattu."
78Sa´an nan a lõkacin da ya ga rãnã tanã bayyana, ya ce: "Wannan shĩ ne Ubangijina, wannan ne mafi girma?" Sa´an nan a lõkacin da ta fãɗi, ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne ni barrantacce nake daga abin da kuke yi na shirki."
79"Lalle ne nĩ, na fuskantar da fuskata ga wanda, Ya ƙãga halittar sammai da ƙasa, inã mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bã ni cikin mãsu shirki."
80Kuma mutãnensa suka yi musu da shi. Ya ce: "Shin kunã musu da ni a cikin sha´anin Allah, alhãli kuwa Yã shiryai da ni? Kuma bã ni tsõron abin da kuke yin shirki da shi, fãce idan Ubangijina Yã so wani abu. Ubangijina Ya yalwaci dukkan kõme da ilmi. Shin, ba zã ku yi tunãni ba?"
81"Kuma yãyã nake jin tsõron abin da kuka yi shirki da shi, kuma ba ku tsõron cħwa lalle ne kũ, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sãshen biyu ne mafi cancanta da aminci, idan kun kasance kunã sani?"
82"Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma ba su gauraya ĩmãninsu da zãlunci ba, waɗannan sunã da aminci, kuma sũ ne shiryayyu."
83Kuma waccan ita ce hujjarMu, Mun bayãr da ita ga Ibrãhĩma a kan mutãnensa. Munã ɗaukaka wanda Muka so da darajõji. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani.
84Kuma Muka bã shi Is´hãƙa da Yãƙubu, dukansu Mun shiryar, kuma Nũhu Mun shiryar da shi a gabãni, kuma daga zuriyarsa akwai Dãwũda da Sulaimãnu da Ayyũba, da Yũsufu da Mũsã da Hãrũna, kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
85Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Ilyasu dukansu daga sãlihai suke.
86Da Ismã´la da Ilyasa, a da Yũnusa da Luɗu, kuma dukansu Mun fĩfĩtã su a kan tãlikai.
87Kuma daga ubanninsu, da zũriyarsu, da ´yan´uwansu, kuma Muka zãɓe su, kuma Muka shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya.
88Wancan ne shiryarwar Allah, Yanã shiryar da wanda Yake so daga bayinSa. Kuma dã sun yi shirki dã haƙĩƙa abin da suka kasance sunã ,aikatãwa yã lãlãce.
89Waɗancan ne waɗanda Muka bai wa Littãfi da hukunci da Annabci. To idan waɗannan (mutãne ) sun kãfirta da ita, to, haƙĩƙa, Mun wakkala wasu mutãne gare ta, ba su zama game da ita kãfirai ba.
90Waɗancan ne Allah Ya shiryar, sabõda haka ka yi kõyi da shiryarsu. Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijãra. Shĩ (Alƙur´ãni) bai zama ba fãce tunãtarwa ga tãlikai."
91Kuma ba su ƙaddara Allah a kan hakkin ƙaddara shi ba, a lõkacin da suka ce: "Allah bai saukar da kõme ba ga wani mutum." Ka ce: "Wãne ne ya saukar da Littãfi wanda Mũsã ya zo da shi, yanã haske da shiriya ga mutãne, kunã sanya shi takardu, kũna bayyana su, kuma kunã ɓõye mai yawa, kuma an sanar da ku abin da ba ku sani ba, ku da ubanninku?" Ka ce: "Allah,"(1) sa´an nan ka bar su a cikin sharhõliyarsu sunã wãsã.
92Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, mai gaskata wanda yake a gabansa ne, kuma dõmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda yake gefenta. Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da Lãhira sunã ĩmãni da shi (Alƙur´ãni), kuma sũ, a kan sallarsu, sunã tsarħwa.
93Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar?" Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã´iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai."
94Kuma lalle ne haƙĩƙa, kun zo Mana ɗai ɗai, kamar yadda Muka halittã ku a farkon lõkaci. Kuma kun bar abin da Muka mallaka muku a bayan bayayyakinku, kuma ba Mu gani a tãre da kũ ba, macħtanku waɗanda kuka riya cħwa lalle ne sũ, a cikinku mãsu tãrayya ne. Lalle ne, h?ƙĩƙa, k?me yã yanyanke a tsakãninku, kuma abin da kuka kasance kunã riyãwa ya ɓace daga gare ku.
95Lalle ne, Allah ne Mai ts?gewar ƙw?yar hatsi da kwalfar gurtsu. Yan? fitar da mai rai daga mamaci, kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne daga mai rai.(1) Wannan ne Allah. To, yãya ake karkatar da ku?
96Mai tsãgħwar sãfiya, kuma Ya sanya dare mai natsuwa, kuma da rãna da watã a bisa liss?fi. Wannan ne ƙaddarãwar Mabuwãyi Masani.
97Kuma Shi ne Ya sanya muku taurãri dõmin ku shiryu da su a cikin duffan tudu da ruwa. Lalle ne Mun bayyana ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke sani.
98Kuma Shi ne Ya ƙãga halittarku daga rai guda, sa´an nan da mai tabbata da wanda ake ajħwa. Lalle ne Mun bayyanã ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke fahimta.
99Kuma Shi ne Ya saukar da ruwa daga sama, Muka fitar da tsiron dukkan kõme game dã shi, sa´an nan Muka fitar da kõre daga gare shi, Muna fitar da kwãya ɗamfararriya daga gare shi (kõren),(2) kuma daga dabĩno daga hirtsinta akwai dumbuje-dumbuje makusanta, kuma (Muka fitar) da gõnaki na inabõbi da zãitũni da rummãni, mãsu kamã da jũna da wasun mãsu kama da jũna. Ku dũba zuwa ´ya´yan itãcensa, idan ya yi ´ya´yan, da nunarsa. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyõyi ga waɗanda suke yin ĩmãni.
100Kuma suka sanya wa Allah abõkan tãrayya, aljannu, alhãli kuwa (Shi) Ya halitta su. Kuma sun ƙirƙira masa ɗiya da ´yã´ya, bã da ilmi ba. TsarkinSa yã tabbata! Kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke sifantãwa.
101Mafarin(3) halittar sammai da ƙasa. Yãya ɗã zai zama a gare Shi alhãli kuwa mãta ba ta kasance ba, a gare Shi, kuma Ya halitta Dukkan k?me, kuma Shĩ, game da dukan kõme, Masani ne?
102Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme.
103Gannai bã su iya riskuwarSa, kuma Shĩ Yanã riskuwar gannai, kuma Shĩ ne Mai tausas?wa, Masani.
104Lalle ne abũbuwan lũra sun je muku daga Ubangijinku, to, wanda ya kula, to, dõmin kansa, kuma wanda ya makanta, to, laifi yanã a kansa, kuma nĩ, a kanku, bã mai tsaro ba ne.
105Kamar wannan ne Muke sarrafa ãyõyi, kuma dõmin su ce: "Kã karanta!" Kuma dõmin Mu bayyana shi ga mutãne waɗanda sunã sani.
106Ka bi abin da aka yi wahayi zuwa gare ka daga Ubangijinka; babu wani abin bautãwa fãce Shi, kuma ka bijire daga mãsu shirki.
107Kuma dã Allah Yã so, dã ba su yi shirki ba, kuma ba Mu sanya ka mai tsaro a kansu ba, kuma ba kai ne wakĩli a kansu ba.
108Kuma kada ku zãgi waɗanda suke kira, baicin Allah, har su zãgi Allah bisa zãlunci, ba, da ilmi ba. Kamar wannan ne Muka ƙawãta ga kõwace al´umma aikinsu, sa´an nan zuwa ga Ubangijinsu makõmarsu take, sa´an nan Ya ba su lãbari da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
109Kuma suka yi rantsuwa da Allah iyakar rantsuwõyinsu (cħwa) lalle ne idan wata ãyã ta j musu, haƙĩƙa, sunã yin ĩmãni da ita. Ka ce: "Abin sani kawai, ãyõyi a wurin Allah suke. Kuma mħne ne zai sanya ku ku sansance cħwa, lalle ne su, idan ãyõyin sun je, ba zã su yi ĩmãni ba?"
110Kuma Munã jujjũya zukãtansu da ganansu, kamar yadda ba su yi ĩmãni da shi ba a farkon lõkaci kuma Munã barin su a cikin kũtsãwarsu, sunã ɗĩmuwa.
111Kuma dã a ce, lalle Mũ Mun saukar da Malã´iku zuwa gare su, kuma matattu suka yi musu magana, kuma Muka tãra dukkan kõme a kansu, gungu-gungu, ba su kasance sunã iya yin ĩmãni ba, sai fa idan Allah Yã so, Kuma amma mafi yawansu sunã jãhiltar haka.
112Kuma kamar wancan ne Muka sanya wa kõwane Annabi maƙiyi; shaiɗãnun mutãne da aljannu, sãshensu yanã yin ishãra(1) zuwa sãshe da ƙawãtaccen zance bisa ga rũɗi. Kuma dã Ubangijinka Yã so, dã ba su aikatã shi ba, don haka ka bar su da abin da, suke ƙirƙirãwa.
113Kuma dõmin zukãtan waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba su karkata saurãrħ zuwa gareshi, kuma dõmin su yarda da shi, kuma dõmin su kamfaci abin da suke mãsu kamfata.
114Shin fa, wanin Allah nake nħma ya zama mai hukunci, alhãli kuwa Shĩ ne wanda Ya saukar muku da Littãfi abin rabħwa daki-daki? Kuma waɗanda Muka bai wa Littãfi sunã sanin cħwa lalleshi (Alƙur´ãni) abin saukarwa ne daga Ubangijinka, da gaskiya? Sabõda haka kada ku kasance daga mãsu shakka.
115Kuma kalmar Ubangijinka tã cika, tanã gaskiya(2) da ãdalci. Babu mai musanyãwa ga kalmõminSa, kuma Shi ne Maiji, Masani.
116Kuma idan ka bi mafiya yawan waɗanda suke a cikin ƙasa da ɗã´a sunã ɓatar da kai daga hanyar Allah. Ba su bin kõme sai fãce ƙaddari-faɗi(3) suke yi.
117Lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Mafi sani ga wanda yake ɓacħwa daga hanyarsa kuma Shi ne mafi sani ga masu shiryuwa.
118Sabõda haka ku ci daga abin da aka ambaci sũnan Allah(4) kansa, idan kun kasance mãsu ĩmãni da ãyõyinSa.
119Kuma mħne ne ya sãme ku, bã zã ku ci ba daga abin da aka ambaci sũnan Allah a kansa,alhãli kuwa, haƙĩƙa, Ya rarrabe, muku daki-daki, abin da Ya haramta a kanku, fãce fa abin da aka bukãtar da ku bisa lalũra zuwa gare shi? Kuma lalle ne mãsu yawa sunã ɓatarwa, da son zũciyõyinsu, ba da wani ilmi ba. Lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Mafi sani ga mãsu ta´addi.
120Kuma ku bar bayyanannen zunubi da ɓõyayyensa. Lalle ne waɗanda suke tsiwurwurin zunubi za a sãka musu da abin da suka kasance sunã kamfata.
121Kada ku ci daga abin da ba a ambaci sũnan Allah ba a kansa(1) . Kuma lalle ne shĩ fãsiƙanci ne. Kuma lalle ne, shaiɗãnu, haƙĩƙa, suna yin ishãra zuwa ga masõyansu, dõmin su yi jãyayya da ku. Kuma idan kuka yi musu ɗã´a, lalle ne kũ, haƙĩƙa, mãsu shirki ne.
122Shin, kuma wanda ya kasance matacce sa´an nan Muka rãyar da shi, kuma Muka sanya wani haske dõminsa, yanã tafiya da shi, yanã zama kamar wanda misãlinsa yanã cikin duffai, shĩ kuma ba mai fita ba daga gare su? Kamar wancan ne aka ƙawãta wa kãfirai abin da suka kasance sunã aikatãwa.
123Kuma kamar wancan ne Mun sanya a cikin kõwace alƙarya, shugabanni sũ ne mãsu laifinta dõmin su yi mãkirci a cikinta, alhãli kuwa ba su yin makirci fãce ga rayukansu, kuma ba su sansancħwa.
124Kuma idan wata ãyã ta je musu sai su ce: "Ba zã mu yi ĩmãni ba, sai an kãwo mana kamar abin da aka kãwo wa manzannin Allah." Allah Mafi sanin inda Yake sanya manzancinSa.(2) Wani wulaƙanci(3) a wurin Allah da wata azãba mai tsanani zã su sãmi waɗanda suka yi laifi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na mãkirci.
125Dõmin haka wanda Allah Ya yi nufin ya shiryar da shi sai ya bũɗa ƙirjinsa dõmĩn Musulunci, kuma wanda Ya yi nufin Ya ɓatar da shi, sai Ya sanya ƙirjinsa mai ƙunci matsattse, kamar dai yanã tãkãwa(1) ne a ckin sama. Kamar wannan ne Allah Yake sanyãwar ƙazanta a kan waɗanda bã su yin ĩmãni.
126Wannan ita ce hanya ta Ubangijinka madaidaiciya. Lalle ne Mun bayyana ãyõyi daki-daki ga mutãne mãsu karɓar tunãtarwa.
127Sunã da gidan aminci a wurin Ubangjinsu, kuma Shĩ ne Majiɓincinsu, sabõda abin da suka kasance sunã aikatãwa.
128Kuma rãnar da yake tãra su gaba ɗaya (Yanã cħwa): "Yã jama´ar aljannu! Lalle ne kun yawaita kanku daga mutãne." Kuma majiɓantansu daga mutãne suka ce: "Yã Ubangjinmu! Sãshenmu(2) ya ji dãɗi da sãshe, kuma mun kai ga ajalinmu wanda Ka yanka mana!" (Allah) Ya ce: "Wuta ce mazaunarku, kunã madawwama a cikinta, sai abin da Allah Ya so. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani."
129Kuma kamar wancan ne Muke jiɓintar da sãshen azzãlumai ga sãshe, sabõda abin da suka kasance sunã tãrãwa.
130Yã jama´ar aljannu da mutãne! Shin, manzanni daga gare ku ba su jħ muku ba sunã lãbarta ãyõyiNa a kanku, kuma sunã yi muku gargaɗin haɗuwa da wannan yini nãku? Suka ce: "Mun yi shaida a kan kãwunanmu." Kuma rãyuwar dũniya tã rũɗħ su. Kuma suka yi shaida a kan kãwunansu cħwa lalle ne sũ, sun kasance kãfirai.
131Wancan kuwa sabõda Ubangijinka bai kasance Mai halaka alƙaryõyi sabõda wani zãlunci ba ne, alhãli kuwa mutãnensu sunã jãhilai.(3)
132Kuma ga kõwanne,(1) akwai darajõji daga abin da suka aikata. Kuma Ubangijinka bai zama mai shagala ba daga abin da suke aikatãwa.
133Kuma Ubangijinika Wadãtacce(2) ne Ma´abũcin rahama. Idan Yã so zai tafi da ku, kuma Ya musanya daga bãyanku, abin da Yake so, kamar yadda Ya ƙãga halittarku daga zũriyar wasu mutãne na dabam.
134Lalle ne abin da ake yi muku wa´adi lalle mai zuwa ne kuma ba ku zama mãsu buwãya ba,
135Ka ce: "Yã ku mutãnena! Ku yi aiki a kan halinku, lalle ne nĩ mai aiki ne, sa´an nan da sannu zã ku san wanda ãƙibar gida zã ta kasance a gare shi. Lalle ne shi, azzãlumai bã zã su ci nasarã ba."
136Kuma sun sanya wani rabõ ga Allah daga abin da Ya halitta daga shũka da dabbõbi, sai suka ce: "Wannan(3) na Allah ne," da riyãwarsu "Kuma wannan na abũbuwan shirkinmu ne." Sa´an nan Abin da ya kasance na abũbuwan shirkinsu, to, bã ya sãduwa zuwa Allah, kuma abin da ya kasance na Allah, to, shĩ yanã sãduwa zuwa ga abũbuwan shirkinsu. Tir da hukuncinsu!
137Kuma kamar wancan ne abũbuwan shirkinsu suka ƙãwata wa mãsu yawa, daga mãsu shirkin; kashewar(4) ´ya´yansu, dõmin su halaka su kuma dõmin su rikitar da addininsu a gare su, kuma dã Allah Yã so dã ba su aikatã shi ba. Sabõda haka ka bar su da abin da suke ƙirƙirãwa.
138Kuma suka ce: "Waɗannan dabbõbi da shũka hanannu ne; bãbu mai ɗanɗanar su fãce wanda muke so," ga riyãwarsu. Da wasu dabbõbi an hana bãyayyakinsu, da wasu dabbõbi bã su ambatar sũnan Allah a kansu, bisa ƙirƙiren ƙarya gare Shi. Zai sãka musu da abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa.
139Kuma suka ce: "Abin da yake a cikin cikkunan waɗannan dabbõbi kħɓantacce ne ga mazanmu, kuma hananne ne a kan mãtan aurenmu. Kuma idan ya kasance mũshe, to, a cikinsa sũ abõkan tãrayya ne, zai sãka musu sifantãwarsu. Lalle ne Shĩ, Mai hikima ne, Masani."
140Lalle ne waɗanda suka kashe ɗiyansu sabõda wauta, ba da ilmi ba, sun yi hasãra! Kuma suka haramta abin da Allah Ya azurta su, bisa ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne sun ɓace, kuma ba su kasance mãsu shiryuwa ba.
141Kuma Shĩ ne Wanda Ya ƙãga halittar gõnaki mãsu rumfuna da wasun mãsu rumfuna da dabĩnai da shũka, mai sãɓãwa ga ´yã´yansa na ci, da zaituni da rummãni mai kama da jũna da wanin mai kama da jũna. Ku ci daga ´ya´yan itãcensa, idan ya yi ´yã´yan, kuma ku bãyar da hakkinSa a rãnar girbinsa, kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shĩ, ba Ya son mabarnata.
142Kuma daga dabbõbi (Ya ƙãga halittar) mai ɗaukar kãya da ƙanãna; Ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, kuma kada ku bi zambiyõyin shaiɗan: Lalle ne shi, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne.
143Nau´õ´i takwas daga tumãkai biyu, kuma daga awãkai biyu; ka ce: Shin mazan biyu ne Ya haramta ko mãtan biyu, ko abin da mahaifar mãtan biyu suka tattara a kansa? Ku bã ni lãbãri da ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya.
144Kuma daga rãƙuma akwai nau´i biyu, kuma daga shãnu biyu; ka ce: Shin, mazan biyu ne Ya hana ko mãtan biyu Ya hana, kõ abin da mahaifar mãtan biyu suka tattara a kansa? Kõ kun kasance halarce ne a lõkacin da Allah Ya yi muku wasiyya da wannan? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, dõmin ya ɓatar da mutãne bã da wani ilmi ba? Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
145Ka ce: "Bã ni sãmu,(1) a cikin abin da aka yõ wahayi zuwa gare Ni, abin haramtãwa a kan wani mai ci wanda yake cin sa fãce idan ya kasance mũshe kõ kuwa jini abin zubarwa kõ kuwa nãman alade, to lalle ne shi ƙazanta ne, kõ kuwa fãsiƙanci wanda aka kurũrũta, dõmin wanin Allah da shi." Sa´an nan wanda larũra ta kãmã shi, bã mai fita jama´a ba, kuma bã mai ta´addi ba, to, lalle Ubangijinka Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
146Kuma a kan waɗanda suka tũba (Yahũdu) Mun haramta(2) dukan mai akaifa, kuma daga shãnu da bisãshe Mun haramta musu kitsattsansu fãce abin da bãyukansu suka ɗauka, kõ kuwa kãyan ciki, kõ kuwa abin da ya garwaya da ƙashĩ. Wannan ne Muka sãka musu sabõda zãluncinsu, kuma Mu, haƙĩƙa, Mãsu gaskiya ne.
147To, idan sun ƙaryatã ka, sai ka ce: "Ubangijinku Ma´abũcin rahama ne Mai yalwa; kuma bã a mayar da azãbarSa daga mutãne mãsu laifi."
148Waɗanda suka yi shirki(1) zã su ce: "Dã Allah Yã so dã ba mu yi shirki ba, kuma dã ubanninmu ba su yi ba, kuma dã ba mu haramta wani abu ba." Kamar wannan ne mutãnen da suke a gabãninsu suka ƙaryata, har suka ɗanɗani azãbarMu. Ka ce: "Shin, kunã da wani ilmi a wurinku dõmin ku fito mana da shi? Bã ku bin kõme fãce zato kuma ba ku zama ba fãce ƙiri-faɗi kawai kuke yi."
149Ka ce: "To Allah ne da hujja isasshiya, sabõda haka: Dã Yã so, dã Yã shiryar da ku gabã ɗaya."
150Ka ce: "Ku kãwo shaidunku, waɗanda suke bãyar da shaidar cħwa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kãwo shaida kada ka yi shaida tãre da su. Kuma kada ka bi son zũciyõyin waɗanda suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, da waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira, alhãli kuwa sũ daga Ubangijinsu suna karkacħwa.
151Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwan alf?sha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta.
152Kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mũdu da sikħli da ãdalci, bã Mu kallafã wa rai fãce iyãwarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi ãdalci, kuma ko dã yã kasance ma´abũcin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. Wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: tsamm?ninku, kunã tunãwa.
153Kuma lalle wannan ne tafarkĩNa, yana madaidaici: Sai ku bĩ shi, kuma kada ku bi wasu hanyõyi, su rarrabu da ku daga barin hanyãTa. Wannan ne Allah Ya yi muku wasiyya da shi tsammãninku, kunã yin taƙawa.
154Sa´an nan kuma Mun bai wa Mũsã Littãfi, yanã cikakke bisa ga wanda ya kyautata (hukuncin Allah) da rarrabħwa, daki-daki, ga kõwane abu, da shiriya da rahama, tsammãninsu,(1) sunã yin ĩmãni da haɗuwa da Ubangijinsu.
155Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, sai ku bĩ shi kuma ku yi taƙawa, tsammãninku, anã jin ƙanku.
156(Dõmin) kada ku ce: "Abin sani kawai, an saukar da littãfi a kan ƙungiya(2) biyu daga gabãninmu, kuma lalle ne mũ, mun kasance, daga karatunsu, haƙĩƙa, gãfilai."
157Kõ kuwa ku ce: "Dã dai lalle mũ an saukar da Littãfi a kanmu, haƙĩƙa, dã mun kasance mafiya,shiryuwa daga gare su." To, lalle ne wata hujja bayyananniya, daga Ubangijinku, tã zo muku, da shiriya da rahama. To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙaryata game da ãyõyin Allah, kuma ya hinjire daga barinsu? Zã Mu sãka wa waɗanda suke hinjirħwa daga barin ãyõyinMu da mugunyar azãba, sabõda abin da suka kasance sunã yi na hinjirħwa.
158Shin, sunã jiran (wani abu), fãce dai malã´iku(1) su je musu kõ kuwa Ubangijinka Ya je, kõ kuwa sãshen ãyõyin Ubangijinka ya je. A rãnar da sãshen ãyõyin Ubangijinka yake zuwa, ĩmãnin rai wanda bai kasance yã yi ĩmãnin ba a gabãni, kõ kuwa ya yi tsiwirwirin wani alhħri, bã ya amfãninsa. Ka ce: "Ku yi jira: Lalle ne mũ, mãsu jira ne."
159Lalle ne waɗanda(2) suka rarraba addininsu, kuma suka kasance ƙungiyã-ƙungiyã, kai ba ka zama daga gare su ba, a cikin kõme: abin sani kawai al´amarinsu zuwa ga Allah yake. Sa´an nan Ya bã su lãbãri game da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
160Wanda ya zo da kyakkyãwan aiki guda, to, yanã da gõma ɗin misãlansa. Kuma wanda ya zo da mũgun aiki gũda, to, bã zã a sãka masa ba fãce da misãlinsa. Kuma sũ bã a zãluntar su.
161Ka ce: "Lalle nĩ, Ubangijina Yã shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addĩni, ƙĩmantãwa ( ga abũbuwa), mai aƙĩdar Ibrãhĩm, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."
162Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai."
163"Bãbu abõkin tãrayya a gare Shi. Kuma da wancan aka umurce ni, kuma ni ne farkon mãsu sallamãwa."
164Ka ce: "Shin wanin Allah nake nħma ya zama Ubangiji, alhãli kuwa Shĩ ne Ubangijin dukan kõme? Kuma wani rai bã ya yin tsirfa fãce dõmin kansa, kuma mai ɗaukar nauyi, bã ya ɗaukar nauyin wani, sa´an nan kuma kõmawarku zuwa ga Ubangijinku take; Sa´an nan Yã bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance, a cikinsa, kunã sãɓã wa jũnã?"
165"Kuma Shĩ ne wanda Ya sanya ku mãsu maye wa jũna ga ƙasa. Kuma Ya ɗaukaka sãshenku bisa ga sãshe da darajõji; dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku." Lalle ne, Ubangijinka Mai gaggãwar uƙkũba ne, kuma lalle ne Shi, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
Chapter 7 (Sura 7)
1A. L̃. M̃. Ṣ̃.
2Littãfi ne aka saukar zuwa gare ka, kada wani ƙunci ya kasance a cikin ƙirjinka daga gare shi, dõmin ka yi gargaɗi da shi. Kuma tunãtarwa ne ga mũminai.
3Ku bi abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, kuma kada ku dinga bin wasu majiɓinta baicinSa. Kaɗan ƙwarai kuke tunãwa.
4Kuma da yawa wata alƙarya Muka halaka ta, sai azãbarMu ta jħ mata da dare kõ kuwa sunã mãsu ƙailũla.
5Sa´an nan bãbu abin da yake da´awarsu, a lõkacin da azãbarMu ta jħ musu, fãce suka ce: "Lalle ne mũ muka kasance mãsu zãlunci,"
6Sa´an nan lalle ne Munã tambayar waɗanda aka aika zuwa gare su, kuma lalle Munã tambayar Manzannin.
7Sa´an nan haƙĩƙa Munã bã su lãbãri da ilmi kuma ba Mu kasance mãsu fakuwa ba.
8Kuma awo a rãnar nan ne gaskiya. To, wanda sikħlansa suka yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu cin nasara.
9Kuma wanda sikħlansa suka yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu, sabõda abin da suka kasance, da ãyõyinMu, sunã yi na zãlunci.
10Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarautar da ku, a cikin ƙasa, kuma Mun sanya muku abũbuwan rãyuwa, a cikinta; kaɗan ƙwarai kuke gõdħwa.
11Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halittã ku sa´an nan kuma Mun sũrantã ku, sa´an nan kuma Mun ce wa malã´iku: "Ku yi sujada ga Ãdam." Sai suka yi sujada fãce Iblĩs, bai kasance daga mãsuyin sujadar ba.(1)
12Ya ce: "Mħne ne ya hana ka, ba ka yi sujada ba, a l?kacin da Na umurce ka?" Ya ce: "Nĩ ne mafĩfĩci daga gare shi, Ka halitta ni daga wuta alhãli kuwa Kã halitta shi daga lãka."
13Ya ce: "To, ka sauka daga gare ta; d?min b? ya kasancħwa a gare ka ga ka yi girman kai a cikinta. Sai ka fita. Lalle ne kanã daga mãsu ƙasƙanci."
14Ya ce: "Ka yi mini jinkiri zuwa ga rãnar da ake tãyar(1) da su."
15Ya ce: "Lalle ne, kanã daga waɗanda aka yi wa jinkiri."(2)
16Ya ce: "To inã rantsuwa da halakarwar da Ka yi mini, lalle ne, inã zaune musu tafarkinKa madaidaici."
17"Sa´an nan kuma haƙĩƙa, Inã je musu daga gaba gare su, kuma daga bãya gare su, kuma daga jihõhin damansu da jihõhin hagunsu; Kuma bã zã ka sãmi mafi yawansu mãsu gõdiya ba."
18Ya ce: "Ka fita daga gare ta kanã abin zargi kõrarre. Lalle ne wanda ya bĩ ka daga gare su, haƙĩƙa, zã Ni cika jahannama daga gare ku, gabã ɗaya."
19"Kuma ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci Wannan itãciya, har ku kasance daga azzãlumai."
20Sai Shaiɗan ya sanya musu waswãsi dõmin ya bayyana musu abin da aka rufe daga barinsu, daga al´aurarsu, kuma ya ce: "Ubangijinku bai hanã ku daga wannan itãciya ba fãce dõmin kada ku kasance malã´iku biyu ko kuwa ku kasance daga madawwama."
21Kuma ya yi musu rantsuwa; Lalle ne nĩ, a gare ku, haƙĩƙa, daga mãsu nasĩha ne.
22Sai ya saukar da su da rũɗi. Sa´an nan a lõkacin da suka ɗanɗani itãciyar, al´aurarsu ta bayyana gare su, kuma suka shiga sunã lĩƙawar ganye a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ubangjinsu Ya kira su: "Shin, Ban hanã ku ba daga waccan itãciya, kuma Na ce muku lalle ne Shaiɗan, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne?" ,
23Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Mun zãlunci kanmu. Kuma idan ba Ka gãfarta mana ba, kuma Ka yi mana rahama, haƙĩƙa, Munã kasancħwa daga mãsu hasãra."
24Ya ce: "Ku sauka, s?shenku zuwa ga s?she yan? maƙiyi, kuma kun? da matabbata a cikin ƙasa, da ɗan jin d?ɗi zuwa ga wani l?kaci."
25Ya ce: "A cikinta kuke rãyuwa, kuma a cikinta kuke mutuwa, kuma daga gare ta ake fitar da ku."
26Yã ɗiyan Ãdam! Lalle ne Mun saukar da wata tufa(1) a kanku, tanã rufe muku al´aurarku, kuma da ƙawã. Kuma tufar taƙawa wancan ce mafi alhħri. Wancan daga ãyõyin Allah ne, tsammãninsu sunã tunãwa!
27Yã ɗiyan Ãdam! Kada Shaiɗan, lalle, ya fitine ku, kamar yadda ya fitar da iyãyenku, biyu daga Aljanna, yanã fizge tufarsu daga gare su, dõmin ya nũna musu al´aurarsu. Lalle ne shĩ, yanã ganin ku, shi da rundunarsa, daga inda bã ku ganin su. Lalle ne Mũ, Mun sanya Shaiɗan majiɓinci ga waɗanda bã su yin ĩmãni.
28Kuma idan suka aikata alfãsha(2) su ce: "Mun sãmi ubanninmu a kanta." Kuma Allah ne Ya umurce mu da ita."Ka ce: "Lalle ne, Allah bã Ya umurni da alfãsha. Shin kunã faɗar abin da bã ku da saninsa ga Allah?"
29Ka ce: "Ubangjina Yã yi umurni da ãdalci; kuma ku tsayar da fuskõkinku a wurin kõwane masallãci, kuma ku rõƙħ Shi, kunã mãsu tsarkake addini gare Shi. Kamar yadda Ya fãra halittarku kuke kõmãwa."
30Wata ƙungiya (Allah) Yã shiryar, kuma wata ƙungiya ɓata tã wajaba a kansu; lalle ne sũ, sun riƙi shaiɗanu majiɓinta, baicin Allah, kuma sunã zaton, lalle sũ, mãsu shiryuwa ne.
31Yã ɗiyan Ãdam! Ku riƙi ƙawarku a wurin kõwane masallãci kuma ku ci, kuma ku sha; Kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shĩ (Allah), bã Ya son mãsu ɓarna.
32Ka ce: "Wãne ne ya haramta ƙawar Allah, wadda Ya fitar sabõda bãyinSa, da mãsu dãɗi daga abinci?" Ka ce: "Sũ, dõmin waɗanda suka yi ĩmani suke a cikin rãyuwar dũniya, suna keɓantattu a Rãnar Kiyãma. "Kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãnen da suke sani.
33Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwan alf?sha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama´a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah."
34Kuma ga kõwace al´umma akwai ajali. Sa´an nan idan ajalinsu ya je, bã zã a yi musu jinkiri ba, sa´a guda, kuma bã zã su gabãce shi ba.
35Yã ɗiyan Ãdam! Ko dai wasu manzanni, daga cikinku, su jħ muku, sunã gaya muku ay?yiNa - to, wanda ya yi taƙawa, kuma ya gyara aikinsa, to, bãbu tsoro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki.
36Kuma waɗanda suka ƙaryatã game da ãyõyinMu, kuma suka yi girman kai daga gare su, waɗannan sũ ne abõkan wuta, sũ, a cikinta madawwama ne.
37To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata game da ãyõyinSa? Waɗannan rabonsu daga Littãfi yanã sãmunsu, har a lõkacin da ManzanninMu suka je musu, sunã karɓar rãyukansu, su ce: "Ĩnã abin da kuka kasance kunã kira, baicin Allah?" Su ce: "Sun ɓace daga gare mu, "Kuma su yi shaida a kansu cħwa lalle sũ, sun kasance kãfirai."
38Ya ce: "Ku shiga a cikin al´ummai waɗanda, haƙĩƙa, sun shige daga gabãninku, daga aljannu da mutãne, a cikin Wuta. A kõ da yaushe wata al´umma ta shiga sai ta la´ani ´yar´uwarta, har idan suka riski jũna, a cikinta, gabã ɗaya, ta ƙarshensu ta ce wa ta farkonsu: "Ya Ubangijinmu! Waɗannan ne suka ɓatar da mu, sai Ka kãwo musu azãba ninki daga wuta." Ya ce: "Ga kõwane(1) akwai ninki; kuma amma ba ku sani ba."
39Kuma ta farkonsu ta ce wa ta ƙarshe: "To, bã ku da wata falala a kanmu, sai ku ɗanɗana azãba sabõda abin da kuka kasance kunã tsirfawa!"
40Lalle ne waɗanda suka ƙaryatã game da ãyõyinMu, kuma suka yi girman kai daga barinsu, bã zã a bubbuɗe musu kõfõfin sama ba, kuma bã su shiga Aljanna sai raƙumi ya shiga kafar allũra, kuma kamar wannan ne Muke sãka wa mãsu laifi.
41Sunã da wata shimfiɗa daga Jahannama kuma daga samansu akwai wasu murafai. Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa azzãlumai.
42Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, bã Mu ƙallafa wa rai fãce iyãwarsa, Waɗannan ne abõkan Aljanna, sũ, a cikinta, madawwma ne.
43Kuma Muka fitar da abin da yake a cikin ƙirãzansu, daga ƙiyayya, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, kuma suka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah, wanda Ya shiryar da mu ga wannan. Kuma ba mu kasance munã iya shiryuwa ba, bã dõmin Allah Ya shiryar da mu ba. Lalle ne haƙĩƙa, Manzannin Ubangjinmu, sun jħ mana da gaskiya." Kuma aka kira su, cħwa: "Waccan Aljanna an gãdar da ku ita, sabõda abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
44Kuma ´yan Aljanna suka kirãyi ´yan Wuta suka ce: "Lalle ne mun sãmi abin da Ubangijinmu Ya yi mana wa´adi, gaskiya ne. To, shin, kun sãmi abin da Ubangijinku Ya yi muku wa´adi, gaskiya?" Suka ce: "Na´am." Sai mai sanarwa ya yi yħkuwa, cħwa: "La´anar Allah ta tabbata a kan azzãlumai."
45"Waɗanda suke kangħwa daga hanyar Allah, kuma sunã nħman ta ta zama karkatacciya,. kuma sũ, game da Lãhira, kãfirai ne."
46Kuma a tsakãninsu akwai wani shãmaki,(1) kuma a kan A´arãf akwai wasu maza sunã sanin kõwa da alãmarsu; Kuma suka kirãyi abõkan Aljanna cħwa: "Aminci ya tabbata a kanku: "Ba su shige ta ba, alhãli kuwa sũ, sunã tsammãni.
47Kuma idan an jũyar da gannansu wajen abõkan wuta, su ce: "Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanyã mu tãre da mutãne azzãlumai."
48Kuma abõkan A´araf suka kirãyi wasu maza, sunã sanin su da alãmarsu, suka ce: "Tãrawar dũkiyarku da abin da kuka kasance kunã yi na girman kai, bai wadãtar ba daga barinku?"
49"Shin, waɗannan ne waɗanda kuka yi rantsuwa, Allah bã zai sãme su da rahama ba? Ku shiga Aljanna, bãbu tsõro a kanku, kuma ba ku zama kunã baƙin ciki ba."
50Kuma ´yan wuta suka kirãyi ´yan Aljanna cħwa: "Ku zubo a kanmu daga ruwa kõ kuwa daga abin da Allah Ya azurta ku." Su ce: "Lalle ne Allah Ya haramtã su a kan kãfirai."
51"Waɗanda suka riƙi addininsu abin shagala da wãsa, kuma rãyuwar dũniya ta rũɗe su." To, a yau Munã mantãwa da su, kamar yadda suka manta da haɗuwa da yininsu wannan, da kuma abin da suka kasance da ãyoyinMu sunã musu.
52Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun jħ musu da Littãfi, Mun bayyana Shi, daki-daki, a kan ilmi, yanã shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin ĩmani.
53Shin, sunã jira, fãce fassararsa, a rãnar da fassararsa take zuwa, waɗanda suka manta da Shi daga gabãni, sunã cħwa: "Lalle ne, Manzannin Ubangijin mu sun jħ da gaskiya. To, shin, munã da wasu mãsu cħto, su yi cħto gare mu, kõ kuwa a mayar da mũ, har mu aikata wanin wanda muka kasance muna aikatãwa?" Lalle ne sun yi hasãrar rãyukansu, kuma abin da suka kasance sunã ƙĩrƙirawa yã ɓace musu.
54Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini, yanã nħman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana!
55Ku kirãyi Ubangijinku da ƙanƙan da kai, da kuma a ɓõye: lalle ne Shĩ, bã Yã son mãsu wuce iyãka.
56Kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Kuma ku kirãye shi sabõda tsõro da tsammãni; lalle ne rahamar Allah makusanciya ce daga mãsu kyautatãwa.
57Kuma Shĩ ne wanda Yake aika iskõki, sunã bishãra gaba ga rahamarSa, har idan sun ɗauki gizãgizai mãsu nauyi,(1) sai Mu kõra su ga wani gari matacce, sa´an nan Mu saukar da ruwa gare shi, sa´an nan Mu fitar, game da shi, daga dukkan ´ya´yan itace. Kamar wancan ne Muke fitar da matattu; tsammãninku, kunã tunãni.
58Kuma gari mai kyau, tsirinsa yanã fita da iznin Ubangijinsa, kuma wanda ya mũnana, (tsirinsa) bã ya fita, fãce da wahala; kamar wannan ne, Muka sarrafa ãyõyi dõmin mutãne waɗanda suke gõdħwa.
59Lalle ne, haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnħnsa, sai ya ce: "Yã mutãnħna! Ku bauta wa Allah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa. Lalle ne nĩ, inã yi muku tsõron azãbar wani Yini mai girma."
60Mashawarta(1) daga mutãnensa suka ce: "Lalle ne mu, haƙĩƙa, Munã ganin ka a cikin ɓata bayyananniya."
61Ya ce: "Yã mutãnena! Bãbu ɓata guda gare ni, kuma amma nĩ Manzo ne daga ubangijin halittu !"
62"Inã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina; kuma inã yi muku nasĩha, kuma inã sani, daga Allah, abin da ba ku sani ba.
63"Shin, kunã mãmãkin cħwa ambato yã zo muku daga Ubangijinku a kan wani namiji, daga gare ku, dõmin ya yi muku gargaɗi, kuma dõmin ku yi taƙawa, kuma tsammãninku anã jin ƙanku?"
64Sai suka ƙaryata shi, sa´an nan Muka tsĩrar da shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgin; kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata shi game da ãyõyinMu. Lalle ne sũ, sun kasance wasu mutãne ɗĩmautattu.
65Kuma zuwa ga Ãdãwa, ɗan´uwansu Hudu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bautã wa Allah! Bã ku da wani abin bautã wa, waninSa. Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?"
66Mashawarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa suka ce: "Lalle ne mũ, haƙĩƙka, Munã ganin ka a cikin wata wauta! Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, Munã zaton ka daga maƙaryata."
67Ya ce: "Yã mutãnena! Bãbu wata wauta a gare ni, kuma amma nĩ, Manzo ne daga Ubangijin halittu!"
68Inã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina, kuma nĩ, gare ku, mai nasĩha ne amintacce.
69"Shin, kuma kun yi mãmãki cħwa ambato daga Ubangijinku ya zo muku a kan wani namiji daga gare ku, dõmin ya yi muku gargaɗi? Kuma ku tunã a lõkacin da Ya sanyã ku mãsu mayħwa daga bãyan mutãnen Nũhu, kuma Ya ƙãra muku zãti a cikin halitta. Sabõda haka ku tuna ni´imõmin Allah; tsammãninku kunã cin nasara."
70Suka ce: "Shin, kã zo mana ne dõmin mu bauta wa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance sunã bauta wa? To, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi da shi idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
71Ya ce: "Haƙĩƙa azãba da fushi sun auku a kanku daga Ubangijinku! Shin, kunã jãyayya da ni a cikin wasu sunãye waɗanda kũ ne kuka yi musu sunãyen, kũ da ubanninku, Allah bai saukar da wani dalili ba a gare su? To, ku yi jira. Lalle ne ni, tãre da ku mai jira ne."
72To, sai Muka tsĩrar da shi, shĩ da waɗanda suke tãre da shi sabõda wata rahama daga gare Mu, kuma Muka katse ƙarshen waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma ba su kasance mũminai ba.
73Kuma zuwa ga Samũdãwa ɗan´uwansu, Sãlihu, ya ce: "Yã mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa wanninSa. Haƙĩƙa hujja bayyananniya tã zo muku daga Ubangijinku! wannan rãƙumar Allah ce, a gare ku, wata ãyã ce. Sai ku bar ta ta ci, a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shãfe ta da wata cũta har azãba mai raɗaɗi ta kãmã ku."
74"Kuma ku tuna a lõkacin da Ya sanyã ku mamaya daga bãyan Ãdãwa kuma Ya zaunar da ku a cikin ƙasa, kunã riƙon manyan gidãje daga tuddanta, kuma kunã sassaƙar ɗãkuna daga duwãtsu; sabõda haka ku tuna ni´imõmin Allah, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa kuna mãsu fasãdi."(1)
75Mashawarta waɗanda suka yi girman kai daga mutanensa suka ce ga waɗanda aka raunanar,(2) ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare su: "Shin, kunã sanin cħwa Sãlihu manzo ne daga Ubangijinsa?" Suka ce: "Lalle ne mũ, da abin da aka aiko shi, mãsu ĩmãni ne."
76Waɗanda suka yi girman kai suka ce: "Lalle ne mu, ga abin da kuka yi ĩmãni da shi kãfirai ne."
77Sai suka sõke rãƙumar, kuma suka kangare daga barin umurnin Ubangijinsu, kuma suka ce: "Yã Sãlihu! Ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi da shi, idan kã kasance daga manzanni !"
78Sai tsãwa ta kãmã su, sabõda haka suka wãyi gari a cikin gidansu guggurfãne!
79Sai ya jũya daga barinsu, kuma ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne, haƙĩƙa, nã iyar muku da manzancin Ubangijina. Kuma nã yi muku nasĩha kuma amma bã ku son mãsu nasĩha!"
80Da Lũɗu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa: "Shin, kunã jħ wa alfãsha, bãbu kõwa da ya gabãce ku da ita daga halittu?"
81"Lalle ne ku, haƙĩƙa kunã jħ wa maza da sha´awa, baicin mata; ôa, kũ mutãne ne maɓarnata."
82Kuma bãbu abin da ya kasance jawãbin mutãnensa, fãce ɗai suka ce: "Ku fitar da su daga alƙaryarku: lalle ne sũ, wasu mutãne ne mãsu da´awar tsarki!"
83Sai Muka tsĩrar da shi, shĩ da iyãlansa, fãce matarsa, ta kasance daga mãsu wanzuwa.
84Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa; Sai ka dũba yadda ãƙibar mãsu laifi ta kasance!
85Kuma zuwa Madayana ɗan´uwansu Shu´aibu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku tã zõ muku! Sai ku cika mũdu da sikeli kuma kada ku nakasa wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Wannan ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance mũminai."
86"Kuma kada ku zauna ga kõwane tafarki kunã ƙyacħwa, kuma kunã kangħwa, daga hanyar Allah, ga wanda ya yi ĩmãni da shi, kuma kunã nħman ta ta zama karkatacciya, kuma ku tuna, a lõkacin da kuka kasance kaɗan, sai Ya yawaita ku, kuma ku dũba yadda ãƙibar mãsu fasãdi ta kasance:"
87"Kuma idan wata ƙungiya daga gare ku ta kasance ta yi ĩmãni da abin da aka aiko ni da shi, kuma wata ƙungiya ba ta yi ĩmãni ba, to, ku yi haƙuri, har Allah Ya yi hukunci a tsakãninmu; kuma Shi ne Mafi alhħrin mãsu hukunci."
88Mashawarta waɗanda suka kangare daga mutãnensa, suka ce: "Lalle ne, Munã fitar da kai, Yã Shu´aibu, kai da waɗanda suka yi Ĩmãni tãre da kai, daga alƙaryarmu; kõ kuwa lalle ku kõmo a cikin addininmu." Ya ce: "Ashe! Kuma kõ dã mun kasance mãsu ƙĩ?"
89"Lalle ne mun ƙirƙira ƙarya ga Allah idan mun kõma a cikin addininku a bãyan lõkacin da Allah ya tsĩrar da mu daga gare shi, kuma bã ya kasancewa a gare mu, mu kõma a cikinsa, fãce idan Al1ah, Ubangijinmu Ya so. Ubangijinmu Yã yalwaci dukan kõme ga ilmi. Ga Allah muka dõgara. Yã Ubangijinmu! Ka yi hukunci a tsakãninmu da tsakanin mutãnenmu da gaskiya, kuma Kai ne Mafi alhħrin mãsu hukunci."
90Kuma mashawarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa, suka ce: "Lalle ne, idan kun bi Shu´aibu haƙĩƙa kũ, a lõkacin nan, mãsu hasãra ne."
91Sai tsãwa ta kãma su, sabõda haka suka wãyi gari, a cikin gidansu, sunã guggurfãne.
92Waɗanda suka ƙaryata Shu´aibu kamar ba su zauna ba a cikinta, waɗanda suka ƙaryata Shu´aibu, sun kasance sũ ne mãsu hasãra!
93Sai ya jũya daga barinsu, kuma ya ce: "Yã mutãnena! Haƙĩƙa, nã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina, kuma nã yi muku nasĩha! To, yãya zan yi baƙin ciki a kan mutãne kãfirai?"
94Kuma ba Mu aika wani Annabi(1) a cikin wata alƙarya ba, fãce Mun kãma mutãnenta da azãba da cũta, tsammãninsu sunã yin ƙasƙantar da kai.
95Sa´an nan kuma Muka musanya mai kyau a matsayin mummũna, har su yi yawa, kuma su ce: "Cũta da azãba sun shãfi ubanninmu." ( Sai su kõma wa kãfirci). Sai Mu kãmã su kwatsam! alhãli kuwa sũ, bã su sansancħwa."
96Kuma dã lalle mutãnen alƙaryu sun yi ĩmãni kuma suka yi taƙawa dã haƙĩƙa Mun bũɗe albarkõki a kansu daga sama da ƙasa, kuma amma sun ƙaryata, don haka Muka kãma su da abin da suka kasance sunã tãrãwa.
97Shin, mutãnen alƙaryu sun amince wa azãbar Mu ta jħ musu da dare, alhãli kuwa sunã barci?
98Kõ kuwa mutãnen alƙaryu sun amince wa azãbarMu ta jħ musu da hantsi, alhãli kuwa sunã wãsa?
99Shin fa, sun amince wa makarun Allah? To, bãbu mai amince wa makarun Allah fãce mutãne mãsu hasãra!
100Shin, kuma bai shiryar da waɗanda suke gãdon ƙasa ba daga bãyan mutãnenta cħwa da Munã so, dã Mun sãme su da zunubansu, kuma Mu rufe a kan zukãtansu, sai su zama bã su ji?
101Waɗancan alƙaryu Munã gaya maka daga lãbãransu, kuma lalle ne, haƙĩƙa manzanninMu sun jħ musu da hujjõji bayyanannnu; to, ba su kasance sunã yin ĩmãni da abin da suka ƙaryata daga gabãni ba. Kamar wancan ne Allah Yake rufħwa a kan zukãtan kãfirai.
102Kuma ba Mu sãmi wani alkawari ba ga mafi yawansu, kuma lalle ne, Mun sãmi mafi yawansu, haƙĩƙa, fãsiƙai.
103Sa´an nan kuma Mun aika Musa,(1) daga bãyansu, da ãyõyinMu zuwa ga Fir´auna da majalisarsa, sai suka yi zãlunci game da su. To, dũbi yadda ãƙibar maɓarnata take.
104Kuma Musa ya ce: "Ya Fir´auna! Lalle ne nĩ, manzo ne daga Ubangijin halittu."
105"Tabbatacce ne a kan kada in faɗi kõme ga Allah fãce gaskiya. Lalle ne, nã zo muku da hujja bayyananniya daga Ubangijinku; Sai ka saki Banĩ Isrã´ila tãre da ni."
106Ya ce: "Idan kã kasance kã zo da wata ãyã, to, ka kãwõ ta, idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
107Sai ya jħfa sandarsa, sai gã ta kumurci bayyananne!
108Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu dũbi!
109Mashãwarta daga mutãnen Fir´auna suka ce: "Lalle ne, wannan, haƙĩƙa, matsafi ne mai ilmi."
110" Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku: To, mħne ne kuke shawartawa?"
111Suka ce: "Ka jinkirtar da shĩ, shĩ da ɗan´uwansa, kuma ka aika da mãsu gayyar mutãne a cikin garũruwa.
112"Su zõ maka da duka matsafi, mai ilmi."
113Kuma matsafa suka jħ wa fir´aunã suka ce: "Lalle ne, shin, Munã da ijãra, idan mun kasance mũ ne marinjaya?"
114Ya ce: "Na´am kuma lalle ne kunã a cikin makusanta."
115Suka ce: "Ya Mũsã! Kõ dai ka jħfa, kõ kuwa mu kasance, mũ ne, mãsu jħfãwa?"
116Ya ce: "Ku jħfa." To a 1õkacin da suka jħfa, suka sihirce idãnun mutãne kuma suka tsõratar da su; Kuma suka jħ da tsafi mai girma."
117Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cħwa: "Ka jħfa sandarka." Sai gã ta tanã lãƙumar abin da suke ƙarya da shi!
118Gaskiya ta auku, kuma abin da suke aikatãwa ya ɓãci.
119Sai aka rinjãye su a can, kuma suka jũya sunã ƙasƙantattu.
120Kuma aka jħfar da matsafan, sunã mãsu sujada.
121Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halittu."
122"Ubangijin Mũsã da Harũna."
123Fir´auna ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni da shi a gabãnin inyi izni a gare ku? Lalle ne, wannan, haƙĩƙa, mãkirci ne kuka mãkirta a cikin birni, dõmin ku fitar da mutãnensa daga gare shi; To, da sannu zã ku sani."
124"Lalle ne, inã karkãtse hannãyenku da ƙafãfunku daga sãɓãni, sa´an nan kuma, haƙĩƙa, inã tsĩre, ku gabã ɗaya."
125Suka ce: "Lalle ne mu, zuwa ga Ubangijinmu, mãsu jũyãwa ne."
126"Kuma bã ka zargin kõme daga gare mu fãce dõmin mun yi ĩmãni da ãyõyin Ubangijinmu a lõkacin da suka zõ mana! Ya Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu, kuma Ka cika mana munã Musulmai!(1) "
127Kuma mashawarta daga mutãnen Fir´auna suka ce: "Shin, zã ka bar Mũsã da mutãnensa dõmin su yi ɓarna a cikin ƙasa, kuma ya bar ka, kai da gumãkanka?" Ya ce: "Zã mu yayyanka ɗiyansu maza kuma mu rãya mãtansu; kuma lalle ne mũ, a bisa gare su, marinjãya ne."
128Mũsã ya ce wa mutãnensa:(2) "Ku nħmi taimako da Allah, kuma ku yi haƙuri; Lalle ne ƙasa ta Allah ce, Yãna gãdar da ita ga wanda Yake so daga bãyinSa, kuma ãƙiba ta mãsu taƙawa ce."
129Suka ce: "An cũtar da mu daga gabãnin ka zõ mana, kuma daga bãyan da kã zõ mana." Ya ce: "Akwai tsammãnin Ubangijinku, Ya halaka maƙiyanku, kuma Ya sanya ku, ku maye a cikin ƙasa, sa´an nan Ya dũba yadda kuke aikatãwa."
130Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun kãma mutãnen Fir´auna da tsananin shħkaru (fari) da nakasa daga ´ya´yan itãce; tsammãninsu sunã tunãwa.
131Sa´an nan idan wani alhħri ya jħ musu, sai su ce: "Wannan nãmu ne," kuma idan masĩfa ta sãme su, sai su yi shu´umci da Mũsã da wanda yake tãre da shi. To, shu´umcinsu a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawansu bã su sani!"
132Kuma suka ce: "Kõ me ka zõ mana da shi daga ãyã, dõmin ka sihirce mu da ita, to, baza mu zama, sabõda kai, mãsu ĩmãni ba."
133Sai Muka aika a kansu da cikõwa, da fãra, da ƙwarƙwata da kwãɗi, da jini; ãyõyi abũbuwan rarrabħwa;(1) Sai suka kangare, kuma suka kasance mutãne mãsu laifi.
134Kuma a lõkacin da masĩfa ta auku a kansu, sukan ce: "Yã Mũsã! Ka rõƙa mana Ubangijinka, sabõda abin da Ya yi alkwari a wurinka, lalle ne idan ka kau da azãbar daga barinmu, haƙĩƙa Munã ĩmãni sabõda kai, kuma munã sakin Banĩ Isrã´ila tare da kai."
135To, a lõkacin da Muka kuranye azãba daga barinsu zuwa a wani ajali wanda suke mãsu iske shi ne, sai gã su sunã warwarħwa!
136Sai Muka yi azãbar rãmuwa, daga gare su, sabõda haka Muka nutsar da su a cikin tħku, dõmin lalle ne sũ, sun ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma sun kasance daga barinsu, gãfilai.
137Kuma Muka gãdar da mutãnen, waɗanda sun kasance anã raunana su, a gabacin ƙasa da yammacinta, wadda Muka sanya albarka a cikinta, kuma kalmar Ubangijinka mai kyau ta cika a kan Banĩ Isrã´ĩla, sabõda abin da suka yi na haƙuri. Kuma Muka murtsuke abin da Fir´auna da mutãnensa suka kasance sunã sanã´antawa, da abin da suka kasance sunã shimfiɗãwa.(2)
138Kuma Muka ƙħtarar da Banĩ Isra´ila ga tħku, sai suka jħ a kan wasu mutãne waɗanda sunã lizimta da ibãda a kan wasu gumãka, nãsu suka ce: "Yã Mũsã! Ka sanya mana wani abin bautawa kamar yadda suke da abũbuwan bautãwa "(1) Ya ce: "Lalle ne kũ, mutãne ne kunã jahilta."
139"Lalle ne waɗannan, abin da suke a cikinsa halakakke ne, kuma abin da suka kasance sunã aikãtawa ƙarya ne."
140Ya ce: "Shin, wanin Allah nike nħma muku ya zama abin bautãwa, alhãli kuwa Shĩ (Allah) Ya fĩfĩta ku a kan halittu?"
141Kuma a lõkacin da Muka tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, sunã tayã muku mugunyar azãba. sunã karkashe ɗiyanku maza, kuma sunã rãyar da matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabãwa daga Ubangijinku,(2) Mai girma.
142Kuma Muka yi wa´adi ga Mũsã da dare talãtin(3) kuma Muka cikã su da gõma, sai miƙatin Ubangijinsa ya cika dare arba´in. Kuma Mũsã ya ce wa ɗan´uwansa, Hãrũna: "Ka maye mini a cikin mutãnena, kuma ka gyãra, kuma kada ka bi hanyar mãsu fasãdi."
143Kuma a lõkacin da Mũsã ya jħ ga mĩkatinMu, kuma Ubangijinsa Ya yi masa magana, shi Mũsã ya ce: "Yã Ubangijina! Ka nũna mini in yi dũbi zuwa gare Ka!" Ya ce: "Bã zã ka gan Ni ba, kuma amma ka dũba zuwa ga dũtse, to, idan ya tabbata a wurinsa, to, zã ka gan Ni." Sa´an nan a lõkacin da Ubangijinsa, Ya kuranye zuwa ga dũtsen, Ya sanyã shi niƙaƙƙe. Kuma Mũsã ya fãɗi sõmamme. To, a lõkacin da ya farka, ya ce: "TsarkinKa ya tabbata! Nã tũba zuwa gare Ka, kuma ni ne farkon mũminai."
144Ya ce: "Ya Mũsã! Lalle ne Nĩ, Nã zãɓe ka bisa ga mutãne da manzanciNa, kuma da maganãTa. Sabõda haka ka riƙi abin da Nã bã ka, kuma ka kasance daga mãsu gõdiya."
145Kuma Muka rubũta masa a cikin alluna daga kõwane abu, wa´azi da rarrabħwa ga dukan kõwane abu: "Sai ka riƙe su da ƙarfi, kuma ka umurci mutãnenka, su yi riƙo ga abin da yake mafi kyawunsu;(1) zã Ni nũna muku gidan fãsiƙai."
146Zã Ni karkatar da waɗanda suke yin girman kai a cikin ƙasa, bã da wani hakki ba, daga ãyõyiNa. Kuma idan sun ga dukan ãyã, bã zã su yi ĩmãni da ita ba, kuma idan sun ga hanyar shiriya, bã zã su riƙe ta hanya ba, kuma idan sun ga hanyar ɓata, sai su riƙe ta hanya. Wancan ne, dõmin lalle ne su, sun ƙaryata da ãyõyinMu, kuma sun kasance, daga barinsu gãfilai.
147Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu da gamuwa da Lãhira, ayyukansu sun ɓãci. Shin, ana saka musu, fãce da abin da suka kasance suna aikatãwa?
148Kuma mutãnen Mũsã suka riƙi maraƙi,(2) jikin mutãne, yanã rũri, daga bãyan tafiyarsa, daga kãyan ƙawarsu. Shin, ba su ganĩ ba, cħwa lalle ne shi, bã ya yi musu magana, kuma bã ya shiryar da su ga hanya, sun riƙa shi, kuma sun kasance mãsu zãlunci.
149Kuma a lõkacin da suka yi nadãma, kuma suka ga cħwa lalle ne sũ haƙĩƙa sun ɓace, suka ce: "Haƙĩƙa, idan UbangijinMu bai yi mana rahama ba, kuma Ya gãfarta mana, lalle ne munã kasancħwa daga mãsu hasãra."
150Kuma a lõkacin da Mũsã ya kõma zuwa ga mutãnensa, yanã mai fushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Tir da abin da kuka yi mini wakilci, a bãyanã! Shin, kun nħmi gaggawar umurnin Ubangijinku ne?" Kuma ya jefar da Allunan, kuma ya yi riƙo ga kan ɗan´uwansa yana jan sa zuwa gare shi. Ya ce: "Yã ɗan´uwata! Lalle ne mutãnen, sun ɗauke ni mai rauni, kuma sun yi kusa su kashe ni, sabõda haka kada ka dãrantar da maƙiya game da ni, kuma kada ka sanya ni tãre da mutãne azzãlumai."
151Ya ce: "Yã Ubangijina! Ka gãfarta mini, nĩ da ɗan´uwana, kuma Ka shigar da mu a cikin rahamarKa, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama!"
152Lalle ne waɗanda suka riƙi maraƙin, wani fushi daga Ubangijinsu da wani walãkanci a cikin rãyuwar dũniya, zã su sãme su: Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu ƙirƙira ƙarya.
153Kuma waɗanda suka aikata miyãgun ayyuka, sa´an nan suka tũba daga bãyansu kuma suka yi ĩmãni, lalle ne Ubangijinka daga bãyansu, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
154Kuma a lõkacin da fushin ya kwanta daga barin Mũsã, sai ya riƙi Allunan, kuma a cikin kwafensu akwai shiriya da rahama ga waɗanda suke sũ, ga Ubangijinsu, mãsu jin tsõro ne.
155Kuma Mũsã ya zãɓi mutãnensa, namiji saba´in dõmin miƙãtinMu. To, a lõkacin da tsãwa ta kãma su, ya ce: "Yã Ubangijina! Dã Kã so, dã Kã halakar da su daga gabãni, sũ da ni. Shin zã Kahalaka mu, sabõda abin da wãwãyen daga gare mu suka aikata? Ba ta zama ba fãce fitinarKa Kanã ɓatarwa, da ita, wanda Kake so kuma kanã shiryarwa da ita, wanda Kake so; Kai ne Majiɓincinmu. Sai Ka gãfarta mana; kuma Ka yi mana rahama, alhãli kuwa Kai ne Mafi alhħrin mãsu gãfara."
156"Kuma Ka rubũta mana alhħri a cikin wannan dũniya, kuma a cikin Lãhira. Lalle ne mũ, mun tũba zuwa gare Ka." Ya ce: "AzãbaTa Inã sãmu, da ita, wanda Nike so, kuma rahamaTa, ta yalwaci dukan kõme. Sa´an nan zã Ni rubũta ta ga waɗanda suke yin taƙawa, kuma sunã bãyar da zakka, da waɗanda suke, game da ãyõyinMu mũminai ne."
157"Waɗanda suke sunã bin Manzo,(1) Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla. yanã umurnin su da alhħri kuma yana hana su daga barin abin da bã a so; kuma yanã halatta musu abũbuwa mãsu daɗi, kuma yana haramtarwar mũnana a kansu. Kuma yanã kãyar da nauyinsu daga barinsu, da ƙuƙummai waɗannan da suka kasance a kansu. To, waɗanda suka yi ĩmãni da shi kuma suka ƙarfafa shi, kuma suka taimake shi, kuma suka bi haske wanda aka saukar tãre da shi, waɗannan ne mãsu cin nasara."
158Ka ce: "Yã kũ mutãne!(2) Lalle ne nĩ manzon Allah ne zuwa gare ku, gabã ɗaya. (Allah) Wanda Yake Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa; Bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Yanã rãyarwa, kuma Yanã matarwa, sai ku yi ĩmãni da Allah da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi, wanda yake yin ĩmãni da Allah da kalmominSa; ku bĩ shi, tsammãninku, kunã shiryuwa."
159Kuma daga mutãnen(3) Mũsã akwai al´umma, sunã shiryarwa da gaskiya, kuma da ita suke yin ãdalci.
160Kuma Muka yayyanka su sibɗi gõma shã biyu, al´ummai. Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã a lõkacin da mutãnensa suka nħme shi, ga shãyarwa, cħwa: "Ka dõki dũtsen(1) da sandarka."Sai marmaro gõma shã biyu suka ɓuɓɓuga daga gare shi: Lalle ne kõwaɗanne mutãne sun san mashãyarsu. Kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kansu."Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku." Kuma ba su zãluncħ Mu ba; kuma amma rãyukansu suke zãlunta.
161Kuma a lõkacin da aka ce masu: "Ku zauna ga wannan alƙarya,(2) kuma ku ci daga gare ta, inda kuka so, kuma ku ce: ´Saryarwa,´ kuma ku shiga kõfa kuna mãsu sujada; Mu gãfarta muku laifuffukanku, kuma zã Mu ɗãra wa mãsu kyautatãwa."
162Sai waɗanda suka yi zãlunci daga gare su, suka musanya magana(3) watar wadda aka ce musu, sai Muka aika azãba a kansu, daga sama, sabõda abin da suka kasance sunã yi na zãlunci.
163Kuma ka tambaye su daga alƙarya wadda ta kasance kusa ga tħku, a lõkacin da suke ƙħtare haddi a cikin Asabar, a lõkacin da kĩfãyensu, suke je musu a rãnar Asabar(4) ɗinsu jħre. Kuma a rãnar da ba su yi Asabar ba, bã su zuwa gare su; Kamar wancan ne Muke jarraba su da abin da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci.
164Kuma a lõkacin da wata al´umma daga gare su ta ce: "Don me kuke yin wa´azi ga mutãne waɗanda Allah Yake Mai halaka su kõ kuwa Mai yi musu azãba, azãba mai tsanani?" Suka ce: "Dõmin nħman hanzari zuwa ga Ubangijinku, kuma tsammãninsu, sunã yin taƙawa."
165To, a lõkacin da suka manta da abin da aka tunãtar da su da shi, Mun tsĩrar da waɗanda suke hani daga cũta, kuma Muka kãma waɗanda suka yi zãlunci, da azãba mai tsanani dõmin abin da suka kasance sunã yi, na fasiƙanci.
166Sa´an nan a lõkacin da suka yi girman kai daga barin abin da aka hana su daga gare shi, Muka ce musu: "Ku kasance birai ƙasƙantattu."
167Kuma a lõkacin da Ubangijinku Ya sanar, lalle ne, zã Ya aika a kansu (Yahũd), zuwa, Rãnar Ƙiyãma, wanda zai ɗanɗana musu mummunar azãba, lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Mai gaggawar uƙũba ne, kuma shĩ haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
168Kuma Muka yayyanka su, a cikin ƙasa, al´ummõmi, daga gare su akwai sãlihai, kuma daga gare su akwai wanda bã haka ba. Muka jarrabe su da abũbuwan alhħri da na musĩfa; Tsammãninsu, sunã kõmõwa.
169Sai wasu´ yan bãya suka maye daga bãyansu, sun gaji Littãfin, sunã karɓar sifar(1) wannan ƙasƙantacciya, sunã cħwa: "Zã a gãfarta mana. "Idan kuma wata sifa irinta ta zo, za su karɓe ta. Shin, ba a karɓi alkawarin Littãfi ba a kansu cħwa kada su faɗa ga Allah, fãce gaskiya, alhãli kuwa sun karanta abin da yake a cikinsa, kuma Gidan Lãhira ne mafi alh ħri ga wanda ya yi taƙawa? Shin, bã zã ku hankalta ba?
170Kuma waɗanda suke riƙħwa da littãfi kuma suka tsayar da salla, lalle ne Mũ, bã Mu tõzarta lãdar mãsu gyãrãwa.
171Kuma a lõkacin da muka ɗaukaka dũtse(1) sama da su, kamar dai shi girgije ne, kuma suka haƙƙaƙe, lalle ne shĩ, mai fãɗuwa ne a gare su, (aka ce): "Ku karɓi abin da Muka kãwo muku da ƙarfi, kuma ku tuna abin da yake a cikinsa, tsammãninku kunã yin taƙawa."
172Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya karɓi (alkawari) daga ɗiyan Ãdam, daga bãyayyakinsu, a zuriyarsu, kuma Ya shaidar da su a kan rãyukansu, (Ya ce): "Shin, bã Nĩ ne Ubangijinku ba?" Suka ce: "Na´am! Mun yi shaida!" (ya ce): "Kada ku ce a Rãnar Kiyãma: Lalle ne mũ, daga wannan, gafalallu ne."(2)
173Kõ kuwa ku ce: "Abin sani kawai, ubanninmu suka yi shirki daga farko, kuma mũ, mun kasance zũriya daga bãyansu. Shin fa, Kanã halaka mu, sabõda abin da mãsu ɓãtãwa suka aikata?"
174Kuma kamar haka Muke rarrabe ãyõyi, daki-daki; tsammãninsu, sunã kõmõwa.
175Ka karanta a kansu lãbãrin wanda Muka kãwo masa(3) ãyõyinMu, sai ya sãɓule daga gare su, sai shaidan ya bi shi, sai ya kasance a cikin halakakku.
176Kuma dã Mun so, da Mun ɗaukakã shi da su, kuma amma shĩ, ya nħmi dawwama a cikin ƙasa, kuma ya bi son zũciyarsa. To, misãlinsa kamar misãlin kare ne, idan ka yi ɗauki a kansa ya yi lallage, kõ kuwa ka bar shi sai ya yi lallage, wannan ne misãlin mutãne waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu: Ka jħranta karãtun lãbãrun; tsammãninsu sunã tunãni.
177Tir da zama misãli, mutãnen da suka ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma kansu suka kasance sunã zãlunta.
178Wanda(4) Allah Ya shiryar, to, shĩ ne Mai shiryuwa, kuma wanda Ya ɓatar, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
179Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sabõda Jahannama, mãsu yawa daga aljannu da mutãne, sunã da zukãta, ba su fahimta da su, kuma sunã da idãnu, bã su gani da su, kuma sunã da kunnuwa, ba su ji da su; waɗancan kamar bisãshe suke. ôa, sũ ne mafi ɓacħwa; Waɗancan sũ ne gafalallu.
180Kuma Allah Yanã da sũnãye mãsu kyau.(1) Sai ku rõƙe shi da su, kuma ku bar waɗanda suke yin ilhãdi a cikin sũnãyenSa: zã a sãka musu abin da suka kasance sunã aikatãwa.
181Kuma daga waɗanda Muka halitta akwai wata al´umma, sunã shiryarwa da gaskiya, kuma, da ita suke yin ãdalci.
182Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
183Kuma Inã yi musu jinkiri, lalle ne kaidĩNa, mai ƙarfi ne.
184Shin, ba su yi Tunani ba, cħwa bãbu wata hauka ga ma´abucinsu? (2) shĩ bai zama ba fãce mai gargaɗi mai bayyanãwa.
185Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?
186Wanda Allah Ya ɓatar to bãbu mai shiryarwa a gare shi: kuma Yanã barin su, a cikin ɓatarsu sunã ɗimuwa.
187Sunã tambayar ka(3) daga Sa´a, a yaushe tabbatarta take? Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Ubangijina yake. Bãbu mai bayyana ta ga lõkacinta fãce shĩ. Tã yi nauyi a cikin sammai da ƙasa. Bã zã ta zo muku ba fãce kwatsam." Sunã tambayar ka, kamar kai masani ne gare ta. Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawan mutãne bã su sani."
188Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãce abin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhħri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba face mai gargaɗi, kuma mai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni."
189Shĩ ne wanda Ya halitta ku daga rai guda, kumaYa sanya, daga gare ta, ma´auranta, dõmin ya natsu zuwa gare(1) ta. Sa´an nan a lõkacin da ya rufe ta, ta yi ciki, ciki sassauƙa, sai ta shũɗe dashi. Sa´an nan a lõkacin da ya yi nauyi, sai suka rõƙi Allah, Ubangijinsu: "Lalle ne idan Ka bã mu abin ƙwarai, haƙĩƙa, zã mu kasance daga mãsu gõdiya."
190To, a lõkacin da Ya bã su abin ƙwarai, suka sanya Masa abõkan tarayya a cikin abin da Ya ba su. To, Allah Yã tsarkaka daga abin da suke yi na shirki.
191Shin, sunã shirki da abin da bã ya halittar kõme, kuma sũne ake halittãwa?
192Kuma ba su iya bãyar da taimako gare su, kuma kansu ma, bã su iya taimaka!
193Kuma idan kun kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su bĩ ku ba, daidai ne a gare ku, shin, kun kirãye su, kõ kuwa kũ mãsu kawaici ne!
194Lalle ne waɗannan da kuke kira, baicin Allah, bãyĩ ne misãlanku: to, ku kirãye su, sa´an nan su karɓa muku, idan kun kasance mãsu gaskiya!
195Shin sunã da ƙafãfu da suke yin tafiya da su? Kõ sunã da hannãye da suke damƙa da su? Kõ sunã da idãnu da suke gani da su? Ko sunã da kunnuwa da suke saurãre da su? Ka ce: "Ku kirãwo abũbuwan(2) shirkinku sa´an nan kuma ku yi mini kaidi, sa´an nan kada ku saurãra mini."
196"Lalle ne, Majiɓincĩna Allah ne Wanda Ya saukar da Littãfi kuma Shĩ ne Yake jiɓintar sãlihai,"
197"Kuma waɗanda kuke kira, baicinSa, bã su iya taimakõn ku, kuma kansu ma, bã su iya taimaka."
198Kuma idan ka kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su ji ba, kuma kanã ganin su, sunã dũbi zuwa gare ka, alhãli kuwa sũ, bã su gani.
199Ka riƙi abin da ya sauƙaƙa; Kuma ka yi umurni da alhħri, Kuma ka kau da kai daga jãhilai.(1)
200Kuma imma wata fizga daga Shaiɗan ta fizge ka, sai ka nħmi tsari ga Allah. Lalle ne shi, Mai jĩ ne, Masani.
201Lalle ne waɗanda suka yi taƙawa idan wani tãshin hankali daga Shaiɗan ya shãfe su, sai su tuna (Allah) sai gã su, sun zama masu basĩra.
202Kuma ´yan´uwan su (shaiɗanu) sunã taimakon su a cikin ɓata, sa´an nan kuma bã su taƙaitãwa.
203Kuma idan ba ka je musu da wata ãyã ba, su ce: "Don me ba ka ƙãga ta ba?" Ka ce: "Abin sani kawai, inã biyar abin da aka yõ wahayi zuwa gare ni ne, daga Ubangjina. Wannan abũbuwan kula ne daga Ubangijinku, da shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin imãni."
204Kuma idan an karanta(2) Alƙur´ãni sai ku saurara gare shi, kuma ku yi shiru; Tsammãninku, anã yi muku rahama.
205Kuma ka ambaci(3) Ubangijinka, a cikin ranka da ƙanƙan da kai, da tsõro, kuma kõma bãyan bayyanawa na magana, da sãfe da marece, kuma kada ka kasance daga gafalallu.
206Lalle ne, waɗanda ke wurin Ubangijinka bã su yin girman kai ga bauta Masa, kuma sunã tsarake shi da tasbĩhi, kuma a gare shi suke yin sujada.
Chapter 8 (Sura 8)
1Suna tambayar ka(1) ga ganĩma. ka ce: "Ganĩma ta Allah da ManzonSa ce. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku gyãra abin da yake a tsakãninku, kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, idan kun kasance mũminai."
2Abin sani kawai, mũminai sũ ne waɗanda suke idan an ambaci Allah, zukãtansu su firgita, kuma idan an karanta ãyõyinSa a kansu, su ƙãrã musu wani ĩmãni, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara.
3Waɗanda suke tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azũrtã su sunã ciyarwa.(2)
4Waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya. Sunã da darajõji a wurin Ubangijinsu, da wata gãfara da arziki na karimci.
5Kamar yadda Ubangijinka Ya fitar da kai daga gidanka da gaskiya, alhãli kuwa lalle wani ɓangare na mũminai, haƙĩƙa, sunã ƙyãma.
6Sunã jãyayya da kai a cikin (sha´anin) gaskiya a bãyan tã bayyanã, kamar dai lalle anã kõra su zuwa ga mutuwa ne alhãli kuwa sunã kallo.
7Kuma a lõkacin(3) da Allah Yake yi muku alkawari da ɗayan ƙungiya biyu, cħwa lalle ita tãku ce: kuma kunã gũrin cħwa lalle ƙungiya wadda bã ta da ƙaya ta kasance gare ku, kuma Allah Yanã nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmõminSa, kuma Ya kãtse ƙarshen kãfirai;
8Dõmin Ya tabbatar da gaskiya, kuma Ya ɓãta ƙarya, kuma kõdã mãsu laifi sun ƙi.
9A lõkacin da kuke nħman Ubangijinku taimako, sai Ya karɓa muku cħwa: "Lalle ne Nĩ, Mai taimakon ku ne da dubu daga malã´iku, jħre."
10Kuma Allah bai sanya shi ba fãce Dõmin bishãra, kuma dõmin zukãtanku su natsu da shi, kuma taimakon, bai zama ba fãce daga wurin Allah; Lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
11A lõkacin da (Allah) Yake rufe ku da gyangyaɗi, ɗõmin aminci daga gare Shi, kuma Yanã saukar da ruwa(1) daga sama, a kanku, dõmin Ya tsarkake ku da shi, kuma Ya tafiyar da ƙazantar Shaiɗan daga barinku, kuma dõmin Ya ɗaure a kan zukãtanku, kuma Ya tabbatar da ƙafãfu da shi.
12A lõkacin da Ubangijinka Yake yin wahayi zuwa ga Malã´iku cħwa: "Lalle ne Ni, Inã tãre da ku, sai ku tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni: Zã Ni jħfa tsõro a cikin zukãtan waɗanda suka kãfirta, sai ku yi dũka bisa ga wuyõyi kuma ku yi dũka daga gare su ga dukkan yãtsu(2) .
13Wancan ne, dõmin lalle ne sũ, sunã sãɓa wa Allah da ManzonSa. Kuma wanda ya sãɓa wa Allah da ManzonSa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
14Wancan ne: "Ku ɗanɗane shi, kuma lalle ne akwai azãbar wuta ga kãfirai."
15Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun haɗu da waɗanda suka kãfirta ga yãƙi, to, kada ku jũya musu bãyayyakinku.
16Kuma duka wanda(3) ya jũya musu bãyansa a yinin nan, fãce wanda ya karkata dõmin kõɗayya, kõ kuwa wanda ya jħ dõmin haɗuwa da wata ƙungiya, to, lalle ne ya kõma da fushi daga Allah, kuma matattararsa Jahannama, kuma tir da makõma ita!
17To, bã kũ ne kuka kashe su ba; kuma amma Allah ne Ya kashe su: kuma ba ka yi jĩfa ba a lõkacin da ka yi jĩfa; kuma amma Allah ne Ya yi jĩfar.(1) Kuma dõminYa jarraba Musulmi da jarrabãwa mai kyau daga gare shi. Kuma Allah Mai ji ne, Masani.
18Wancan ne, kuma lalle ne, Allah Mai raunana kaidin kãfirai ne.
19Idan kun yi alfãnun cin nasara to lalle nasarar tã je muku, kuma idan kun hanu, to Shi ne Mafi alhħri a gare ku, kuma idan kun kõma zã Mu kõma, kuma jama´arku bã zã ta wadãtar muku da kõme ba, kõ dã tã yi yawa. Kuma lalle ne cħwa Allah Yanã tãre da mũminai!
20Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku jũya daga barinSa, alhãli kunã ji.
21Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka ce: "Mun ji, alhãli kuwa sũ bã su ji."
22Lalle ne, mafi sharrin dabbõbi a wurin Allah, sũ ne kurãme, bħbãye, waɗanda Bã su yin hankali.
23Dã Allah Yã san wani alhħri a cikinsu, dã Yã jiyar da su, kuma kõ da Yãjiyar da su, haƙĩƙa, dã sun jũya , alhãli sũ, sunã mãsu hinjirħwa.
24Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku karɓa wa Allah, kuma ku karɓa wa Manzo, idan Ya kirãye ku zuwa ga abin da Yake rãyar da ku; Kuma ku sani cħwa Allah Yanã shãmakacħwa a tsakãnin mutum da zũciyarsa, kuma lalle ne Shĩ, a zuwa gare Shi ake tãra ku.
25Kuma ku ji tsõron fitina wadda bã ta sãmun waɗanda suka yi zãlunci daga gare ku kħɓe, kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
26Ku tuna a lõkacin da kuke kaɗan, waɗanda ake raunanarwã a cikin ƙasa kunã tsõron mutãne su cafe ku, sai Ya tattara ku (a wurin natsuwa, Maɗina), kuma Ya ƙarfafã ku da taimakonSa kuma Ya azurtã ku daga abũbuwa mãsu dãɗi; Tsammãninku, kunã gõdħwa.
27Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari amãnõninku, alhãli kuwa kunã sane.
28Kuma ku sani cħwa abin sani kawai, dũkiyõyinku da ´ya´yanku, wata fitina ce, kuma lalle ne Allah, a wurinSa, akwai ijãra mai girma.
29Ya kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun bi Allah da taƙawa, zai sanyã muku mararraba (da tsõro) kuma Ya kankare ƙanãnan zunubanku daga barinku. Kuma Ya gãfartã muku. Kuma Allah ne Ma´abũcin falalã Mai girma.
30Kuma a lõkacin da waɗanda(1) suka kãfirta sukħ yin mãkirci game da kai, dõmin su tabbatar da kai, kõ kuwa su kashe ka, kõ kuwa su fitar da kai, sunã mãkirci kuma Allah Yanã mayar musa da mãkirci kuma Allah ne Mafificin mãsu mãkirci.
31Kuma idan aka karanta, ãyõyinMu a kansu, sukan ce: "Lalle ne mun ji dã muna so, haƙĩƙa, da mun faɗi irin wannan; wannan bai zama ba fãce tãtsunãyõyin mutãnen farko."
32A lõkacin da suka ce: "Yã Allah! Idan wannan ya kasance shĩ ne gaskiya daga wurinKa, sai Ka yi ruwan duwãtsu, a kanmu, daga sama, kõ kuwa Kazõ mana da wata azãba, mai raɗaɗi."
33Kuma Allah bai kasance Yanã yi musu azãba ba alhãli kuwa kai kanã cikinsu,(2) kuma Allah bai kasance Mai yi musu azãba ba alhãli kuwa sunã yin istigfãri.
34Kuma mħne ne a gare su da Allah ba zai yi musu azãba ba, alhãli kuwa sũ, sunã kangħwa daga Masallaci Mai alfarma kuma ba su kasance majiɓintanSa ba? Bãbu majiɓintanSa fãce mãsu taƙawa. Kuma mafi yawansu ba su sani ba.
35Kuma sallarsu a wurin Ɗãkin ba ta kasance ba fãce shħwa da yãyã; sai ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kasance kunã yi na kãfirci.
36Lalle ne waɗanda suka kãfirta, sunã ciyar da dũkiyõyinsu, dõmin su kange daga hanyar Allah; to, zã a su ciyar da ita, sa´ an nan kuma ta kasance nadãma a kansu, sa´an nan kuma a rinjãye su. Kuma waɗanda suka kãfirta zuwa ga Jahannama ake tãra su;
37Dõmin Allah Ya rarrabe mummũna daga mai kyau, kuma Ya sanya mummũnan, sãshensa a kan sãshe, sa´an nan Ya shirga shi gabã daya, sa´an nan Ya sanyã shi a cikin Jahannama. Waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
38Ka ce wa waɗanda suka kãfirta, idan sun hanu, zã a gãfarta musu abin da ya riga ya shige, kuma idan sun kõma, to, hanyar kãfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe.
39Kuma ku yãƙe su har wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini dukansa ya kasance na Allah. To, idan sun hanu to lalle ne, Allah ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne.
40Kuma idan sun jũya, to, ku sani cħwa lalle Allah ne Majiɓincinku: Mãdalla da Majiɓinci, kuma mãdalla da Mai taimako, Shĩ.
41Kuma ku sani, abin da kuka sãmi(1) ganĩma daga wani abu, to, lalle ne Allah Yanã da humusinsa kuma da Manzo, kuma da mãsu zumunta, da marãyu da miskĩnai da ɗan hanya, idan kun kasance kun yi ĩmãni da Allah da abin da Muka saukar a kan bãwanMu a Rãnar Rarrabħwa, a Rãnar da jama´a biyu suka haɗu, kuma Allah ne, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi.
42A lõkacin da kuke a gãɓa ta kusa sũ kuma sunã a gãɓa ta nħsa, kuma ãyarin yana a wuri mafi gangarãwa daga gare ku, kuma dã kun yi wa jũna wa´adi, dã kun sãɓa ga wa´adin; kuma amma dõmin Allah Ya hukunta abin da yake ya kasance abin aikatãwa. Dõmin wanda yake halaka ya halaka daga shaida, kuma mai rãyuwa ya rãyu daga shaida, kuma lalle Allah ne, haƙĩƙa, Mai ji Masani.
43A lõkacin da Allah Yake nũna maka sũ sunã kaɗan, a cikin barcinka, kuma dã Ya nũna maka su sunã Da yawa, lalle ne dã kun ji tsõro, kuma lalle ne dã kun yi jãyayya a cikin al´amarin, kuma amma Allah Yã tsare ku: Lalle Shĩ ne Masani ga abin da yake a cikin ƙirãza.
44Kuma a lõkacin da Yake nũna muku su, a lõkacin da kuka haɗu, a cikin idanunku sunã kaɗan, kuma Ya ƙarantar da ku a cikin idanunsu dõmin Allah Ya hukunta wani al´amari wanda ya kasance abin aikatãwa. Kuma zuwa ga Allah ake mayar da al´umurra.
45Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun haɗu da wata ƙungiyar yãƙi, to, ku tabbata, kuma ku ambaci(2) Allah da yawa, tsammãninku kunã cin nasara.
46Kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku yi jãyayya har ku raunana kuma iskarku ta tafi, kuma ku yi haƙuri. Lalle ne Allah Yanã tãre da mãsu haƙuri.
47Kada ku kasance kamar waɗanda suka fita daga gidãjensu(1) , sunã mãsu alfahari da yin riya ga mutãne, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah. Kuma Allah ne ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa.
48Kuma a lõkacin da Shaiɗan(2) ya ƙawãce musu ayyukansu, kuma ya ce: "Bãbu marinjayi a gareku a yau daga mutãne, kuma nĩ maƙwabci ne gare ku." To, a lõkacin da ƙungiya biyu suka haɗu, ya kõma a kan digãdigansa, kuma ya ce: "Lalle ne nĩ barrantacce ne daga gare ku! Nĩ inã ganin abin da bã ku gani; ni inã tsõron Allah: Kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne."
49A lõkacin da munãfukai da waɗanda suke akwai cũtã a cikin zukãtansu, suke cħwa: "Addĩnin waɗannan yã rũɗe su. " Kuma wanda ya dõgara ga Allah, to, lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
50Kuma dã kã gani, a lõkacin da Malã´iku suke karɓar rãyukan waɗanda suka kãfirta, sunã dukar fuskõkinsu da ɗuwãwunsu, kuma suna cħwa: "Ku ɗanɗani azãbar Gõbara."
51"Wancan sabõda abin da hannãyenku suka gabãtar ne. Kuma lalle ne, Allah bai zama Mai zãlunci ba ga, bãyinSa."
52"Kamar al´ãdar mutãnen Fir´auna da waɗanda suke gabãninsu, sun kãfirta da ãyõyin Allah, sai Allah Ya kãma su da zunubansu. Lalle Allah ne Mai ƙarfi, Mai tsananin uƙũba.
53"Wancan ne, dõmin lalle ne, Allah bai kasance Mai canza wata ni´ima wadda ya ni´imtar da ita a kan wasu mutãne ba fãce sun sãke abin da yake ga rãyukansu, kuma dõmin lalle Allah ne Mai jĩ,Masani."
54Kamar al´adar mutãnen Fir´auna da waɗanda suke a gabãninsu, sun ƙaryata game da ãyõyin Ubangijinsu, sai Muka halaka su, sabõda zunubansu, kuma Muka nutsar da mutãnen Fir´auna. Kuma dukansu sun kasance ne mãsu zãlunci.
55Lalle mafi sharrin dabbõbi a wurin Allah, sũ ne waɗanda suka kãfirta, sa´an nan bã zã su yi ĩmãni ba.
56Waɗanda ka yi ƙullin alkawari da su, daga gare su, sa´an nan kuma sunã warwarewar alkawarinsu a kõwane lõkaci kuma sũ, bã su yin taƙawa.
57To, in dai ka kãma su a cikin yãƙi, sai ka kõre(1) waɗanda suke a bãyansu, game da su, tsammãninsu, zã su dinga tunãwa.
58Kuma in ka ji tsõron wata yaudara daga wasu mutãne, to, ka jħfar da alkawarin, zuwa gare su, a kan daidaita: Lalle ne Allah, bã Ya son mayaudara.
59Kuma waɗanda suka kãfirta kada su yi zaton sun tsħre: Lalle ne sũ, bã zã su gãgara ba.
60Kuma ku yi tattali, dõminsu, abin da kuka sãmi ĩkon yi na wani ƙarfi,(2) kuma da ajiye dawaki, kunã tsoratarwa, game da shi, ga maƙiyin Allah kuma maƙiyinku da wasu, baicin su, ba ku san su ba, Allah ne Yake sanin su, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu a cikin hanyar Allah, zã a cika muku sakamakonsa, kuma kũ ba a zãluntar ku.
61Kuma idan sun karkata zuwa ga zaman lãfiya, to, ka karkata zuwa gare shi, kuma ka dõgara ga Allah: Lalle ne Shĩ, Mai ji ne Masani.
62Kuma idan sun yi nufin su yaudare ka, to, lalle ma´ishinka Allah ne, Shĩ ne wanda Ya ƙarfafa ka da taimakonSa, kuma da mũminai.
63Kuma Ya sanya sõyayya a tsakãnin zukãtansu. Dã kã ciyar da abin da yake cikin ƙasa, gabã ɗaya, dã ba ka sanya sõyayya a tsakãnin zukãtansu ba, kuma amma Allah Yã sanya sõyayya a tsakãninsu. Lalle Shi ne Mabuwãyi, Mai hikima.
64Ya kai Annabi! Ma´ishinka Allah ne, kai da wanda ya biye maka daga mũminai.
65Ya kai Annabi! Ka kwaɗaitar da mũminai a kan yãƙi. Idan mutum ashirin mãsu haƙuri sun kasance daga gare ku, zã su rinjãyi mħtan kuma idan ɗari suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi dubu daga waɗanda suka kãfirta, dõmin sũ, mutãne ne bã su fahimta.
66A yanzu Allah Yã sauƙaƙe daga gare ku, kuma Yã sani cħwa lalle ne akwai mãsu rauni a cikinku. To, idan mutum ɗari, mãsu haƙuri, suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi mħtan, kuma idan dubu suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi dubu biyu, da iznin Allah. Kuma Allah Yanã tãre da mãsu haƙuri.
67Bã ya kasancewa(1) ga wani annabi, kãmammu su kasance a gare shi sai (bãyan) yã zubar da jinainai a cikin ƙasa. Kunã nufin sifar dũniya kuma Allah Yanã nufin Lãhira. Kuma Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima.
68Bã dõmin wani Littãfi daga Allah ba, wanda ya gabãta(2) , dã azãba mai girma daga Allah tã shãfe ku a cikin abin da kuka kãma.
69Sabõda haka, ku ci daga abin da kuka sãmu ganĩma, yanã halal mai kyau. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.
70Ya kai Annabi! Ka ce wa wanda yake a cikin hannãyenku daga kãmammu: "Idan Allah Ya san akwai wani alhħri a cikin zukãtanku, zai kawo muku mafi alhħri daga abin da aka karɓa daga gare ku, kuma Ya yi muku gãfara. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."
71Kuma idan sun yi nufin yaudararka, to, haƙĩƙa, sun yaudari Allah daga gabãni sai Ya bãyar da dãmã daga gare su: Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
72Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu, a cikin hanyar Allah, da waɗanda suka bãyar da masauki, kuma suka yi taimako. Waɗancan, sãshensu waliyyai ne ga sãshe. Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma ba su yi hijira(1) ba, bã ku da wani abu daga waliccinsu, sai sun yi hijira. Kuma idan suka nħme ku taimako a cikin addini, to taimako yã wajaba a kanku, fãce a kan mutãne waɗanda a tsakãninku da tsakãninsu akwai wani alkwari. Kuma Allah ne, ga abin da kuke aikatãwa, Mai gani.
73Kuma waɗanda suka kãfirta sãshensu ne waliyyan sãshe, idan ba ku aikata shi ba, wata fitina zã ta kasance a cikin ƙasa, da fasãdi babba.
74Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka yi hijira, kuma suka yi Jihãdi, a cikin hanyar Allah, kuma da waɗanda suka bãyar da masauki, kuma suka yi tamiako, waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya, sunã da gãfara da wani abinci na karimci.
75Kuma waɗanda suka yi ĩmãni daga bãya, kuma suka yi hijira kuma suka yi jihãdi tãre da ku, to, waɗannan daga gare ku suke. Kuma ma´abũta zumunta, sãshensu ne waliyyan(2) sãshe a cikin Littãfin Allah. Lalle Allah ne ga dukkan kõme Masani.
Chapter 9 (Sura 9)
1Barranta daga Allah da ManzonSa zuwa ga waɗanda kuka yi wa alkawari daga mãsu shirki(1)
2Sabõda haka ku yi tafiya a cikin ƙasa watã huɗu,(2) kuma ku sani lalle kũ, bã mãsu buwãyar Allah ba ne, kuma lalle Allah ne Mai kunyatar da kãfirai.
3Kuma da yħkuwa daga Allah da ManzonSa zuwa ga mutãne, a Rãnar Haji Babba cħwa lallene Allah Barrantacce ne daga mãsu shirki, kuma ManzonSa (haka). To, idan kun tũba to shi ne mafi alhħri a gare ku, kuma idan kun jũya, to, ku sani lalle ne kũ, bã mãsu buwãyar Allah ba ne. Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka kãfirta, da azãba mai raɗaɗi.
4Sai waɗanda kuka yi wani alkawari daga mãsu shirki, sa´an nan kuma ba su rage ku da kõme ba, kuma ba su taimaki kõwa a kanku ba, to, ku cika alkawarin, zuwa gare su, har ga iyakar yarjħjħyarsu. Lalle ne Allah Yanã son mãsu taƙawa.
5Kuma idan watanni, mãsu alfarma suka shige, to, ku yãki mushirikai inda kuka sãmħ su, kuma ku kãmã su, kuma ku tsare su, kuma ku zaune musu dukkan madãkata. To, idan sun tũba, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka to ku sakar musu da hanyarsu. Lalle Allah ne Mai gãfara,Mai jin ƙai.
6Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya ji, maganar Allah, sa´an nan ka isar da shi ga wurin amincewarsa. Wancan fa domin lalle ne su, mutãne ne waɗanda ba su sani ba.
7Yãya wani alkawari a wurin Allah a wurin ManzonSa yake kasancħwa ga mushirikai, fãce ga waɗanda kuka yi wa alkawari wurin Masallaci Mai alfarma? To matuƙar sun tsaya sõsai gare ku, sai ku tsayu sõsai gare su. Lalle ne Allah Yanã son mãsu taƙawa.
8Yãya, alhãli idan sun ci nasara a kanku, bã zã su tsare wata zumun ta ba a cikinku, kuma haka wata amãna, sunã yardar da ku da bãkunansu kuma zukãtansu sunã ƙi? Kuma mafi yawansu fãsiƙai ne.
9Sun saya da ãyõyin Allah, ´yan kuɗi kaɗan, sa´an nan suka kange daga hanyar Allah. Lalle ne sũ, abin da suka kasance sunã aikatãwa yã mũnana.
10Bã su tsaron wata zumunta a cikin mũminai, kuma haka bãsu tsaron wata amãna. Kuma waɗannan ne mãsu ta´adi.
11Sa´an nan idan sun tũba(1) kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka, to, ´yan´uwanku ne a cikin addini, kuma Munã rarrabe ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke sani.
12Kuma idan suka warware rantsuwõyin amãna daga bãyan alkawarinsu, kuma suka yi sũka a cikin addininku, to, ku yaki shũgabannin kãfirci. Lalle ne sũ, bãbu rantsuwõyin amãna a gare su. Tsammãninsu sunã hanuwa.
13Shin, bã ku yaƙin mutãne, waɗanda suka warware rantsuwõyinsu, kuma suka yi niyya ga fitar da Manzo, kuma sũ ne suka fãra muku, tun a farkon lõkaci? Shin kunã tsõron su ne? To, Allah ne marfi cancantar ku ji tsõronSa, idan kun kasance mũminai!
14Ku yãƙe su, Allah Ya yi musu azabã da hannãyenku, kuma Ya kunyatar da su, kuma Ya taimake ku, kuma Ya warkar da ƙirãzan mutãne mũminai.
15Kuma Ya tafĩ da fushin zukãtansu, kuma Ya karɓi tũba a kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
16Kõ kunã zaton(1) a bar ku, tun Allah bai bayyana waɗanda suka yi jihãdi ba daga gare ku, kuma sũ ba su riƙi wani shigeba, baicin Allah da ManzonSa da mũminai? Kuma Allah ne Mai jarrabãwa ga abin da kuke aikatãwa.
17Bã ya kasancewa ga mãsu shirki su rãya masallatan Allah, alhãli kuwa sunã mãsu bãyar da shaida a kan rãyukansu da kafirci, waɗannan ayyukansu sun ɓãci, kuma a cikin wutã sũ madawwama
18Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu.
19Shin, kun sanya shãyar da mahajjata da rãyar da Masallaci Mai alfarma kamar wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya yi jihãɗi a cikin hanyar Allah? Bã su daidaita a wurin Allah. Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
20Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihãdi, a cikin hanyar Allah, da dũkiyõyinsu, da rãyukansu, sũ ne mafi girma ga daraja, a wurin Allah, kuma waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
21Ubangijinsu Yanã yi musu bishãra da wata rahama daga gare shi, da yarda, da gidãjen Aljanna. sunã da, a cikinsu, ni´ima zaunanniya.
22Sunã madawwamã a cikinsu, har abada. Lalle ne Allah a wurinSa akwai lãda mai girma.
23Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi ubanninku da ´yan´uwanku masõya, idan sun nũna son kãfirci a kan ĩmãni.(1) Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, waɗannan sũ ne azzãlumai.
24Ka ce: "Idan ubanninku da ɗiyanku da ´yan´uwanku da mãtanku da danginku da dũkiyõyi, waɗanda kuka yi tsiwirwirinsu, da fatauci wanda kuke tsõron tasgaronsa, da gidaje waɗanda kuke yarda da su, sun kasance mafiya sõyuwa a gare ku daga Allah da ManzonSa, da yin jihãdi ga hanyarSa, to, ku yi jira har Allah Ya zo da umurninSa! Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai."
25Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a cikin wurãre mãsu yawa, da Rãnar Hunainu,(2) a lõkacin da yawanku ya bã ku sha´awa, sai bai amfãnar da ku da kõme ba, kuma ƙasa ta yi ƙunci a kanku da yalwarta, sa´an nan kuma kuka jũya kunã mãsu bãyar da bãya.
26Sa´an nan kuma Allah Ya saukar da natsuwarSa a kan ManzonSa kuma a kan mũminai, kuma Ya saukar da rundunõni waɗanda ba ku gan su ba, kuma Ya azabtar da waɗanda suka kãfirta: Wancan ne sakamakon kãfirai.
27Sa´an nan kuma Allah Ya karɓi tũba daga bãyan wancana kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai rahama.
28Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, sabõda haka kada su kusanci Masallaci Mai alfarma a bãyan shħkararsu wannan. Kuma idan kun ji tsõron talauci(1) to, da sannu Allah zai wadãta ku daga falalarSa, idan Ya so. Lalle Allah ne Masani, mai hikima.
29Ku yãƙi waɗanda(2) bã su yin ĩmãni da Allah kuma bã su ĩmãni da Rãnar Lãhira kumabã su haramta abin da Allah da ManzonSa suka haramta, kuma bã su yin addini, addinin gaskiya, daga waɗanda aka bai wa Littãfi, har sai sun bãyar da jizya daga, hannu, kuma sunã ƙasƙantattu.
30Kuma Yahũdãwa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasãra suka ce: "Masĩhu ɗan Allah ne." Wancan zancensu ne da bãkunansu. Sunã kamã da maganar waɗanda suka kãfirta daga gabãni. Allah Yã la´ance su! Yãya aka karkatar da su?
31Sun riƙi mãlamansu(3) (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama ( haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi.
32Sunã nufin su bice hasken Allah da bãkunãnsu. Kuma Allah Yanã ki, fãce dai Ya cika haskenSa, kuma kõ da kãfirai sun ƙi.
33Shi ne wanda Ya aiko manzonSa da shiriya da addinin gaskiya, dõmin ya bayyanl shi a kan addini dukansa, kuma kõ dã mushirikai sun ƙi.
34Yã waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle ne mãsu yawa daga Ahbãr(1) da Ruhbãnãwa haƙĩƙa sunã cin dũkiyar mutãne da ƙarya, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah. Kuma waɗanda suke taskacħwar zĩnãriya da azurfa, kuma bã su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
35A Rãnar da ake ƙõna shi a kanta a cikin wutar Jahannama, sai a yi lalas da ita ga gõshinansu da sãshinansu da bãyayyakinsu, (a ce musu): "Wannan ne abin da kuka taskace dõmin rãyukanku. To, ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã sanyãwa a taska."
36Lallai ne ƙidãyayyun watanni a wurin Allah watã gõma shã biyu ne a cikin Littãfin(2) Allah, a Rãnar da Ya halicci sammai da ƙasa daga cikinsu akwai huɗu mãsu alfarma. Wannan ne addini madaidaici. Sabõda haka kada ku zãlunci kanku a cikinsu. Kuma ku yãƙi mushirikai gabã ɗaya, kamar yadda suke yãƙar ku gabã ɗaya. Kuma ku sani cħwa lallai ne Allah Yanã tãre da mãsu taƙawa.
37Abin sani kawai, "Jinkirtãwa" ƙãri ne a cikin kãfirci, anã ɓatar da waɗanda suka kãfirta game da shi. Sunã halattar da watã a wata shħkara kuma su haramtar da shi a wata shħkara dõmin su dãce da adadin abin da Allah Ya haramta. Sabõda haka sunã halattar da abin da Allah Ya haramtar. An ƙawãce musu mũnanan ayyukansu. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne kãfirai.
38Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Mħne ne a gare ku, idan ance muku, "Ku fita da yãƙi a cikin hanyar Allah," sai ku yi nauyi(1) zuwa ga ƙasa. Shin, kun yarda da rãyuwar dũniya ne daga ta Lãhira? To jin dãɗin rãyuwar dũniya bai zama ba a cikin Lãhira, fãce kaɗan.
39Idan ba ku fita da yãƙi ba, Allah zai azabta ku da azãba mai raɗaɗi, kuma Ya musanya wasu mutãne, wasunku (a maimakonku). Kuma bã zã ku cũtar da Shida kõme ba. Kuma Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.
40Idan ba ku taimake shi ba, to, lalle ne Allah Yã taimake shi, a lõkacin da waɗanda suka kãfirta suka fitar da shi, Yanã na biyun biyu, a lõkacin da suke cikin kõgon dũtse, a lõkacin da yake cħwa da sãhibinsa: "Kada ka yi baƙin ciki, lalle ne Allah Yanã tãre da mu." Sai Allah Ya saukar da natsuwarSa a kansa, kuma Ya taimake shi da waɗansu rundunõni, ba ku gan su ba, kuma Ya sanya kalmar waɗanda suka kãfirta maƙasƙanciya, kuma kalmar Allah ita ce maɗaukakiya. Kuma Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima.
41Ku fita da yãƙi kunã mãsu sauƙãƙan kãyã da mãsu nauyi, kuma ku yi jihãdi da dũkiyõyinku da kuma rãyukanku a cikin hanyar Allah. Wancan ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kunã sani.
42Dã yã kasance(1) wata siffar dũniya ce: makusanciya, da tafiya matsakaiciya, dã sun bĩ ka, kuma amma fagen yã yi musu nĩsa.Kuma zã su yi ta yin rantsuwa da Allah, "Dã mun sãmi dãma, dã mun tafi tare da ku." Sunã halakar da kansu (da rantsuwar ƙarya) ne, kuma Allah Yanã sanin lalle, haƙĩƙa, sumaƙaryata ne.´
43Allah Ya yãfe maka laifi. Dõmin me ka yi musu izinin zama? Sai waɗanda suka yi gaskiya ssun bayyana a gare ka, kuma ka san maƙaryata.
44Waɗanda suke yin ĩmãnida Allah da Rãnar Lãhira, bã zã su nħmi izininka ga yin, jihãdida dũkiyõyinsu da rãyukansu ba. Kuma Allah ne Masani ga mãsu taƙawa.
45Abin sani kawai, waɗanda bã sa ĩmãni da Allah, da Rãnar Lãhira, kuma zukãtansu suka yi shakka, sũ ne ke nħman izininka, sa´an nan a cikin shakkarsu sunã ta yin kai kãwo.
46Kuma dã sun yi nufin fita, dã sun yi wani tattali sabõda shi, kuma amma Allah Ya ƙi zãburarsu, sai Ya nauyayar da zamansu. Kuma aka ce ku zauna tãre da mãsu(2) zama.
47Dã sun fita a cikinku bã zã su ƙãre ku da kõme ba fãce da ɓarna, kuma lalle dã sun yi gaggãwar sanya annamĩmanci a tsakãninku, sunã nħma muku fitina. Kuma a cikinku akwai ´yan rahõto sabõda su. Kuma Allah ne Masani ga azzãlumai,
48Kuma lalle ne, haƙĩƙa sun nħmi fitina daga gabãni, kuma, suka jũya maka al´amari, har gaskiya ta zo,(1) kuma umurnin Allah Ya bayyana, alhãli sunã mãsu ƙyãma,
49Kuma daga cikinsu(2) akwai mai cħwa, "Ka yi mini izinin zama, kuma kada ka fitine ni." To, a cikin fitinar suka fãɗa. Kuma lalle ne Jahannama, haƙĩƙa, mai ƙħwayħwa ce ga kãfirai.
50Idan wani alhħri ya sãme ka, zai ɓãta musu rai, kuma idan wata masifa ta sãme ka sai su ce: "Haƙĩƙa, mun riƙe al´amarinmu daga gabãni."Kuma sujũya, alhãli kuwa sunã mãsu farin ciki.
51Ka ce: "Bãbu abin da yake sãmun mu fãce abin da Allah Ya rubũta sahõda mu. Shĩ ne Majiɓincinmu. Kuma ga Allah, sai mũminai su dõgara."
52Ka ce: "Shin, kunã dãko ne da mu? Fãce dai da ɗayan abũbuwan biyu(3) mãsu kyau, alhãli kuwa mũ, munã dãko da ku, AllahYa sãme ku da wata azãba daga gare Shi, kõ kuwa da hannayenmu. To, ku yi dãko. Lalle ne mũ, tãre da ku mãsu dãkon ne."
53Ka ce: "Ku ciyar a kan yarda kõ kuwa a kan tĩlas. Bã zã a karɓa daga gare ku ba. Lalle ne kũ, kun kasance mutãne fãsiƙai."
54Kuma bãbu abin da ya hana a karɓi ciyarwarsu daga gare su fãce dõmin sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma bã su zuwa ga salla fãce Luma sunã mãsu kasãla, kuma bã su ciyarwa fãce sunã mãsu ƙyãma.
55Sabõda haka, kada dũkiyõyinsu su bã ka sha´awa, kuma haka ´ya´yansu. Abin sani kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba, da su a cikin rãyuwar dũniya, kuma rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai.
56Kuma sunã rantsuwa da Allah cħwa, lalle ne sũ, haƙĩƙa, daga gare ku suke, alhãli kuwa ba su zamo daga gare ku ba. Kuma amma sũ mutãne ne mãsu tsõro.
57Dã sunã sãmun mafaka kõ kuwa waɗansu ɓulõli, kõ kuwa wani mashigi, da sun, jũya zuwa gare shi, kuma suna gaggawar shiga.
58Kuma daga cikinsu akwai wanda yake zunɗen ka a kan sha´anin dũkiyõyin sadaka, sai idan an bã su daga cikinta, su yarda, kuma idan ba a bã su ba daga cikinta sai su zamo sunã mãsu fushi.
59Kuma dã dai su lalle sun yarda da abin da Allah Ya bã su, da ManzonSa kuma suka ce: "Ma´ishinmu Allah ne, zai kãwo mana daga falalarSa kuma ManzõnSa (zai bã mu). Lalle ne mũ, zuwa ga Allah mãsu kwaɗayi ne."
60Abin sani kawai, dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da mabarta, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
61Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke cũtar Annabi, kuma sunã cħwa "Shi kunne(1) ne." Ka ce: "Kunnen alhħri gare ku,Yanã ĩmãni da Allah, kuma Yanã yarda da mũminai, kuma rahama ne ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare ku."Kuma waɗanda suke cũtar Manzon Allah sunã da azãba mai raɗaɗi.
62Sunã rantsuwa da Allah sabõda ku, dõmin su yardar da ku. Kuma Allah da ManzonSa ne mafi cancantar su yardar da Shi, idan sun kasance mũminai.
63Shin, ba su sani ba cħwa "Lalle ne wanda ya sãɓa wa Allah da ManzonSa, haƙĩƙa Yanã da wutar Jahannama, Yanã madawwami a cikinta? Waccan ita ce wulãkantãwa babba!"
64Munãfukai sunã tsõron a saukar da wata sũra a kansu,wadda take bã su lãbãri ga abin da yake cikin zukãtansu. Ka ce: "Ku yi izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitai da abin da kuke tsõro."
65Kuma lalle ne, idan ka tambaye(1) , su haƙĩƙa, sunã cħwa, "Abin sani kawai, mun kasance munã hĩra kuma munã wãsã. Ka ce: "Shin da Allah, da kuma ãyõyinSa da ManzonSa kuka kasance kunã izgili?"
66"Kada ku kãwo wani uzuri, haƙĩƙa, kun kãfirta a bãyanĩmãninku. Idan Mun yãfe laifi ga wata ƙungiya daga gare ku, zã Mu azabta wata ƙungiya sabõda, lalle, sun kasance mãsu laifi."
67Munãfukai maza da munãfukai mãtã, sãshensu(2) daga sãshe, sunã umurni da abin ƙi kuma sunã hani daga alhħri.Kuma sunã damƙħwar hannayensu.Sun mance Allah, sai Ya mantã da su. Lalle ne munãfukai sũ ne fãsiƙai.
68Allah yã yi wa´adi ga munãfukai maza da munãfukai mãtã da kãfirai da wutar Jahannama, sunã madawwama a cikinta. Ita ce ma´ishiyarsu. Kuma Allah Yã la´ance su, kuma sunã da azãba zaunanniya.
69Kamar waɗanda suke a gabãninku, sun kasance mafi tsananin ƙarfi daga gare ku, kuma mafi yawan dũkiyõyi da ɗiya. Sai suka ji daɗi da rabonsu, sai kuka ji daɗi da rabonku kamar yadda waɗanda suke a gabãninku suka ji dãɗi, da rabonsu, kuma kuka kũtsa kamar kũtsãwarsu. Waɗancan ayyukansu sun ɓãci a dũniya da Lãhira, kuma waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
70Shin lãbarin waɗanda suke a gabãninsu bai je musu ba, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdãwa da mutãnen Ibrãhĩm da Ma´abũta Madyana da waɗanda aka birkice? Manzanninsu sun jħ musu da ãyõyayi bayanannu. To, Allah bai kasance Yanã zãluntar su ba, amma sun kasance rãyukansu suke zãlunta.
71Kuma mummunai maza da mummunai mãtã sãshensu majiɓincin sãshe ne, sunã umurni da alhħri(1) kuma sunã hani daga abin da bã a so, kuma sunã tsayar da salla, kuma sunã bãyar da zakka, kuma sunãɗã´a ga Allah da ManzonSa. Waɗannan Allah zai yi musu rahama. Lalle Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima.
72Kuma Allah Yã yi wa´adi ga mummunai maza da mummunai mãtã da gidãjen Aljanna ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwamã a cikinsu, da wurãren zama mãsu dãɗi a cikin gidãjen Aljannar. Kuma yarda daga Allah ce mafi girma. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
73Ya kai Annabi! Ka yãƙi kãfirai da munãfukai kuma ka tsaurara a kansu. Kuma matattararsu Jahannama ce. Tir da ta zama makõmar!
74Sunã rantsuwa da Allah, ba su faɗa ba, alhãli kuwa lalle ne, haƙĩƙa, sun faɗi kalmar kãfirci, kuma; sun kãfirta a bãyan musuluntarsu, kuma sun yi himma ga abin da ba su sãmu ba. Kuma ba su zargi kõme ba fãce dõmin Allah da ManzonSa Ya wadãtar da su daga falalarSa. To, idan sun tũba zai kasance mafi alhħri gare su,kuma idan sun jũya bãya, Allah zaiazabtã su da azãba mai raɗaɗi a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wani masõyi kõ wani mataimaki a cikin kasa.
75Kuma daga cikinsu akwai wadɗanda suka yi wa Allah alkawari, "Lalle ne idan ya kãwo mana daga falalarSa, haƙĩƙa, munãbãyar da sadaka, kuma lalle ne munã kasancħwa, daga sãlihai."
76To, a lõkacin da Ya bã su daga falalarSa, sai suka yi rõwa da shi, kuma suka jũya bãya sunã mãsu bijirħwa,
77Sai Ya biyar musu da munãfunci a cikin zukatansu har zuwa ga Rãnar da suke haɗuwa da Shi sabõda sãɓã wa Allah a abin da suka yi Masa alkawari, kuma sabõda abin da suka kasance sunã yi na ƙarya.
78Shin, ba su sani ba cħwa lalle ne Allah Yanã sanin asĩrinsuda gãnawarsu, kuma lalle Allah ne Masanin abũbuwan fake?
79Waɗanda suke aibanta mãsu yin alhħri daga mummunaia cikin dũkiyõyin sadaka, da waɗanda ba su sãmu fãce iyãkar ƙõƙarinsu, sai sanã yi musu izgili. Allah Yanã yin izgili gare su. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
80Kõ kã nħma musu gãfara ko ba ka nħma musu ba, idan ka nħma musu gãfara sau saba´in, to, Allah bã zai gãfarta musu ba. Sabõda sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne fãsiƙai.
81Waɗanda aka bari sun yi farin ciki da zamansu a bãyan Manzon Allah, kuma suka ƙi su yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu a cikin hanyar Allah, kuma suka ce: "Kada ku fita zuwa yãƙi a cikin zãfi."Ka ce: "Wutar Jahannama ce mafi tsanlnin zãfi." Dã sun kasance sunã fahimta!
82Sabõda haka su yi dãriya kaɗan, kuma su yi kũkada yawa a kan sãkamako ga abin da suka kasance sunã tsirfatãwa.
83To, idan Allah Ya mayar da kai zuwa ga wata ƙungiyã daga gare su sa´an nan suka nħme ka izni dõmin su fita, to, ka ce: "Bã zã ku fita tãre da nĩ ba har abada,kuma bã zã ku yi yãƙi tãre da nĩ ba a kan wani maƙiyi. Lalle ne kũ, kun yarda da zama a farkon lõkaci, sai ku zauna tãre da mãtã mãsu zaman gida."
84Kuma kada ka yi salla a kan kõwa daga cikinsu wanda ya mutu, har abada, kuma kada ka tsaya a kan kabarinsa. Lalle ne sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma sun mutu alhãli kuwa sunã fãsiƙai.
85Kuma kada dũkiyõyinsu da ɗiyansu su bã ka sha´awa. Abin sani kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba da su a cikin dũniya, kuma rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai.
86Kuma idan aka saukar da wata sũra cħwa; Ku yi ĩmãni da Allah kuma ku yi jihãdi tãre da ManzionSa. Sai mawadãta daga gare su su nħmi izninka, kuma su ce: Ka bar mu mu kasance tãre da mazauna.
87Sun yarda da su kasance tãre da mãtã mãsu zama (a cikin gidãje). Kuma aka rufe a kan zukãtansu, sabõda haka, sũ, bã su fahimta.
88Amma Manzon Allah da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sun yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu. Kuma waɗannan sunã da ayyukan alhħri, kuma waɗannan sũ ne mãsu cin nasara.
89Allah yã yi musu tattalin gidãjen Aljanna, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwamã a cikinsu. Wancan ne babban rabo mai girma.
90Kuma mãsu uzuri daga ƙauyãwa zuka zo dõmin a yi musu izini, kuma waɗanda suka yi wa Allah da ManzonSa ƙarya, suka yi zamansu. wata azãba mai raɗaɗi zã ta sãmi waɗanda suka kãfirta daga gare su.
91Bãbu laifi a kan maraunana kuma haka majinyata, kuma bãbu laifi a kan waɗanda bã su sãmun abin da suke ciyarwa idan sun yi nasĩha(1) ga Allah da ManzonSa. Kuma bãbu wani laifi a kan mãsu kyautatãwa. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai tausayi.
92Kuma bãbu (laifi) a kan waɗanda idan sun je maka dõmin ka ɗauke su ka ce: "Bã ni da abin da nake ɗaukar ku a kansa," suka jũya alhãli kuwa idãnunsu sunã zubar da hawãye dõmin baƙin ciki cħwa ba su sãmi abin da suke ciyarwa ba.
93Abin sani kawai, laifi Yanã a kan waɗanda suke nħman izininka alhãli kuwa sũ mawadãta ne.Sun yarda su kasance tãre da mãtã mamaya (gidãje), kuma Allah Yã danne a kan zukãtansu, dõmin haka sũ, bã su gãnħwa.
94Sunã kãwo uzurinsu zuwa gare ku idan kun kõma zuwa gare su Ka ce: "Kada ku kãwo wani uzuri, bã zã mu amince muku ba. Haƙĩƙa, Allah Yã bã mu lãbãri daga lãbãrunku, Allah zai ga aikinku kuma ManzonSa (zai gani). Sa´an nan kuma a mayar da ku zuwa ga Masanin gaibi da bayyane, sai Ya bã ku lãbarin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
95Zã su yi rantsuwa da Allah a gare ku idan kun jũya zuwa gare su, dõmin ku kau da kai daga gare su. To, ku kau da kai daga gare su don kõ sũ ƙarantã ne, kuma Jahannama ce matattararsu bisa ga sãkamakon abin da suka kasance sunã tsirfatãwa.
96Sunã rantsuwã gare ku dõmin ku yarda da su. To, idan kun yarda da su, to, lalle ne Allah bã shi yarda da mutãne fãsiƙai.
97Ƙauyãwã ne mafi tsananin(1) kãfirci da munãfinci, kuma sũne mafi kamanta ga, rashin sanin haddõjin abin da Allah Ya saukar a kan ManzonSa. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
98Kuma daga ƙauyãwã akwai waɗanda(2) suke riƙon abin da suke ciyarwa a kan tãra ce, kuma sunã saurãron aukuwar masĩfa a gare ku, aukuwar mummunar masĩfa ta tabbata a kansu. Kuma Allah ne Mai ji, Masani.
99Kuma daga ƙauyãwã akawi waɗanda suke yin ĩmanida Allah da Rãnar Lãhira, kuma sunã riƙon abin da suke ciyarwa (tamkar) waɗansu ibãdõdin nħman kusanta ne a wurin Allah da addu´õ´in ManzonSa. To, lalle ne ita (ciyarwar nan) ibãdar nħman kusanta ce a gare su. Allah zai shigar da su a cikin RahamarSa. Lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.
100Kuma mãsu tsħrħwa(1) na farko daga Muhãjirina da Ansar da waɗanda suka bi su da kyautatãwa, Allah Ya yarda daga gare su su kuma sun yarda daga gare Shi, kuma Ya yi mãsu tattalin gidãjen Aljanna; Ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, suna madawwamã a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma.
101Kuma daga waɗanda suke a għfenku daga ƙauyãwa akwai munãfukai,(2) haka kuma daga mutãnen Madnĩa. Sun gõge a kan munãfunci, bã ka sanin su, Mũ ne Muke sanin su. zã Mu yi musu azãba sau biyu, sa´an nan a mayar da su zuwa ga azãba mai girma.
102Kuma da waɗansu, sun yi furuci(3) da laifinsu, sun haɗa aiki na ƙwarai da wani mummuna. Akwai tsammãnin Allah Ya karɓi tũba a kansu. Lallai Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.
103Ka karɓi sadaka daga dũkiyõyinsu kana tsarkake su, kuma kana tabbatar da kirkinsu da ita. Kuma ka yi musu addu´a. Lallai addu´õ´inKa natsuwã ne a gare su. Kuma Allah ne Mai ji, Masani.
104Shin, ba su sani ba cħwa lallai Allah, ne Yake karɓar tũbã daga bãyinSa, kuma Yanã karɓar sadakõkinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai?
105Kuma ka ce: "Ku yi aiki, sa´an nan Allah zai ga aikinku, da ManzonSa da Muminai kuma zã a mayar da ku zuwa ga masanin fake da bayyane, sa´an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
106Kuma da waɗansu waɗanda(4) aka jinkirtar ga umurnin Allah, kõ dai Ya yi musu azãba kõ kuma Ya karɓi tũba a kansu.Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
107Kuma waɗanda(1) suka riƙi wani masallãci dõmin cũta da kãfirci da nħman rarrabħwa a tsakãnin muminai da fakħwã ga taimakon wanda ya yãƙi Allah da ManzonSa daga gabãni, kuma haƙĩƙa sunã yin rantsuwa cħwa, "Ba mu yi nufin kõmai ba fãce alhħri", alhãli kuwa Allah Yanã yin shaida cħwa,su, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
108Kada ka tsaya a cikinsa har abada. Lalle ne, Masallaci wanda aka yi harsãshinsa a kan taƙawa tun farkon yini, shĩ ne mafi cancantar ka tsaya a cikinsa. A cikinsa akwai waɗansu maza sunã son su tsarkaka. (2) Kuma Allah Yanã son mãsu nħman tsarkakuwa.
109Shin, wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan taƙawa daga Allah da yarda, shi ne mafi alhħri kõ kuwa wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan gãɓar rãmi mai tusgãwa? Sai ya rũsa da shi a cikin wutar Jahannama. Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai.
110Gininsu, wanda suka gina, bã zai gushe ba Yanã abin shakka a cikin zukãtansu fãce idan zukãtansu sun yanyanke. Kuma Allah ne Masani, Mai Hikima.
111Lalle ne, Allah Ya saya(3) daga mummunai, rãyukansu da dũkiyõyinsu, da cħwa sunã da Aljanna, sunã yin yãƙi a cikin hanyar Allah, sabõda haka sunã kashħwa anã kashħ su. (Allah Yã yi)wa´adi a kanSa, tabbace a cikin Attaura da Linjĩla da Alƙur´ãni. Kuma wãne ne mafi cikãwa da alkawarinsa daga Allah? Sabõda haka ku yi bushãra da cinikinku wanda kuka ƙulla da Shi. Kuma wancan shi ne babban rabo, mai girma.
112Mãsu(1) tũba, mãsu bautãwa, mãsu gõdħwa, mãsu tafiya, mãsu ruku´i, mãsu sujada mãsu umurni da alhħri da mãsu hani daga abin da aka ƙi da mãsu tsarħwã ga iyãkõkin Allah. Kuma ka bãyar da bushãra ga muminai.
113Bã ya kasancħwa(2) ga Annabi da waɗanda suka yi ĩmãni, su yi istigifãri ga mushirikai, kuma kõ dã sun kasance ma´abũta zumunta ne daga bãyan sun bayyana a gare su, cħwa lalle ne, sũ, ´yan Jahĩm ne.
114Kuma istigifãrin Ibrãhĩm ga ubansa bai kasance ba fãce sabõda wani wa´adi ne da ya ƙulla alƙawarinsa da shi, sa´an nan a lõkacin da ya bayyana a gare shi (Ibrãhĩm) cħwa lalle ne shĩ (ubansa) maƙiyi ne ga Allah, sai ya barranta daga gare shi. Lalle ne Ibrahim, haƙĩƙa, mai yawan addu´a ne, mai haƙuri.
115Kuma Allah bai kasance mai ɓatar da mutãne a bãyan Yã shiryar da su ba, sai Ya bayyanã musu abin da zã su yi taƙawa da shi. Lalle ne Allah, ga kõme, Masani ne.
116Lalle ne Allah Yanã(3) da mulkin sammai da ƙasa, Yanã rãyarwa kuma Yanã matarwa. Kuma bã ku da wani masõyi, kuma bã ku da mataimaki, baicin Allah.
117Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Ya karɓi tũbar Annabi da(4) Muh?jirĩna da Ans?r waɗanda suka bĩ shi, a cikin s?´ar tsanani, daga b?ya zuk?tan wani ɓangare daga gare su sun yi kusa su karkata, sa´an nan ( Allah) Ya karɓi tũbarsu. Lalle, Shĩ ne Mai tausayi, Mai jin ƙai gare su.
118Kuma (Allah) Yã karɓi tũba a kan ukun(1) nan waɗanda aka jinkirtar har ƙasa da yalwarta ta yi ƙunci a kansu, kuma rãyukansu suka yi ƙunci a kansu, kuma suka yi zaton bãbu wata mafakã daga Allah fãce (kõmãwa) zuwa gare Shi. Sa´an nan Allah Ya karɓi tũbarsu, dõmin su tabbata a kan tũba. Lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
119Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku kasance tãre da mãsu gaskiya.
120Bã ya kasancħwa(2) ga mutãnen Madĩna da wanda yake a għfensu, daga ƙauyãwã, su sãba daga bin Manzon Allah, kuma kada su yi gudu da rãyukansu daga ransa. Wancan, sabõda ƙishirwa bã ta sãmun su, haka kuma wata wahala, haka kuma wata yunwa, a cikin hanyar Allah, kuma bã su tãkin wani matãki wanda yake takaitar da kãfirai kuma bã su sãmun wani sãmu daga maƙiyi fãce an rubuta musu da shi, lãdar aiki na ƙwarai. Lallai ne Allah bã Ya tõzarta lãdar mãsu kyautatãwa.
121Kuma bã su ciyar da wata ciyarwa, ƙarama kõ babba, kuma bã su kħta wani rafi sai an rubutã musu, dõmin Allah Ya sãka musu da mafi kyãwon abin da suka kasance sunã aikatãwa.
122Kuma bã ya kasancħwã ga muminai su fita zuwa yãƙi gabã ɗaya.(3) Sabõda haka, don me ne wata jama´a daga kowane ɓangare daga gare su ba ta fita (zuwa nħman ilimi ba) dõmin su nħmi ilimi ga fahimtar addĩni kuma dõmin su yi gargaɗi ga mutãnensu idan sun kõma zuwa gare su, tsammãninsu, sunã yin sauna?
123Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yãƙi waɗanda suke kusantar(1) ku daga kãfirai. Kuma su sami tsanani daga gare ku. Kuma ku sani cħwa Allah Yanã tãre da mãsu taƙawa.
124Kuma idan aka saukar(2) da wata sũra, to, daga gare su akwai waɗanda suke cħwa: "Wãne ne a cikinku wannan sũra ta ƙãra masa ĩmãni?" To amma waɗanda suka yi ĩmãni, to, ta ƙara musu imani, kuma sũ, sunã yin bushãra (da ita).
125Amma kuma waɗanda suke a cikin zukãtansu akwai cũta, to, tã ƙãra musu ƙazanta zuwa ga ƙazantarsu, kuma su mutu alhãlin kuwa sunã kãfirai.
126Shin, bã su ganin cħwa anã fitinar su a cikin kõwace shħkara: sau ɗaya kõ kuwa sau biyu, sa´an nan kuma bã su tũba, kuma ba su zama sunã tunãni ba?
127"Kuma idan haƙĩƙa, aka saukar da wata sũra, sai sãshensu ya yi dũbi zuwa ga wani sãshe, (su ce): "Shin, wani mutum yanã ganin ku?" Sa´an nan kuma sai su jũya. Allah Ya jũyar da zukãtansu, dõmin, haƙĩƙa sũ mutãne ne, bã su fahimta.
128Lalle ne, haƙĩƙa, Manzo(3) daga cikinku yã je muku. Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwaɗayi ne sabõda ku. Ga muminai Mai tausayi ne, Mai jin ƙai.
129To, idan sun jũya, sai ka ce: Ma´ishĩna Allah ne. Bãbu abin bautãwa fãce shi. A gare Shi nake dõgara. Kuma Shi ne Ubangijin Al´arshi mai girma.
Chapter 10 (Sura 10)
1A. L̃. R. Waɗancan ãyõyin littãfi ne kyautatacce.
2Shin, yã zama abin mãmaki ga mutãne dõmin Mun yi wahayi zuwa ga wani namiji daga gare su cħwa, "Ka yi gargaɗi ga mutãne kuma ka yi bushãra ga waɗanda suka yi ĩmãni da cħwa: Lalle ne sunã da abin gabãtarwar gaskiya a wurin Ubangijinsu."Kãfirai suka ce: "Lalle ne wannan, haƙĩƙa, masihirci ne bayyananne."
3Lalle Allah ne Ubangijinku wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwãna shida, sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi Yanã gudãnar da al´amari. Bãbu wani macħci fãce a bayan izninSa. Wannan ne Allah, Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Shin fa, ba ku tunãni?
4Zuwa gare Shi makõmarku take gabã ɗaya, wa´adin Allah gaskiya ne. Haƙĩƙa, Shi ne Yake fara halitta, sa´an nan kuma Ya mayar da ita dõmin Ya sãka wa waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai da ãdalci, kuma waɗanda suka kãfirta sunã da abin sha daga ruwan zãfi, da azãba mai raɗaɗi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci.
5Shĩ ne wanda Ya sanya muku rãnã, babban haske, da watã mai haske, kuma Ya ƙaddara shi ga Manzilõli, dõmin ku san ƙidãyar shħkaru da lissãfi. Allah bai halitta wannan ba, fãce da gaskiya, Yanã bayyana ãyõyi daki-daki dõmin mutãne waɗanda suke sani.
6Lalle ne a cikin sãɓãwar dare da yini, da abin da Allah Ya halitta a cikin sammai da ƙasa, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin taƙawa.
7Lalle ne waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mũ, kuma suka yarda da rãyuwar dũniya kuma suka natsu da ita, da waɗanda suke gafalallu ne daga ãyõyinMu,
8Waɗannan matattãrarsu Jahannama ce sabõda abin da suka kasance sunã tsirfãtawa.
9Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, Ubangijinsu Yanã shiryar da su sabõda ĩmãninsu, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, a cikin gidãjen Aljannar ni´ima.
10Kiransu a cikinta, "TsarkinKa yã Allah!" Kuma gaisuwarsu a cikinta,"Salãmun", kuma ƙarshen kiransu, cħwa, "Gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu."
11Kuma dã Allah Yana gaggãwa ga mutãne da sharri kamar yadda Yake gaggauta musu da alhħri, haƙĩƙa dã an hukunta ajalinsu zuwa gare su. Sabõda haka Munã barin waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mu, a cikin kangararsu sunã ta ɗimuwa.
12Kuma idan cũta ta shãfi mutum, sai ya kirãye Mu, yanã (kwance) ga sãshensa kõ kuwa zaune, kõ kuwa a tsaye. To, a lõkacin, da Muka kuranye cũtar daga gare shi, sai ya shũɗe kamar ɗai bai kirãye Mu ba zuwa ga wata cũta wadda ta shãfe shi. Kamar wannan ne aka ƙawãta ga maɓannata, abin da suka kasance sunã aikatãwa.
13Kuma, haƙĩƙa, Mun halakar da al´ummomi daga gabãninku, a lõkacin da suka yi zãlunci, kuma manzanninsu suka jħ musu da hujjõji bayyanannu, amma ba su kasance sunã ĩmãni ba. Kamar wannan ne, Muke sãkãwa ga mutãne mãsu laifi.
14Sa´an nan kuma Muka sanya ku mãsu mayħwa a cikin ƙasa daga bãyansu, dõmin Mu ga yãya kuke aikatãwa.
15Kuma idan anã karatun ãyõyĩnMu bayyanannu a kansu, sai waɗanda bã su ƙaunar gamuwa da Mu, su ce: "Ka zo da wani Alƙur´ãni, wanin wannan, ko kuwa ka musunyã shi."(1) Ka ce: "Bã ya kasancħwa a gare ni in musanyã shi da kaina. Bã ni biyar kõme fãce abin da aka yiwo wahayi zuwa gare ni. Kuma, haƙĩƙa ni inã tsõro idan na sãɓã wa Ubangijina, ga azãbar wani yini mai girma."
16Ka ce: "Dã Allah Ya so dã ban karanta shi ba a kanku, kuma dã ban sanar da kũ ba gameda shi, dõmin lalle ne nã zauna a cikinku a zãmani mai tsawo daga gabãnin (fãra saukar) sa. Shin fa, bã ku hankalta?"
17"Sabõda haka wãne ne mafi Zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata ãyõyinSa? Haƙĩƙa, mãsu laifi bã su cin nasara!"
18Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da bã ya cũtar dasu kuma bã ya amfãninsu, kuma sunã cħwa: "Waɗannan ne macħtanmu a wurin Allah."Ka ce: "Shin, kunã bai wa Allah lãbãri ne, ga abin da bai sani ba, a cikin sammai ko a cikin ƙasa? TsarkinSa ya tabbata kuma Yã ɗaukaka daga abin da duk suke yin shirki da Shi."
19Kuma mutãne ba su kasance ba fãce al´umma guda, sa´an nan kuma suka sãɓã wa jũna, kuma ba dõmin wata kalma ba wadda ta gabãta daga Ubangijinka, dã an yi hukunci a tsakãninsu a kan abin da yake a cikinsa suke sãɓã wa jũna.
20Kuma sunã cħwa: "Don me ba a saukar da wata ãyã ba a gare shi, daga Ubangijinsa?" To, ka ce: "Abin sani kawai, gaibi ga Allah yake. Sai ku yi jira. Lalle ne nĩ, tãre da ku, inã daga mãsu jira."
21Kuma idan Muka ɗanɗanã wa mutãne wata rahama, a bãyan wata cũta tã shãfe su, sai gã su da mãkirci a cikin ãyõyinMu. Ka ce: "Allah ne mafi gaggãwar (sakamakon) mãkirci." Lalle ne ManzanninMu sunã rubũta abin da kuke yi na mãkirci.
22Shĩ ne wanda Yake tafiyar da ku a cikin tudu da (kuma) tħku, sai idan kun kasance a cikin jirãge, su gudãna tãre da su da iska mai dãɗi, kuma su yi farin ciki da ita, sai wata gũguwa ta je wa jirãgen, kuma tãguwar ruwa ta jħ musu daga kõwane wuri, kuma su tabbata cħwa sũ, an kħwaye su, sai su kirãyi Allah, sunã mãsu tsarkake addini gare Shi, (sunã cħwa): Lalle ne idan Ka kuɓutar da mu daga wannan, haƙĩƙa munã kasancħwa daga mãsu gõdiya.
23To, a lõkacin da Ya kuɓutar da su, sai, gã su sunã zãlunci a cikin ƙasa, bã da wanĩ hakki ba. Yã ku mutãne! Abin sani kawai, zãluncinku a kanku yake, a bisa rãyuwar dũniya. Sa´an nan kuma zuwa gare Mu makõmarku take, sa´an nan Mu bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa,
24Abin sani kawai, misãlin rãyuwar dũniya kamar ruwa ne Muka saukar da shi daga sama, sa´an nan tsiron ƙasa ya garwaya da shi. Daga abin da mutãne da dabbõbi suke ci, har idan ƙasa ta riƙi zinãriyarta kuma ta yi ƙawa, kuma mutãnenta suka zaci cħwa sũ ne mãsu ĩkon yi a kanta, sai umurninMu ya je mata da dare kõ kuma da rãna, sai Mu maishħta girbabba kamar ba ta wadãta ba a jiya. Kamar wannan ne Muke rarrabe ãyõyi, daki-daki, ga mutãne waɗanda suke tunãni.
25Kuma Allah Yanã kira zuwa ga gidan aminci, kuma, Yanã shiryar da wanda Yake so zuwa ga tafarki madaidaici.
26Waɗanda suka kyautata yi, sunã da abu mai kyãwo kuma da ƙari,(1) wata ƙũra bã ta rufe fuskõkinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. Waɗancan ne abokan Aljanna, sunã madawwama a cikinta.
27Kuma waɗanda suka yi tsirfar mũnanan ayyuka, sakamakon mummuna da kamarsa yake, kuma ƙasƙanci yanã rufe su. Bã su da wani matsari daga Allah, kamar an rufe fuskokinsu da guntãyen ƙirãruwa daga dare mai duhu. Waɗannan ne abõkan wuta, sunã madawwama a cikinta.
28Kuma a rãnar da Muke tãra su gabã ɗaya, sa´an nan kuma Mu ce wa waɗanda suka yi shirki, "Ku kãma matsayinku, kũ da abũbuwan shirkĩnku." Sa´an nan Mu rarrabe a tsakãninsu, kuma abũbuwan shirkinsu su ce: "Bã mũ kuka kasance kunã bauta wa ba."
29"To, kuma Allah Yã isa zama shaida a tsakãninmu da tsakãninku. Haƙĩƙa mun kasance ba mu san kõme ba na bautãwarku a gare mu!"
30A can ne kõwane rai yake jarraba abin da ya bãyar bãshi, kuma aka mayar da su zuwa ga Allah, Majiɓincinsu Tabbatacce kuma, abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa ya ɓace musu.
31Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al´amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?"
32To, Wancan ne Allah, Ubangijinku Tabbatacce. To, mħne ne a bãyan gaskiya fãce ɓãta? To, yãya ake karkatar da ku?
33Kamar wancan ne kalmar Ubangijinka, ta tabbata a kan waɗanda suka yi fãsiƙanci, cħwa haƙĩƙa sũ, bã zã su yi ĩmãni ba.
34Ka ce: "Shin, daga abũbuwan shirkinku akwai wanda yake fãra halitta, sa´an nan kuma ya mayar da ita?" Ka ce: "Allah ne Yake fãra halitta, sa´an nan kuma Ya mayar da ita. To, yãyã ake jũyar da ku?"
35Ka ce: "Shin, daga abũbuwan shirkinku akwai wanda yake shiryarwa zuwa ga gaskiya?" Ka ce: "Allah ne Yake shiryarwa zuwa ga gaskiya. Shin fa, wanda Yake shiryarwa ne mafi cancantar a bi Shi, ko kuwa wanda bã ya shiryarwa fãce dai a shiryar da shi? To, mħne ne a gare ku? Yãya kuke yin hukunci?"
36Kuma mafi yawansu bã su biyar kõme fãce zato. Lalle ne zato bã ya wadãtar da kõme daga gaskiya. Lalle Allah ne Masani ga abin da suke aikatãwa.
37Kuma wannan Alƙur´ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake.
38Kõ sunã cħwa, "Yã ƙirƙira shi?" Ka ce: "Ku zo da sũra guda misãlinsa, kuma ku kirãyi wanda kuka iya duka, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya."
39ôa, sun ƙaryata game da abin da ba su kħwaye da saninsa ba, kuma fassararsa ba ta riga ta jħ musu ba. Kamar waɗancan ne waɗanda suke a gabãninsu. Sai ka dũba, yãya ãƙibar azzãlumai ta kasance?
40Kuma daga cikinsu akwai wanda yake yin ĩmãni da Shi, kuma daga cikinsu akwai wanda bã ya yin ĩmãni da Shi. Kuma Ubangijinka ne Mafi sani ga maɓarnata.
41Kuma idan sun ƙaryata ka, to, ka ce: "Inã da aikĩna kuma kunã da aikinku, kũ kuɓutattu ne daga abin da nake aikatãwa kuma ni kuɓutacce ne daga abin da kuke aikatãwa."
42Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke saurare zuwa gare ka. Shin fa, kai kana jiyar da kurma, kuma kõ dã sun kasance bã su hankalta?
43Kuma daga cikinsu akwai wanda yake tsõkaci zuwa gare ka. Shin fa, kai kana shiryar da makãfi, kuma kõ dã sun kasance bã su gani?
44Lalle ne Allah ba Ya zãluntar mutãne da kõme, amma mutãnen ne ke zãluntar kansu.
45Kuma rãnar da Yake tãra su, kamar ba su zauna ba fãce sa´a guda daga yini. Sunã gãne jũna a tsakãninsu. Haƙĩƙa, waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasãra. Kuma ba su kasance mãsu shiryuwa ba.
46Kuma imma dai, haƙĩƙa, Mu nũna maka sãshen abin da Muke yi musu alkawari, kõ kuwa Mu karɓi ranka, to, zuwa gare Mu makõmarsu take. Sa´an nan kuma Allah ne shaida a kan abin da suke aikatãwa.
47Kuma ga kõwace al´umma akwai Manzo.(1) Sa´an nan idan Manzonsu ya je, sai a yi hukunci a tsakãninsu da ãdalci, kuma sũ, bã a zãluntar su.
48Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi zai auku, idan kun kasance mãsu gaskiya?"
49Ka ce: "Ba na mallaka wa kaina wata cũta, haka kuma wani amfãni, sai abin da Allah Ya so. Ga kõwace al´umma akwai ajali, idan ajalinsu ya zo, to, bã zã su yi jinkiri daga gare shi ba, kõ dã sã´ã guda, kuma bã zã su gabãta ba."
50Ka ce: "Shin, kun gani, idan azãbarSa ta zo muku da dare ko da rãna? Mħne ne daga gare shi mãsu laifi suke nħman gaggãwarsa?"
51Shin sa´an nan kuma idan har ya auku, kun yi ĩmãni da shi? Ashe? Yanzu kuwa, alhãli kun kasance game da shi kunã nħman gaggãwar aukuwarsa?
52Sa´an nan kuma aka ce ga waɗanda suka yi zãlunci, "Ku ɗanɗani azãbar dawwama! Shin, anã sãka muku fãce da abin da kuka kasance kuna aikatãwa?"
53Kuma sunã tambayar ka: Shin gaskiya ne? Ka ce: "Ĩ, ina rantsuwa da Ubangijĩna. Lalle gaskiya ne, kuma ba ku zama mãsu buwãya ba."
54Kuma dã kõwane rai wanda ya yi zãlunci yã mallaki duka abin da yake a cikin ƙasa, to, dã yã yi fansa da shi. Kuma suka dinga nadãma a lõkacin da suka ga azãba. Sa´an nan aka yi hukunci a tsakãninsu da ãdalci, kuma bã zã a zãlunce su ba.
55To! Haƙĩƙa Allah Ya mallaki abin da yake a cikin sammai da ƙasa. To! Haƙĩƙa wa´adin Allah gaskiya ne. Amma kuma mafi yawansu ba su sani ba.
56Shi ne Yake rãyarwa kuma Yake matarwa. Kuma zuwa gare Shi ne ake mayar da ku.
57Ya ku mutãne! Lalle wa´azi yã jħ muku daga Ubangijinku, da waraka ga abin da yake a cikin ƙirãza, da shiriya da rahama ga muminai.
58Ka ce: "Da falalar Allah da rahamarSa. Sai su yi farin ciki da wannan." Shĩ ne mafi alhħri daga abin da suke tãrãwa.
59Ka ce: "Shin, kun ga abin da Allah Ya saukar sabõda ku na arziki, sai kuka sanya hukuncin haramci da halacci a gare shi?" Ka ce: "Shin, Allah ne Ya yi muku izni, ko ga Allah kuke ƙirƙirãwar ƙarya?"
60Kuma mħne ne zaton waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, a Rãnar Ƙiyãma? Lalle haƙĩƙa, Allah Ma, abũcin falala ne a kan mutãne, amma kuma mafi yawansu bã su gõdħwa.
61Kuma ba ka kasance a cikin wani sha´ani ba, kuma ba ka karanta wani abin karatu daga gare shi ba, kuma ba ku aikata wani aiki ba, fãce Mun kasance Halarce a lõkacin da kuke zubuwa a cikinsa. Kuma wani ma´aunin zarra bã zai yi nĩsa ba daga Ubangijinka a cikin ƙasa, haka kuma a cikin sama, kuma bãbu wanda yake mafi ƙaranci daga haka, kuma bãbu mafi girma, fãce yana a cikin littãfi bayyananne.
62To, Lalle ne masõyan(1) Allah bãbu tsõro a kansu, kuma bã zã su kasance sunã yin baƙin ciki ba.
63Waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka kasance sunã yin taƙawa.
64Sunã da bushãra a cikin rãyuwar dũniya da ta Lãhira.Bãbu musanyãwa ga kalmõmin Allah. Wancan shi ne babban rabo mai girma,
65Kada maganarsu(2) ta sanya ka a cikin baƙin ciki. Lalle ne alfarma ga Allah take gaba ɗaya. Shi ne Mai jĩ, Masani.
66To! Haƙĩƙa Allah Yanã da mulkin wanda ke a cikin sammai da wanda ke a cikin ƙasa kuma waɗanda suke kiran wanin Allah, bã su biyar waɗansu abõkan tarħwa (ga Allah a MulkinSa). Bã su biyar kõme fãce zato. Kuma ba su zama ba fãce sunã ƙiri faɗi kawai.
67Shĩ ne wanda Ya sanya muku dare, dõmin ku natsu a cikinsa, da yini mai sanya a yi gani. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda sukħ ji.
68Suka ce: "Allah Ya riƙi ɗa." Tsarkinsa yã tabbata! Shi ne wadãtacce Yanã da mallakar abin da yake, a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, A wurinku bãbu wani dalĩli game da wannan! Shin, kunã faɗar abin da ba ku sani ba game da Allah?
69Ka ce: "Haƙĩƙa waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, bã zã su ci nasara ba."
70Jin dãɗi ne a cikin dũniya, sa´an nan kuma makõmarsu zuwa gare Mu take, sa´an nan Mu ɗanɗana musu azãba mai tsanani sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci.
71Kuma ka karanta musu lãbãrin Nũhu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Ya mutãnħna! Idan matsayĩna da tunãtarwata ame da ãyõyin Allah sun kasance sun yi nauyi a kanku, to, ga Allah na dõgara. Sai ku tãra al´amarinku, kũ da abũbuwan shirkinku, sa´annan kuma kada al´amarinku ya kasance rufaffe a kanku, sa´an nan kuma ku kashe ni, kada ku yi mini jinkiri."
72"Kuma idan kuka jũya bãya, to, ban tambaye ku wata ijãra ba. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Allah, kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu sallamãwa."(1)
73Sai suka ƙaryata shi, sa´an nan Muka kuɓutar da shi da wanda yake tãre da shi, a cikin jirgi, kuma Muka sanya su mãsu mayħwa, kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata ãyõyinMu. Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
74Sa´an nan kuma Muka aika waɗansu Manzanni daga bãyansa zuwa ga mutãnensu, suka jħmusu da hujjõji bayyanannu, to, ba su kasance zã su yi ĩmãni ba sabõda sun ƙaryata shi a gabani. Kamar wannan ne Muke rufħwa a kan zukãtan mãsu ta´addi.
75Sa´an nan kuma a bãyansu Muka aika Mũsa da Hãrũna zuwa ga Fir´auna da mashãwartansa, tãre da ãyõyinMu. Sai suka kangara kuma sun kasance mutãne mãsu laifi.
76Sa´an nan a lõkacin da gaskiya ta jħ musu daga gare Mu, suka ce: "Wannan haƙĩƙa sihiri ne bayyananne."
77Mũsã ya ce: " Shin, kunã cħwa ga gaskiya a lõkacin data zo muku? Shin, sihiri ne wannan? Lalle masihirci, bã ya cin nasara."
78Suka ce: "Shin, ka zo mana ne dõmin ka jũyar da mu daga abin da muka iske ubanninmu a kansa, kuma girma ya kasance gare ku, ku biyu a cikin ƙasa? Bã zã mu zama mãsu ĩmãni ba sabõda ku."
79Kuma Fir´auna ya ce: "Ku zo mini da dukan masihirci, masani."
80To, a lõkacin da masihirta suka je, Mũsã ya ce musu,"Ku jħfa abin da kuke jħfãwa."
81To, a lõkacin da suka jħfa, Mũsa ya ce: "Abin da kuka zo da shi sihiri ne. Lalle ne Allah zai ɓãta shi. Haƙĩƙa Allah bã Ya gyãra aikin maɓarnata.
82"Kuma Allah Yanã tabbatar da gaskiya da kalmõminSa, kõ dã mãsu laifi sun ƙi."
83Sa´an nan bãbu wanda ya yi ĩmãni da Mũsa fãce zuriya daga mutãnensa, a kan tsõron kada Fir´auna da shũgabanninsu su fitinħ su. Lalle, haƙĩƙa, Fir´auna marinjãyi ne a cikin ƙasa, kuma lalle shĩ haƙĩƙa, yanã daga mãsu ɓarna.
84Kuma Mũsã ya ce: "Yã kũ mutãnena! Idan kun kasance kun yi ĩmãni da Allah, to, a gare Shi sai ku dõgara, idan kun kasance Musulmi."
85Sai suka ce: "Ga Allah muka dõgara. Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanyã mu fitina ga mutãne azzãlumai.
86"Kuma Ka kuɓutar da mu dõmin RahamarKa, daga mutãne kãfirai."
87Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã da ɗan´uwansa, cħwa: Kũ biyu, ku zaunar da mutãnenku a Masar a cikin wasu gidãje. Kuma ku sanya gidãjenku su fuskanci Alƙibla(1) , kuma ku tsayar da salla. Kuma ku bãyar da bushãra ga mãsu ĩmãni.
88Sai MũSã ya ce: "Yã Ubangijinmu! Haƙĩƙa Kai ne Ka bai wa Fir´auna da majalisarsa ƙawa da dũkiyõyi a cikin rãyuwar dũniya, yã Ubangijinmu, dõmin su ɓatar (da mutãne) daga hanyarKa. Yã Ubangijinmu! Ka shãfe a kan dũkiyarsu kuma Ka yi ɗauri(2) a kan zukãtansu yadda bã zã su yi ĩmãni ba har su ga azãba mai raɗaɗi."
89(Allah) Yã ce: "Lalle ne an karɓi addu´arku. Sai ku daidaitu kuma kada ku bi hanyar waɗanda ba su sani ba."
90Kuma Muka ƙħtãrar da Banĩ Isrã´ila tħku sai Fir´auna da rundunarsa suka bĩ su bisa ga zãlunci da ƙħtare haddi, har a lõkacin da nutsħwa ta riske shi ya ce: "Nã yi(1) ĩmãni cħwa, haƙĩƙa, bãbu abin bautawa fãce wannan da Banũ Isrã´il suka yi ĩmãni da Shi, kumanĩ, ina daga Musulmi."
91Ashe! A yanzu! Alhãli kuwa, haƙĩƙa ka sãɓa a gabãni, kuma ka kasance daga mãsu ɓarna?
92To, a yau Munã kuɓutar(2) da kai game da jikinka, dõmin ka kasance ãyã ga waɗanda suke a bãyanka. Kuma lalle ne mãsu yawa daga mutãne, haƙĩƙa, gafalallu ne ga ãyõyinMu.
93Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun zaunar(3) da Banĩ Isrã´ila mazaunar gaskiya kuma Muka arzũta su daga abũbuwa mãsu dãɗi. Sa´an nan ba su sãɓa ba har ilmi ya jħ musu. Lalle ne Ubangijinka Yanã yin hukunci a tsakãninsu a Rãnar Kiyãma a cikin abin da suka kasance sunã sãɓa wa jũna.
94To, idan ka kasance a cikin shakka daga abin da Muka saukar zuwa gare ka, sai ka tambayi waɗanda suke karatun Littãfi daga gabaninka. Lalle ne, haƙĩƙa, gaskiya tã jħ maka daga Ubangijinka dõmin haka kada ka kasance daga mãsu kõkanto.
95Kuma kada ka kasance daga waɗanda suke ƙaryatãwa game da ãyõyin Allah, har ka kasance daga mãsu hasãra.
96Lalle ne waɗanda kalmar Ubangijinka ta wajaba a kansu, bã zã su yi ĩmãni ba.
97Kuma kõ dã kõwace ãyã ta jħ musu, sai sun ga azãba mai raɗaɗi.
98To, dõmin me wata alƙarya ba ta kasance ta yi(1) ĩmãni ba har ĩmãninta ya amfãne ta, fãce mutãnen Yũnus? A lõkacin da suka yi ĩmãni, Mun janye azãbar wulãkanci daga gare su a cikin rãyuwar dũniya. Kuma Muka jiyar da su dãɗi zuwa wani lõkaci.
99Kuma dã Ubangijinka Ya so, dã waɗanda suke a cikin ƙasa sun yi ĩmãni dukansu gabã ɗaya. Shin, kai kanã tĩlasta mutãne ne har su kasance mãsu ĩmãni?
100Kuma ba ya kasancħwa ga wani rai ya yi ĩmãni fãce da iznin Allah, kuma (Allah) Yanã sanya ƙazanta a kan wa ɗanda bã su yin hankali.
101Ka ce: "Ku dũbi abin da yake cikin sammai da ƙasa."Kuma ãyõyi da gargaɗi bã su wadãtarwa ga mutãne waɗanda bã su yin ĩmãni.
102To, Shin sunã jiran wani abu fãce kamar misãlin kwãnukan waɗanda suka shũɗe daga gabãninsu? Ka ce: "Ku yi jira! Lalle nĩ tãre da ku, inã daga mãsu jira."
103Sa´an nan kuma Munã kuɓutar da manzanninMu da waɗanda suka yi ĩmãni, kamar wannan ne, tabbatacce ne a gare Mu, Mu kuɓutar da mãsu ĩmãni.
104Ka ce: "Yã kũ mutãne! Idan kun kasance a cikin kõkanto daga addinĩna, to bã ni bauta wa,waɗanda kuke, bautã wa, baicin Allah, kuma amma ina bauta wa Allah wanda Yake karɓar rãyukanku. Kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu ĩmãni."
105"Kuma (an ce mini ): Ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã karkata zuwa ga gaskiya, kuma kada ka kasance daga mãsu shirka.
106"Kuma kada ka kirãyi, baicin Allah, abin da bã ya amfãnin ka kuma bã ya cũtar ka. To, idan ka aikata haka, sa´an nan lalle kai, a lõkacin, kanã daga mãsu zãlunci."
107Kuma idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, bãbu mai yãyħ ta fãce shi, kuma idan Yanã nufin ka da wani alhħri, to, bãbu mai mayar da falalarSa. Yanã sãmun wanda Yake so daga cikin bãyinSa da shi. Kuma Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.
108Ka ce: "Yã ku mutãne! Lalle ne gaskiya, ta zo muku daga Ubangijinku. To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai, kuma wanda ya ɓace yana ɓacewa ne a kansa kawai. Kuma ban zama wakĩli a kanku ba."
109Kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ka yi haƙuri har Allah Ya yi hukunci. Kuma Shĩ ne Mafi alhħrin mãsu hukunci.
Chapter 11 (Sura 11)
1A. L̃. R. Littãfi ne an kyautata ãyõyinsa, sa´an nan an bayyanã su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa.
2Kada ku bautã wa kõwa fãce Allah. Lalle ne ni a gare ku mai gargaɗi ne kuma mai bushãrã daga gare Shi.
3Kuma ku nħmi gãfara gun Ubangijinku. Sa´an nan ku tũba zuwa gare Shi, Ya jiyar da ku dãɗi, jiyarwa mai kyau zuwa ga ajali ambatacce, kuma Ya bai wa dukkan ma´abucin, girma girmansa. Amma idan kun jũya, to, lalle nĩ, inã tsõron azãbar yini mai girma a kanku.
4Zuwa ga Allah makõmarku take, kuma Shĩ a kan kõme Mai ĩkon yi ne.
5To, lalle sũ sunã karkatar(1) da ƙirjinsu dõmin su ɓõye daga gare shi. To, a lõkacin da suke lulluɓħwa da tufãfinsu Yanã sanin abin da suke ɓoyewa da abin da suke bayyanãwa. Lalle Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙirãzã.
6Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa fãce ga Allah arzikinta yake, kuma Yanã sanin matabbatarta(1) da ma´azarta, duka sunã cikin littãfi bayyananne.
7Kuma shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwanaki shida, kuma Al´arshinSa ya kasance akan ruwa,(2) d?min Ya jarrab? ku, wanne ne daga cikinku mafi kyãwon aiki. Kuma haƙĩƙa idan ka ce: "Lalle kũ waɗanda ake tãyarwa ne a bãyan mutuwa," haƙĩƙa waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Wannan bai zama ba fãce sihiri bayyananne."
8Kuma lalle ne idan Mun jinkirta da azãba gare su zuwa ga wani lõkaci ƙidãyayye, haƙĩƙa sunãcħwa me yake tsare(3) ta? To, a rãnar da zã ta je musu, ba ta zama abin karkatarwa ba daga gare su. Kuma abin da suka kasance suna yin izgili da shi, yã wajaba a kansu.
9Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana wa mutum wata rahama daga gare Mu, sa´an nan kuma Muka zãre ta daga gare shi, lalle ne shĩ, hakĩka, mai yanke tsammãni ne, mai yawan k?firci.
10Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana masa ni´ima a bãyan cũta ta shãfe shi, Yana cħwa mũnanan halaye sun tafi daga wurina. Lalle shi mai farin ciki ne, mai alfahari.
11Sai waɗanda suka yi haƙuri kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai. Waɗannan sunã da gãfara da lãda mai girma.
12Sabõda haka tsammãninka kai mai barin sãshen abin da aka yi wahayi zuwa gare ka ne, kuma mai ƙuntata ƙirjinka da shi ne dõmin sun ce: "Dõmin me ba a saukar masa da wata taska ba, kõ kuma Malã´ika ya zo tãre da shi?"(4) Kai mai gargaɗi ne kawai. Kuma Allah ne Wakili a kan kõme.
13Kõ sunã cewa: "Yã ƙirƙira(1) shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da sũrõri gõma misãlinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirãyi wanda kuke iyãwa, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya."
14To, idan ba su amsa muku ba, to, ku sani cħwa an saukar da shi kawai ne da sanin Allah, kuma cħwa bãbu abin bauta wa fãce Shi. To, shin, kũ mãsu sallamãwa ne?,
15Wanda ya kasance yã yi nufin rãyuwar dũniya da ƙawarta, Munã cika musu ayyukansu zuwa gare su a cikinta, kuma a cikinta bã zã a rage su ba.
16Waɗannan ne waɗanda bã su da kõme a cikin Lãhira fãce wuta, kuma abin da suka sanã´anta a cikinta (dũniya) yã ɓãci, kuma abin da suka kasance sunã aikatãwa ɓãtacce ne.
17Shin, wanda ya kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijinsa, kuma wata shaida tanã biyar sa daga gare Shi, kuma a gabãninsa akwai littãfin Mũsã abin kõyi da rahama? Waɗannan sunã yin ĩmãni da shi, kuma wanda ya kãfirta da shi daga ƙungiyõyi, to, wutã ce makõmarsa. Sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga gare shi. Lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka, amma kuma mafi yawan mutãne bã su yin ĩmãni.
18Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah? Waɗannan anã gitta su ga Ubangijinsu, kuma mãsu shaida su ce: "Waɗannan ne suka yi ƙarya ga Ubangijinsu. To, la´anar Allah ta tabbata a kan azzãlumai."
19Waɗanda suke kangħwa daga hanyar Allah kuma sunã nħman ta karkace, kuma sũ ga Lãhira sunã kãfirta.
20Waɗannan ne ba su kasance mabuwãya ba a cikin ƙasa, kuma waɗansu masõya ba su kasance ba a gare su, baicin Allah. Anã ninka musu azãba, ba su kasance sunã iya ji ba, kuma ba su kasance sunã gani ba.
21Waɗannan ne wɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirawa ya ɓace musu.
22Bãbu makawã cħwa, haƙĩƙa, sũ a lãhira, sũ ne mafi hasãra.
23Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi tawãlu´i zuwa ga Ubangijinsu, waɗannan ne abõkan Aljanna, sunã madawwama a cikinta.
24Misãlin ɓangaren biyu kamar makãho ne da kurmã, da mai gani da mai ji. Shin, sunã daidaita ga misãli? Ashe, bã ku yin tunãni?
25Kuma haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutanensa, (ya ce): "Lalle ne ni, a gare ku mai gargaɗi bayyananne ne."
26"Kada ku bautã wa kõwa fãce Allah. Lalle nĩ, inã jin tsõron azãbar yini mai raɗaɗi a kanku."
27Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta, daga mutãnensa, suka ce: "Bã mu ganin ka fãce mutum kake kamarmu, kuma ba mu ganin wani ya bĩ ka fãce waɗanda suke sũ ƙasƙantattunmu ne marasa tunani. Kuma bã mu ganin wata falalã agare ka a kanmu. ôa, Munã zaton ku maƙaryata ne."
28Ya ce: "Ya mutãnena! Shin, kun gani idan na kasance a kan wata hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Yã bã ni wata Rahama daga wurinSa, Sa´an nan aka rufe ta (ita Rahamar) daga gare ku, shin, zã mu tĩlasta muku ita, alhãli kuwa kũ mãsu ƙi gare ta ne?
29"Kuma yã mutãnena! Bã zan tambaye ku wata dũkiya ba akansa, ijãrata ba ta zama ba, fãce daga Allah, kuma ban zama mai kõrar waɗanda suka yĩ ĩmãni ba. Haƙĩƙa sũ, mãsu haɗuwa da Ubangijinsu ne, kuma amma ni, inã ganin ku mutãne ne jãhilai."
30"Kuma ya mutãnena! Wãne ne yake taimakõna daga Allah idan na kõre su? Ashe, bã ku tunãni?"
31"Kuma bã ni ce muku a wurĩna taskõkin Allah suke kuma bã inã sanin gaibi ba ne. Kuma ba inã cħwa ni Malã´ika ba ne. Kuma ba ni cħwa ga waɗanda idãnunku suke wulãkantãwa, Allah bã zai bã su alhħri ba. Allah ne Mafi sani ga abin da yake cikin zukatansu. Lalle ne ni, idan (nã yi haka) dã ina daga cikin azzalumai."
32Suka ce: "Yã Nũhu, lalle ne kã yi jayayya da mu, sa´an nan kã yawaita yi mana jidãli, to, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
33Ya ce: "Allah kawai ne Yake zo muku da shi idan Ya so. Kuma ba ku zama mabuwãya ba."
34"Kuma nasĩhãta bã zã ta amfãne ku ba, idan nã yi nufin in yi muku nasĩha, idan Allah Ya kasance Yanã nufin Ya halaka ku. Shĩ ne Ubangijinku, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku."
35Ko sunã cħwa: (Nũhu) ya ƙirƙira shi. Ka ce: "Idan nĩ (Nũhu) na ƙirƙira shi to, laifĩnã a kaina yake, kuma nĩ mai barrantã ne daga abin da kuke yi na laifi."
36Kuma aka yi wahayi zuwa ga Nũhu cħwa: Lalle ne bãbu mai yin ĩmãni daga mutãnenka fãce wanda ya riga ya yi ĩmãnin, sabõda haka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
37Kuma ka sassaƙa jirgi da kyau bisa idanunMu da wahayinMu, kuma kada ka yi Mini magana a cikin sha´anin waɗanda suka kãfirta, lalle ne sũ, waɗanda ake nutsarwa ne.
38Kuma Yanã sassaƙa jirgin cikin natsuwa, kuma a kõ yaushe waɗansu shugabanni daga mutãnensa suka shũɗe a gabansa, sai su yi izgili gare shi. Ya ce: "Idan kun yi izgili gare mu, to, haƙĩƙa mũ mã zã mu yi izgili gare ku, kamar yadda kuke yin izgili.
39"Sa´an nan da sannu zã ku san wanda azãba zã ta zo masa, ta wulakantã shi (a dũniya), kuma wata azãba zaunanna ta sauka a kansa (a Lãhira)."
40Har a lõkacin da umurninMu ya je, kuma tandã ta ɓulɓula. Muka ce: "Ka ɗauka, a cikinta, daga kõme, ma´aura biyu, da kuma iyalanka, fãce wanda magana ta gabãta a kansa,(1) da wanda ya yi ĩmãni." Amma kuma bãbu waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi fãce kaɗan."
41Kuma ya ce: "Ku hau a cikinta, da sũnan Allah magudãnarta da matabbatarta. Lalle ne Ubangijĩna, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai."
42Kuma ita tanã gudãna da su a cikin tãguwar ruwa kamai duwãtsu, sai Nũhu ya kirãyi ɗansa alhãli, kuwa ya kasance can wuri mai nĩsa. "Yã ƙaramin ɗãnã! zo ka hau tãre da mu, kuma kada ka kasance tãre da kãfirai!"
43Ya ce: "Zan tattara zuwa ga wani dũtse ya tsare ni daga ruwan." (Nũhu) ya ce: "Bãbu mai tsarħwa a yau daga umurnin Allah fãce wanda Ya yi wa rahama." Sai taguwar ruwa ta shãmakace a tsakãninsu, sai ya kasance daga waɗanda aka nutsar.
44Kuma aka ce: "Yã ƙasa! Ki haɗiye ruwanki, kuma yã sama! Ki kãme."Kuma aka faƙar da ruwan kuma aka hukunta al´amarin, kuma Jirgin ya daidaita a kan Jũdiyyi, (2) kuma aka ce: "Nĩsa ya tabbata ga mutãne azzãlumai."
45Kuma Nũhu ya kira Ubangijinsa, sa´an nan ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne ɗãna na daga iyãlĩna! Kuma haƙĩƙa wa´adinKa gaskiya ne, kuma Kai ne Mafi hukuncin mãsu yin hukunci."
46Ya ce: "Yã Nũhu! Lalle ne shi bã ya a ciki iyãlanka, lalle ne shĩ, aiki ne wanda ba na ƙwarai ba, sabõda haka kada ka tambaye Ni abin da bã ka da ilmi a kansa. Haƙĩƙa, Nĩ Inã yi maka gargaɗi kada ka kasance daga jãhilai."
47Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, inã nħman tsari gare Ka da in tambaye Ka abin da bã ni da wani ilmi a kansa. Idan ba Ka gãfarta mini ba, kuma Ka yi mini rahama, zan kasance daga mãsu hasãra."
48Aka ce: "Ya Nũhu! Ka sauka da aminci daga gare Mu da albarka a kanka, kuma rahama ta tabbata a kan waɗansu al´ummõmi daga waɗanda suke tãre da kai. Da waɗansu al´ummõmi da zã Mu jiyar da su dãɗi, sa´an nan kuma azãba mai raɗaɗi ta shafe su daga gare Mu."
49Waccan ƙissa tanã daga lãbãran gaibi, Munã yin wahayinsu zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance kanã sanin su ba, haka kuma mutãnenka ba su sani ba daga gabãnin wannan. Sai ka yi haƙuri. Lalle ne ãƙiba tanã ga mãsu taƙawa,
50Kuma zuwa ga Ãdãwa, (Mun aika) ɗan´uwansu Hũdu. Ya ce: "Yã kũ mutãnena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautãwa fãce Shi. Ba ku kasance ba fãce kunã mãsu ƙirƙirãwa.
51"Yã ku mutãnena! Bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa, ijãrata ba ta zama ba, fãce ga wanda Ya ƙãga halittata. Shin fa, bã ku hankalta?"
52"Kuma, ya mutãnena! Ku nħmi Ubangijinku gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare Shi, zai saki sama a kanku, tanã mai yawan zubar da ruwa, kuma Ya ƙãra muku wani ƙarfi ga ƙarfinku. Kuma kada ku jũya kunã mãsu laifi."
53Suka ce: "Yã Hũdu! Ba ka zo mana da wata hujja bayyananna ba, kuma ba mu zama mãsu barin abũbuwan bautawarmu ba dõmin maganarka, kuma ba mu zama mãsu yin ĩmãni da kai ba."
54"Bã mu cħwa, sai dai kurum sashen abũbuwan bautawarmu ya sãme ka da cũtar hauka." Yace: "Lalle ne nĩ, inã shaida wa Allah, kuma ku yi shaidar cħwa" lalle ne nĩ mai barranta ne daga abin da kuke yin shirki da shi."
55"Baicin Allah: Sai ku yi mini kaidi gabã ɗaya, sa´an nan kuma kada ku yi mini jinkiri."
56"Haƙĩƙa, ni na dõgara ga Allah, Ubangijĩna kuma Ubangijinku. Bãbu wata dabba fãce Shi ne Mai riko ga kwarkwaɗarta.(1) Haƙĩƙa, Ubangijĩna Yanã (kan) tafarki madaidaici."
57"To! Idan kun jũya, haƙĩƙa, nã iyar muku abin da aka aiko ni da shi zuwa gare ku. Kuma Ubangijĩna Yanã musanya waɗansu mutãne, waɗansunku su maye muku. Kuma bã ku cũtar Sa da kõme. Lalle Ubangijina a kan dukkan kõme, Matsari ne."
58Kuma a lõkacin da umurninmu ya je, Muka kuɓutar da Hũdu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare Mu. Kuma Muka kuɓutar da su daga azãba mai kauri.
59Haka Ãdãwa suka kasance, sun yi musun ãyõyin Ubangijinsu, kuma sun sãɓa wa ManzanninSa, kuma sun bi umurnin dukan mai girman kai, makangari.
60Kuma an biyar musu da la´ana a cikin wannan dũniya da Rãnar Kiyãma. To! Lalle ne Ãdãwa sun kãfirta da Ubangijinsu. To, Nĩsa ya tabbata ga Ãdãwa, mutãnen Hũdu!
61Kuma zuwa ga Samũdãwa (an aika) ɗan´uwansu Sãlihu. Ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa fãce Shi. Shĩ ne Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma Ya sanya ku mãsu yin kyarkyara a cikinta. Sai ku nħme Shi gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare Shi. Lalle Ubangijina Makusanci ne Mai karɓãwa."
62Suka ce: "Ya Sãlihu! Haƙĩƙa, kã kasance a cikinmu, wanda ake fatan wani alhħri da shi a gabãnin wannan. Shin kana hana mu bauta wa abin da ubanninmu suke bauta wa? Kuma haƙĩƙa mũ, munã cikin shakka daga abin da kake kiran mu gare shi, mai sanya kõkanto."
63Ya ce: "Ya mutãnħna! Kun gani? Idan na kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Ya bã ni rahama daga gare Shi, to, wane ne zai taimake ni daga Allah idan nã sãɓa Masa? Sa´an nan bã zã ku ƙãre ni da kõme ba fãce hasãra."
64"Kuma ya mutãnena! wannan rãƙumar Allah ce, tanã ãyã a gare ku. Sai ku bar ta ta ci a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shãfe ta da wata cũta kar azãba makusanciya ta kãma ku."
65Sai suka sõke ta. Sai ya ce: "Kuji dãɗi a cikin gidãjenku kwãna uku. Wannan wa´adi ne bã abin ƙaryatãwa ba."
66To, a lõkacin da umurninMu ya je, muka kuɓutar da Sãlihu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare Mu, kuma daga wulãkancin rãnar nan. Lalle ne Ubangijinka Shĩ neMai ƙarfi, Mabuwãyi.
67Sai tsãwa ta kãma waɗanda suka yi zãlunci, sai suka wãyi gari sunã guggurfãne a cikin gidãjensu.
68Kamar dai ba su zauna a cikinta ba. To! Lalle ne samũdãwa sun kãfirce wa Ubangijinsu. To, Nĩsa ya tabbata ga Samũdãwa.
69Kuma haƙĩƙa, manzanninMu sun je wa Ibrãhim da bushãra suka ce: "Aminci." Ya ce: "Aminci (ya tabbata a gare ku)." Sa´an nan bai yi jinkiri ba ya je da maraƙi ƙawãtacce.
70Sa´an nan a lõkacin da ya ga hannayensu bã su sãduwa zuwa gare shi (maraƙin), sai ya yi ƙyãmarsu, kuma ya ji tsõronsu. Suka ce, "Kada kaji tsõro lalle ne mũ, an aiko mu ne zuwa ga mutãnen Lũɗu"
71Kuma mãtarsa tanã tsaye(1) . Ta yi dãriya. Sai Muka yi mata bushãra (da haihuwar) Is´hãƙa, kuma a bayan Is´hãƙa, Yãƙũbu.
72Sai ta ce: "Yã kaitõna! Shin, zan haihu ne alhãli kuwa inã tsõhuwa, kuma ga mijĩna tsõho ne? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmãki."
73Suka ce: "Shin kinã mãmaki ne daga al´amarin Allah? Rahamar Allah da albarkarSa su tabbata a kanku, ya mutãnen babban gida! Lalle ne Shĩ abin gõdewa ne, Mai girma."
74To, a lõkacin da firgita ta tafi daga Ibrãhĩm, kuma bushãra tã je masa, Yanã mai jayayya a gare Mu, sabõda mutãnen Lũɗu!
75Lalle Ibrãhĩm, haƙĩƙa mai haƙuri ne, mai yawan addu´a, mai tawakkali.
76Ya Ibrãhĩm! Ka bijira daga wannan. Lalle shi, haƙĩƙa, umurnin Ubangijinka ne ya zo, kuma lalle ne sũ, abin da yake mai je musu azãba ce wadda bã a iya hanãwa.
77Kuma a lõkacin da manzanninMu suka je wa Lũɗu aka ɓãta masa rai game da su, ya, ƙuntata rai sabõda su. Ya ce: "Wannan yini ne mai tsananin masĩfa."
78Kuma mutãnensa suka je masa sunã gaggãwa zuwa gare shi, kuma a gabãni, sun kasance sunã aikatãwar mũnãnan ayyuka. Ya ce: "Yã mutãnħna! waɗannan, ´yã´yã na(1) sũ ne mafiya tsarki a gare ku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku wulãkantã ni a cikin bãƙĩna. Shin, bãbu wani namiji shiryayye daga gare ku?"
79Suka ce: "Lalle, haƙĩƙa kã sani, bã mu da wani hakki a cikin ´ya´yanka, kuma lalle kai haƙĩƙa, kanã sane da abin da muke nufi."
80Ya ce: "Dã dai inã da wani ƙarfi game da ku, kõ kuwa inã da gõyon bãya daga wani rukuni(2) mai ƙarfi?"
81(Manzannin) Suka ce: "Yã Lũɗu! Lalle mũ, manzannin Ubangijinka ne. Bã zã su iya sãduwa zuwa gare ka ba. Sai ka yi tafiyarka a wani yankin dare da iyãlinka, kuma kada wani daga gare ku ya waiwaya fãce mãtarka. Lalle ne abin da ya same su mai sãmunta ne. Lalle wa´adinsu lõkacin sãfiya ne. Shin lõkacin sãfiya bã kusa ba ne?"
82Sa´an nan a lõkacin da umurninMu ya je, Muka sanya na samanta ya zama na ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu a kanta (ƙasar Lũɗu) daga taɓo cũrarre.
83Alamtacce a wurin Ubangijinka. Kuma ita (ƙasar Lũɗu) ba ta zama mai nĩsa ba daga azzãlumai (Kuraishãwa).
84Kuma zuwa ga Madyana (Mun aika) ɗan´uwansu(1) Shu´aibu. Ya ce: "Ya Mutãnena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautãwa fãce shi kuma kada ku rage mũdu da sikħli. Lalle nĩ, inã ganin ku da wadãta.(2) Kuma lalle inã ji muku tsõron azãbar yini mai kħwayħwa."
85"Ya mutãnħna! Ku cika mũdu da sikħli da ãdalci, kuma kada ku naƙasta wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi ɓarnã a cikin ƙasa kunã mãsu fasãdi."
86"Falalar Allah mai wanzuwa ita ce mafi alhħri a gare ku idan kun kasance muminai, kuma ni bã mai tsaro ne a kanku ba."
87Suka ce: "Yã Shu´aibu! Shin sallarka ce take umurtar ka ga mu bar abin da ubanninmu suke bautãwa, kõ kuwa mu bar aikata abin da muke so a cikin dũkiyõyinmu? Lalle, haƙĩƙa kai ne mai haƙuri shiryayye!"
88Ya ce: "Ya mutãnena! Kun gani idan na kasance a kan hujja bayyananniya daga Ubangijina, kuma Ya azurta nĩ da arziki mai kyãwo daga gare Shi? Kuma bã ni nufin in sãɓa muku zuwa ga abin da nake hana ku daga gare shi. Bã ni nufin kõme fãce gyãrã, gwargwadon da na sãmi dãma. Kuma muwãfaƙãta ba ta zama ba fãce daga Allah. A gare shi na dõgara, kuma zuwa gare Shi na wakkala."
89"Kuma ya mutãnena! Kada sãɓa mini ya ɗauke ku ga misãlin abin da ya sãmi mutãnen Nũhu kõ kuwa mutãnen Hũdu kõ kuwa mutãnen Sãlihu ya sãme ku. Mutãnen Lũɗu ba su zama a wuri mai nĩsa ba daga gare ku."
90"Kuma ku nħmi Ubangijinku gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare shi. Lalle Ubangijĩna Mai Jin ƙai ne, Mai nũna sõyayya."
91Suka ce: "Yã Shu´aibu! Bã mu fahimta da yawa daga abin da kake faɗi, kuma munã ganin ka mai rauni a cikinmu. Kuma bã dõmin jama´arka ba dã mun jħfe ka, sabõda ba ka zama mai daraja a gunmu ba."
92Ya ce: "Ya mutãnena! Ashe, jama´ãta ce mafi daraja a gare ku daga Allah, kuma kun riƙħ Shi a bãyanku abin jħfarwa? Lallene Ubangijĩna Mai kħwayħwa ne ga abin da kuke aikatãwa."
93"Kuma ya mutãnena! Ku yi aiki a kan hãlinku. Lalle nĩ mai aiki ne. Da sannu zã ku san wãne ne azãba zã ta zo masa, ta wulakanta shi, kuma wãne ne maƙaryaci. Kuma ku yi jiran dãko, lalle ni mai dãko ne tãre da ku."
94Kuma a lõkacin da umurninMu yã je, Muka kuɓutar da Shu´aibu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare, Mu. Kuma tsãwa ta kama waɗanda suka yi zãlunci. Sai suka wãyi gari guggurfãne a cikin gidãjensu.
95Kamar ba su zaunã ba a cikinsu. To, halaka ta tabbata ga Madyana kamar yadda Samũdãwa suka halaka.
96Kuma haƙĩƙa Mun aiki Mũsã da ãyõyinMu, da dalĩli bayyananne.
97Zuwa ga Fir´auna da majalisarsa. Sai suka bi umurnin Fir´auna, amma al´amarin Fir´auna bai zama shiryayye ba.
98Yanã shũgabantar mutãnensa a Rãnar Kiyãma, har ya tuzgar da su a wuta. Kuma tir da irin tuzgãwarsu.
99Kuma aka biyar musu da la´ana a cikin wannan dũniya da Rãnar Kiyãma. Tir da kyautar(1) da ake yi musu.
100Wancan Yanã daga lãbãran alƙaryõyi. Munã bã ka lãbãrinsu, daga gare su akwai wanda ke tsaye da kuma girbabbe.(2)
101Kuma ba Mu zãlunce su ba, amma sun zãlunci kansu sa´an nan abũbuwan bautawarsu waɗanda suke kiran su, baicin Allah, ba su wadãtar musu kõme ba a lõkacin da umurnin Ubangijinka ya je, kuma (gumãkan) ba su ƙãra musu wani abu ba fãce hasãra.
102Kuma kamar wancan ne kãmun Ubangijinka, idan Ya kãma alƙaryõyi alhãli kuwa sunã mãsu zãlunci. Lalle kamũnSa mai raɗaɗi ne, mai tsanani.
103Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga wanda ya ji tsõron azãbar Lãhira. Wancan yini ne wanda ake tãra mutãne a cikinsa kuma wancan yini ne abin halarta.
104Ba Mu jinkirtã shi ba fãce dõmin ajali ƙidãyayye.
105Rãnar da za ta zo wani rai ba ya iya magana fãce da izninSa. Sa´an nan daga cikinsu akwai shaƙiyyi da mai arziki.
106To, amma waɗanda suka yi shaƙãwa, to, sunã a cikin wuta. Sunã mãsu ƙãra da shħka a cikinta.
107Suna madawwama a cikinta matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, fãce abin da Ubangijinka Ya so. Lalle Ubangijinka Mai aikatãwa ne ga abin da Yake nufi.
108Amma waɗanda suka yi arziki to, sunã a cikin Aljanna sunã madawwama, a cikinta, matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, fãce abin da Ubangijinka Ya so. Kyauta wadda bã ta yankħwa.
109Sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga abin da waɗannan suke bautawa. Bã su wata ibãda fãce kamar yadda ubanninsu ke aikatãwa a gabani. Kuma haƙĩƙa Mũ, Mãsu cika musu rabon su ne, bã tãre da nakasãwa ba.
110Kuma haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã littãfi, sai aka sãɓã(1) wa jũna a cikinsa. Kuma bã dõmin wata kalma wadda ta gabãta daga Ubangijinka ba, haƙĩƙa, dã an yi hukunci a tsakãninsu. Kuma haƙĩƙa, sunã a cikin wata shakka, game da shi, mai sanya kõkanto.
111Kuma lalle, haƙĩƙa, Ubangijinka Mai cika wa kõwa (sakamakon) ayyukansa ne. Lalle Shĩ, Mai ƙididdigewa ne ga abin da suke aikatãwa.
112Sai ka daidaitu(2) kamar yadda aka umurce ka, kai da waɗanda suka tũba tãre da kai kunã bã mãsu ƙħtara haddi ba. Lalle shĩ, Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa.
113Kada ku karkata(3) zuwa ga waɗanda suka yi zãlunci har wuta ta shãfe ku. Kuma bã ku da waɗansu majiɓinta baicin Allah, sa´an nan kuma bã zã a taimake ku ba.
114Kuma ka tsai da salla a għfe guda biyu na yini da wani yanki daga dare. Lalle ne ayyukan ƙwarai sunã kõre mũnãnan ayyuka. Wancan(4) ne tunãtarwa ga mãsu tunãwa.
115Kuma ka yi haƙuri. Allah bã Ya tõzartar da lãdar mãsu kyautatãwa.(5)
116To, don me mãsu hankali ba su kasance daga mutãnen ƙarnõnin da suke a gabãninku ba, sunã hani daga ɓarna a cikin ƙasa? fãce kaɗan daga wanda Muka kuɓutar daga gare su (sun yi hanin). Kuma waɗanda suka yi zãlunci suka bi abin da aka ni´imtar da su a cikinsa, suka kasance mãsu laifi.
117Kuma Ubangijinka bai kasance Yanã halakar da alƙaryu sabõda wani zãlunci ba, alhãli mutãnensu sunã mãsu gyãrãwa.(6)
118Kuma dã Ubangijinka Ya so, dã Yã sanya mutãne al´umma guda. Kuma bã zã su gushe ba sunã mãsu sãɓã wa jũna.
119Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama, kuma dõmin wannan(1) ne Ya halicce su. Kuma kalmar "Ubangijinka" Lalle ne zã Ni cika Jahannama da aljannu da mutãne gaba ɗaya" ta cika.
120Kuma dũbi dai Munã bã da lãbãri a gare ka daga lãbarun Manzanni, abin da Muke tabbatar da zuciyarka da shi. Kuma gaskiya ta zo maka a cikin wannan da wa´azi da tunãtarwã ga mãsu ĩmãni.
121Kuma kace wa waɗanda bã su yin ĩmãni, "Ku yi aiki a kan hãlinku, lalle mũ mãsu aiki ne.
122"Kuma ku yi Jiran dãko, lalle mu mãsu Jiran dãko(2) ne."
123Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake. Kuma zuwa gare Shi ake mayar da dukan al´amari. Sabõda haka ku bauta Masa kuma ku dõgara a kanSa. Kuma Ubangijinka bai zama Mai gafala daga abin da kuke aikatãwa ba.
Chapter 12 (Sura 12)
1A. L̃. R. Waɗancan ãyoyin Littãfi mai bayyanãwa ne.
2Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta.
3Mũ, Munã bãyar da lãbãri a gare ka, mafi kyãwon lãbãri ga abin da Muka yi wahayin wannan Alƙur´ãni zuwa gare ka. Kuma lalle ne kã kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga gafalallu.
4A lõkacin da Yũsufu ya ce wa ubansa, "Yã bãba! Lalle ne nĩ, nã ga taurãri gõma shã ɗaya, da rãnã da watã. Na gan su sunã mãsu sujada a gare ni."
5Ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Kada ka faɗi mafarkinka ga ´yan´uwanka, har su ƙulla maka wani kaidi. Lalle ne Shaidan ga mutum, haƙĩƙa, maƙiyi ne bayyanãnne.(1)
6"Kuma kãmar wancan ne, Ubangijinka Yake zãɓen ka, kuma Ya sanar da kai daga fassarar lãbãrai, kuma ya cika ni´imõminSa a kanka, kuma a kan gidan Yãƙũba kãmar yadda ya cika su a kan ubanninka biyu, a gabãni, Ibrãhĩm da Is´hãƙa. Lalle Ubangijinka ne Masani, Mai hikima."
7Lalle ne, haƙĩƙa, ãyõyi(2) sun kasance ga Yũsufu da ´yan´uwansa(3) dõmin mãsu tambaya.
8A lõkacin da suka ce:(4) lalle ne Yũsufu da ɗan´uwansa ne mafiya sõyuwa ga ubanmu daga gare mu, alhãli kuwa mũ jama´a guda ne. Lalle ubanmu, haƙĩƙa, yanã cikin ɓata bayyananniya.
9Ku kashe Yũsufu, kõ kuwa ku jħfa shi a wata ƙasa, fuskar ubanku ta wõfinta sabõda ku, kuma ku kasance a bãyansa mutãne sãlihai.
10Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Kada ku kashe Yũsufu. Ku jħfa shi a cikin duhun rĩjiya, wasu matafiya su tsince shi, idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
11Suka ce: "Yã bãbanmu!(5) Mħne ne a gare ka ba ka amince mana ba a kan Yũsufu, alhãli kuwa lalle ne mũ, haƙiƙa mãsu nashĩha muke a gare shi?"
12"Ka bar shi tãre da mu a gõbe, ya ji dãɗi, kuma ya yi wãsa. Kuma lalle ne mu, a gare shi, mãsu tsaro ne."
13Ya ce: "Lalle ne ni, haƙiƙa yanã ɓãta mini rai ku tafii da shi, Kuma inã tsõron kerkħci ya cinye shi, alhãli ku kuwa kunã mãsu shagala daga gare shi."
14Suka ce: "Haƙĩƙa idan kerkħci ya cinye shi, alhãli kuwa munã dangin jũna, lalle ne mũ, a sa´an nan, hakĩka, mun zama mãsu hasãra."
15To, a lõkacin(1) da suka tafi da shi, kuma suka yi niyyar su sanya shi a cikin duhun rĩjiya, Muka yi wahayi zuwa gare shi, "Lalle ne, kanã bã su lãbari game da wannan al´amari nãsu, kuma sũ ba su sani ba."
16Kuma suka je wa ubansu da dare sunã kũka.
17Suka ce: "Yã bãbanmu!(2) Lalle ne, mun tafi munã tsħre, kuma muka bar Yusufu a wurin kãyanmu, sai kerkħci ya cinye shi, kuma kai, bã mai amincħwa da mu ba ne, kuma kõ dã mun kasance mãsu gaskiya!"_
18Kuma suka je, a jikin rigarsa akwai wani jinin ƙarya. Ya ce: "ôa, zukatanku suka ƙawãta muku wani al´amari. Sai haƙuri mai kyau! Kuma Allah ne wanda ake nħman taimako (a gunSa) a kan abin da kuke siffantãwa."
19Kuma wani ãyari(3) ya je, sai suka aika mai nħman musu rũwa, sai ya zura gugansa, ya ce: "Yã bushãrata! Wannan yãro ne." Kuma suka ɓõye shi yanã abin sayarwa. Kuma Allah ne Masani ga abin da suke aikatãwa.
20Kuma suka sayar(4) da shi da ´yan kuɗi kaɗan, dirhamõmi ƙidãyayyu, Kuma sun kasance, a wurinsa, daga mãsu isuwa da abu kaɗan.
21Kuma wanda ya saye shi daga Masar(5) ya ce wa mãtarsa, "Ki girmama mazauninsa, akwai tsammãnin ya amfãne mu, kõ kuwa mu riƙe shi ɗã."Kuma kamar wancan ne Muka tabbatar ga Yũsufu,a cikin ƙasa kuma dõmin Mu sanar da shi daga fassarar labaru, kuma Allah ne Marinjãyi a kan al´amarinSa, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba."
22Kuma a lõkacin da ya isa mafi ƙarfinsa, Muka bã shi hukunci da ilmi. Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
23Kuma wadda yake(1) a cikin ɗãkinta, ta nħme shi ga kansa, kuma ta kukkulle ƙõfõfi, kuma ta ce, "Yã rage a gare ka!" ya ce: "Ina neman tsarin Allah! Lalle shĩ ne Ubangijina. Yã kyautata mazaunina. Lalle ne shĩ, mãsu zãlunci ba su cin nasara!"
24Kuma lalle ne, tã himmantu da shi. Kuma yã himmantu da ita in bã dõmin ya ga dalĩlin Ubangijinsa ba. Kãmar haka dai, dõmin Mu karkatar da mummũnan aiki da alfãsha daga gare shi. Lalle ne shi, daga bãyinMu zaɓaɓɓu yake.
25Kuma suka yi tsħre(2) zuwa ga ƙõfa. Sai ta tsãge rigarsa daga bãya, kuma suka iske mijinta a wurin ƙõfar. Ta ce: "Mħnene sakamakon wanda ya yi nufin cũta game da iyãlinka? Fãce a ɗaure shi, ko kuwa a yi masa wata azãba mai raɗaɗi."
26Ya ce: "Ita ce ta nħme ni a kaina."Kuma wani mai shaida daga mutãnenta ya bãyar da shaida:(3) "Idan rigarsa ta kasance an tsage ta daga gaba, to, tã yi gaskiya, kuma shĩ ne daga maƙaryata."
27"Kuma idan rigarsa ta kasance an tsãge ta daga bãya, to, tã yi ƙarya, kuma shĩ ne daga mãsu gaskiya."
28Sa´an nan a lõkacin da ya ga rĩgarsa an tsãge ta daga bãya, ya ce: "Lalle ne shi, daga kaidinku ne, mata! Lalle ne kaidinku mai girma ne!"
29"Yusufu! Ka kau da kai daga wannan. Kuma ki nħmi gãfara(4) dõmin laifinki. Lalle ne ke, kin kasance daga mãsu kuskure."
30Kuma waɗansu mãtã(5) a cikin Birnin suka ce: "Matar Azĩz tanã nħman hãdiminta daga kansa! Haƙĩƙa, yã rufe zũciyarta da so. Lalle ne mũ, Munã ganin ta a cikin ɓata bayyanãnna."
31Sa´an nan a lõkacin da ta ji lãbãri game da mãkircinsu, sai ta aika kiran liyafa zuwa gare su, kuma ta yi tattalin abincin da ake dõgara wajen cinsa, kuma ta bai wa kõwace ɗaya daga cikinsu wuƙa, kuma ta ce: "Ka fito a kansu." To, a lõkacin da, suka gan shi, suka girmamã shi, kuma suka yanyanke hannãyensu, kuma suka ce: "Tsarki yanã ga Allah! Wannan bã mutum ba ne! Wannan bai zama ba fãce Malã´ika ne mai daraja!"
32Ta ce: "To wannan ne fa wanda kuka, zarge(1) ni a cikinsa! Kuma lalle ne, haƙiƙa na nħme shi daga kansa, sai ya tsare gida, kuma nĩ inã rantsuwa, idan bai aikata abin da nake umurnin sa ba, haƙiƙa anã ɗaure shi. Haƙĩƙa, yanã kasancewa daga ƙasƙantattu."
33Ya ce: "Yã Ubangijina! Kurkuku ne mafi sõyuwa a gare ni daga abin da suke kirã na zuwa gare shi. Kuma idan ba Ka karkatar da kaidinsu daga gare ni ba, zan karkata zuwa gare su, kuma in kasance daga jãhilai."
34Sai Ubangijinsa Ya karɓa masa sabõda haka Ya karkatar da kaidinsu daga gare shi. Lalle Shĩ ne Mai jĩ, Masani.
35Sa´an nan kuma ya bayyana a gare su a bãyan sun ga alãmõmin, lalle ne dai su ɗaure shi har zuwa wani lõkaci.
36Kuma waɗansu samãri biyu suka shiga kurkuku tãre da shi.(2) Ɗayansu ya ce: "Lalle ne nĩ, nã yi mafarkin gã ni inã mãtsar giya." Kuma ɗayan ya ce: "Lalle ne nĩ, nã yi Mafarkin gã ni inã ɗauke da waina a bisa kaina, tsuntsãye sunã ci daga gare ta. Ka bã mu lãbãri game da fassararsu. Lalle ne mũ, Munã ganin ka daga mãsu kyautatãwa."
37Ya ce: "Wani abinci bã zai zo muku ba wanda ake azurtã ku da shi fãce nã bã ku lãbãrin fassararsa(3) , kãfin ya zo muku. Wannan kuwa yanã daga abin da Ubangijĩna Ya sanar da ni. Lalle ne nĩ nã bar addinin mutãne waɗanda ba su yi ĩmãni da Allah ba, kuma game da lãhira, sũ kãfirai ne."
38"Kuma na bi addinin iyayħna, Ibrãhĩm da Is´hãka da Yãƙũba. Bã ya yiwuwa a gare mu mu yi shirka da Allah da kõme. Wannan yana daga falalar Allah a kanmu da mutãne, amma mafi yawan mutãne bã su gõdewa."
39"Yã abõkaina biyu na kurkuku! Shin iyãyen giji dabam-dabam ne mafiya alhħri kõ kuwa Allah Makaɗaici Mai tanƙwasãwa?"
40"Ba ku bauta wa kõme, baicinSa, fãce waɗansu sũnãye waɗanda kuka ambace su, kũ da ubanninku. Allah bai saukar da wani dalĩli ba game da su. Bãbu hukunci fãce na Allah. Ya yi umurnin kada ku bauta wa kõwa fãce Shi. Wancan ne addini madaidaici, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba."
41"Yã abõkaina biyu, na kurkuku! Amma ɗayanku, to, zai shãyar da uban gidansa giya, kuma gudan, to, zã a tsĩrħ shi, sa´an nan tsuntsãye su ci daga kansa. An hukunta al´amarin, wanda a cikinsa kuke yin fatawa."
42Kuma ya ce da wanda ya tabbatar da cħwa shi mai kuɓuta ne daga gare su, "Ka ambacħ ni a wurin uban gidanka." Sai Shaiɗan ya mantar da shi tunãwar Ubangijinsa, sabõda haka ya zauna a cikin kurkuku ´yan shekaru.
43Kuma sarki ya ce: "Lalle ne, nã yi mafarki;(1) nã ga shãnu bakwai mãsu ƙiba, waɗansu bakwai rãmammu, sunã cin su, da zangarku bakwai kõre-kõre da waɗansu ƙeƙasassu. Yã kũ jama´a! Ku yi mini fatawa a cikin mafarkĩna, idan kun kasance ga mafarki kunã fassarawa."
44Suka ce: "Yãye-yãyen mafarki ne, kuma ba mu zamo masana ga fassarar yãye-yãyen mafarki ba."
45Kuma wannan da ya kuɓuta daga cikinsu ya ce: a bãyan yã yi tunãni a lõkaci mai tsawo, "Nĩ, inã bã ku lãbãri game da fassararsa. Sai ku aike ni."
46"Yã Yũsufu! Yã kai mai yawan gaskiya! Ka yi mana fatawa a cikin shãnu bakwai mãsu ƙiba, waɗansu bakwai rãmammu sunã cin su, da zangarku bakwai kõrãye da waɗansu ƙeƙasassu, tsammãnĩna in kõma ga mutãne, tsammãninsu zã su sani."
47Ya ce: "Kunã shũka, shħkara bakwai tutur, sa´an nan abin da kuka girbe, sai ku bar shi, a cikin zanganniyarsa,(1) sai kaɗan daga abin da kuke ci."
48"Sa´an nan kuma waɗansu bakwai mãsu tsanani su zo daga bãyan wancan, su cinye abin da kuka gabãtar dõminsu, fãce kaɗan daga abin da kuke ãdanãwa."
49"Sa´an nan kuma wata shħkara ta zo daga bãyan wancan, a cikinta ake yi wa mutãne ruwa mai albarka, kuma a cikinta suke mãtsar abin sha."
50Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi." To, a lõkacin da manzo ya je masa (Yũsufu), ya ce: "Ka kõma zuwa ga uban gidanka, sa´an nan ka tambaye shi; Mħnene hãlin mãtãyen nan waɗanda suka yanyanke hannãyensu? Lalle ne Ubangijĩna ne Masani game da kaidinsu."
51Ya ce: "Mħne ne babban al´amarinku, a lõkacin da kaka nħmi Yũsufu daga kansa?" Suka ce: "Tsarki ga Allah yake! Ba mu san wani mummũnan aiki a kan saba." Mãtar Azĩz ta ce: "Yanzu fa gaskiya(2) ta bayyana. Nĩ ce nã nħme shi daga kansa. Kuma lalle ne shĩ, haƙĩƙa, yanã daga mãsu gaskiya.
52"Wancan ne, dõmin ya san cħwa lalle ne ni ban yaudare shi ba a ɓõye, kuma lalle Allah bã Ya shiryar da kaidin mayaudara."
53"Kuma bã ni kuɓutar da kaina. Lalle ne rai, haƙĩƙa, mai yawan umurni ne da mummũnan aiki, fãce abin da Ubangjina Ya yi na rahama. Lalle Ubangjina Mai gãfara ne, Mai jin ƙai."
54Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi in kħɓe shi ga kaina." To, a lõkacin da Yũsufu ya yi masa magana sai ya ce: "Lalle ne kai a yau, a gunmu, mai daraja ne, amintacce."(1)
55Ya ce: "Ka sanya ni a kan taskõkin ƙasa. Lalle ne nĩ, mai tsarħwa ne, kuma masani."
56Kuma kamar wancan ne Muka bãyar da ĩko ga Yũsufu a cikin ƙasa(2) yanã sauka a inda duk yake so. Munã sãmun wanda Muke so da rahamar Mu, kuma bã Mu tõzartar da lãdar mãsu kyautatawa.
57Kuma lalle lãdar Lãhira ce mafi alhħri ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka kasance mãsu taƙawa.
58Kuma ´yan´uwan(3) Yũsufu suka jħ, sa´an nan suka shiga a gare shi, sai ya gãne su, alhãli kuwa su, sunã mãsu musunsa.
59Kuma a lõkacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, ya ce: "Ku zo mini da wani ɗan´uwa nãku daga ubanku. Ba ku gani ba cħwa lalle ne nĩ, inã cika ma´auni, kuma nĩ ne mafi alhħrin mãsu saukarwa?"
60"Sa´an nan idan ba ku zo mini da shĩ ba, to, bãbu awo a gare ku a wurĩna, kuma kada ku, kasance ni."
61Suka ce: "Zã mu nħme shi daga ubansa. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu aikatãwa ne."
62Kuma ya ce wa yaransa, "Ku sanya hajjarsu a cikin kãyansu, tsammãninsu sunã gãne ta idan sun jũya zuwa ga mutãnensu, tsammãninsu, zã su kõmo."
63To, a lõkacin da suka kõma zuwa ga ubansu, suka ce: "Yã bãbanmu! An hana mu awo sai ka aika ɗan´uwanmu tãre da mu. Zã mu yi awo. Kuma lalle ne, haƙĩƙa mũ, mãsu lũra da Shi ne."
64Ya ce: "Ashe, zã ni amince muku a kansa? Fãce dai kamar yadda na amince muku a kan ɗan´uwansa daga gabãni, sai dai Allah ne Mafĩfĩcin mãsu tsari, kuma Shĩ ne Mafi rahamar mãsu rahama."
65Kuma a lõkacin da suka bũɗe kãyansu, suka sãmi hajjarsu an mayar musu da ita, suka ce: "Yã bãbanmu! Ba mu zãlunci! Wannan hajjarmu ce an mayar mana da ita, kuma mu nħmo wa iyalinmu abinci, kuma mu kiyãye ɗan´uwanmu, kuma mu ƙãra awon kãyan rãƙumi guda, wancan awo ne mai sauki."
66Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙĩƙa, kunã dawo mini da shi, sai fa idan an kħwaye ku." To, a, lõkacin da suka yi mãsa alkawari, ya ce: "Allah ne wakĩli a kan abin da muke faɗa."
67Kuma ya ce: "Yã ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙõfa guda, ku shiga ta ƙõfõfi dabam-dabam,(1) kuma bã na wadãtar muku kõme daga Allah. Bãbu hukunci fãce daga Allah, a gare Shi na dõgara, kuma a gare Shi mãsu dõgara sai su dõgara."
68Kuma a lõkacin da suka shiga daga inda ubansu ya umurce su wani abu bai kasance yanã wadãtarwa ga barinsu daga Allah ba fãce wata bukata ce a ran Yãƙũbu, ya bayyana ta. Kuma lalle ne shĩ, haƙĩƙa, ma´abũcin wani ilmi ne ga abin da Muka sanar da shi, kuma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
69Kuma a lõkacin da suka shiga wajen Yũsufu, ya tattara ɗan´uwansa zuwa gare shi, ya ce: "Lalle nĩ ne ɗan´uwanka, sabõda haka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance sunã aikatãwa."
70Sa´an nan a lõkacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, sai ya sanya ma´auni a cikin kãyan ɗan´uwansa sa´an nan kuma mai yħkuwa ya yi yħkuwa," Yã kũ ãyari! lalle ne, haƙĩƙa kũ ɓarãyi ne."
71Suka ce: kuma suka fuskanta zuwa gare su: "Mħne ne kuke nħma?"
72Suka ce: "Munã nħman ma´aunin sarki. Kuma wanda ya zo da shi, yanã da kãyan rãkumi ɗaya, kuma ni ne lãmuni game da shi."
73Suka ce: "Tallahi! Lalle ne, haƙĩƙa, kun sani, ba mu zo don mu yi ɓarna a cikin ƙasa ba, kuma ba mu kasance ɓarãyi ba."
74Suka ce: "To mħne ne sakamakonsa idan kun kasance maƙaryata?"
75Suka ce: "Sakamakonsa, wanda aka same shi a cikin kãyansa, to, shi ne sakamakonsa,(1) kamar wancan ne muke sãka wa azzãlumai."
76To, sai ya fãra (bincike) da jikunansu a gabãnin jakar ɗan´uwansa. Sa´an nan ya fitar da ita daga jakar ɗan´uwansa. Kamar wancan muka shirya wa Yũsufu. Bai kasance ya kãma ɗan´uwansa a cikin addinin (dõkõkin) sarki ba, fãce idan Allah Ya so. Munã ɗaukaka darajõji ga wanda Muka so, kuma a saman kõwane ma´abũcin ilmi akwai wani masani.
77Suka ce: "Idan ya yi sãta, to, lalle ne wani ɗan´uwansa yã taɓa yin sãta a gabãninsa." Sai Yũsufu ya bõye(2) ta a cikin ransa. Kuma bai bayyana ta ba a gare su, ya ce: "Kũ ne mafi sharri ga wuri. Kuma Allah ne Mafi sani daga abin da kuke siffantãwa."
78Suka ce: "Yã kai Azĩzu! Lalle ne yanã da wani ubã, tsoho mai daraja, sabõda haka ka kãma ɗayanmu amatsayinsa. Lalle ne mũ, muna ganin ka daga mãsu kyautatãwa."
79Ya ce: "Allah Ya tsare mu daga mu kãma wani fãce wanda muka sãmi kãyanmu a wurinsa. Lalle ne mũ, a lõkacin nan, haƙĩƙa, azzãlumai ne."
80Sabõda haka, a lõkacin da suka yanke tsammãni daga gare shi, sai suka fita sunã mãsu gãnãwa.(1) Babbansu ya ce: "Shin, ba ku sani ba cħwa lalle ne ubanku ya riƙi alkawari daga Allah a kanku, kuma daga gabanin haka akwai abin da kuka yi na sakaci game da Yũsufu? Sabõda haka, bã zan gushe daga ƙasar nan ba fãce ubana yã yi mini izni, kõ kuwa Allah Ya yi hukunci a gare ni, kuma Shĩ ne Mafi alhħrin mahukunta."
81"Ku kõma zuwa ga ubanku, ku gaya masa: Yã bãbanmu, lalle ne ɗanka yã yi sãta, kuma ba mu yi shaida ba fãce da abin da muka sani, kuma ba mu kasance mun san gaibu ba."
82"Kuma ka tambayi alƙarya wadda muka kasance a cikinta da ãyari wanda muka gabãto a cikinsa, kuma lalle ne haƙĩƙa, mũ mãsu gaskiya ne."
83Ya ce: "ôa, zukatanku sun ƙawãta wani al´amari a gare ku. Sai haƙuri mai kyãwo, akwai tsammãnin Allah Ya zo mini da su gabã ɗaya ( Yũsufu da ´yan´uwansa). Lalle ne Shĩ ne Masani, Mai hikima."
84Kuma ya jũya daga gare su, kuma ya ce: "Yã baƙin cikina a kan Yũsufu!" Kuma idãnunsa suka yi fari sabõda huznu sa´an nan yanã ta haɗħwar haushi.
85Suka ce: "Tallahi! Bã zã ka gushe ba, kanã ambaton Yũsufu,(2) har ka kasance Mai rauni ƙwarai, kõ kuwa ka kasance daga mãsu halaka."
86Ya ce: "Abin sani kawai, inã kai ƙarar baƙin cikĩna da sunõna zuwa ga Allah, kuma na san abin da ba ku sani ba daga Allah."
87"Yã ɗiyãna! Sai ku tafi ku nħmo lãbãrin Yũsufu(1) da ɗan´uwansa. Kada ku yanke tsammãni daga rahamar Allah. Lalle ne, bãbu Mai yanke tsammãni daga rahamar Allah fãce mutãne kãfirai."
88Sa´an nan a lõkacin da suka shiga gare shi suka ce: "Yã kai Azĩzu! Cũta ta shãfe mu, mũ da iyãlinmu, iuma mun zo da wata hãja maras kuma. Sai ka cika mana ma´auni, kuma ka yi sadaka a gare mu. Lalle ne Allah Yanã sãka wa mãsu yin sadaka.(2) "
89Ya ce: "Shin, kun(3) san abin da kuka aikata ga Yũsufu da ɗan´uwansa a lõkacin da kuke jãhilai?"
90Suka ce: "Shin kõ, lalle ne, kai ne Yũsufu?" Ya ce: "Nĩ ne Yũsufu, kuma wannan shĩ ne ɗan´uwãna. Haƙĩƙa Allah Yã yi falala a gare mu. Lalle ne, shi wanda ya bi Allah da taƙawa, kuma ya yi haƙuri, to, Lalle ne Allah bã Ya tõzarta lãdar mãsu kyautatãwa."
91Suka ce: "Tallahi! Lalle ne haƙĩƙa, Allah Yã zãɓe ka a kanmu, kuma lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, mãsu kuskure."
92Ya ce: "Bãbu zargi a kanku a yau, Allah Yanã gãfartã muku, kuma Shĩ ne Mafi rahamar mãsu rahama."
93"Ku tafi da rĩgãta wannan, sa´an nan ku jħfa ta a kan fuskar mahaifina, zai kõma mai gani. Kuma ku zo mini da iyãlinku bãki ɗaya."
94Kuma, a lõkacin da ãyari(4) ya bar (Masar) ubansa ya ce: "Lalle ne nĩ inã shãƙar iskar Yũsufu, bã dõmin kunã ƙaryata ni ba."
95Suka ce: "Tallahi lalle ne, kai, haƙĩƙa, kanã a cikin ɓatarka daɗaɗɗa."
96Sa´an nan a lõkacin da mai bãyar da bushãra ya je, sai ya jħfa ta a kan fuskarsa, sai ya kõma mai gani. Ya ce: "Shin, ban gaya muku ba, lalle ne, ni inã sanin abin da ba ku sani ba, daga Allah?"
97Suka ce: "Yã ubanmu!(1) ka nħma mana gãfara ga zunubanmu, lalle ne mũ, mun kasance mãsu kuskure."
98Ya ce: "Da sannu zã ni nħma muku gãfara daga Ubangijina. Shi ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."
99Sa´an nan a lõkacin(2) da suka shiga gun Yũsufu, yã tattara mahaifansa biyu a gare shi, kuma ya ce: "Ku shiga Masar in Allah Ya so, kuna amintattu."
100Kuma ya ɗaukaka iyãyensa biyu a kan karaga, sa´an nan suka fãɗi a gare shi, suna mãsu sujada.(3) Kuma ya ce: "Ya bãbãna! Wannan ita ce fassarar mafarkin nan nãwa. Lalle ne Ubangijina Ya sanya shi ya tabbata sõsai, kuma lalle ne Ya kyautata game da ni a lõkacin da Ya fitar da ni daga kurkuku. Kuma Ya zo da ku daga ƙauye, a bãyan Shaiɗan yã yi fisgar ɓarna a tsakãnĩna da tsakãnin ´yan´uwana. Lalle ne Ubangijina Mai tausasawa ne ga abin da Yake so. Lalle ne Shĩ, Shĩ ne Masani, Mai hikima."
101"Yã Ubangijina(4) lalle ne Kã bã ni daga mulki, kuma Kã sanar da ni daga fassarar lãbaru. Ya Mahaliccin sammai da ƙasa! Kai ne Majiɓincĩna a dũniya da Lãhira Ka karɓi raina inã Musulmi, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
102Wannan daga(5) lãbarun gaibi ne, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke yin niyyar zartar da al´amarinsu, alhãli sunã yin mãkirci.
103Kuma mafi yawan mutãne ba su zama mãsu ĩmãni ba ,kõ da kã yi kwaɗayin haka.
104Kuma bã ka tambayar su wata lãdã a kansa. Shĩ bai zama ba fãce ambato dõmin halittu.
105Kuma da yawa, wata ãyã a cikin sammai da ƙasa sunã shũɗħwa a kanta kuma sũ, sunã bijirħwa daga gare ta.
106Kuma mafi yawansu ba su yin ĩmãni da Allah fãce kuma sunã mãsu shirki.
107Shin fa, sun amince cħwa wata masĩfa daga azãbar Allah ta zo musu ko kuwa Tãshin Ƙiyãma ta zo musu kwatsam, alhãli sũ ba su sani ba?
108Ka ce: "Wannan ce hanyãta(1) ; inã kira zuwa ga Allah a kan basĩra, nĩ da waɗanda suka bĩ ni, kuma tsarki ya tabbata ga Allah! Nĩ kuma, ban zama daga mãsu shirki ba."
109Kuma ba Mu aika ba a gabãninka fãce mazãje, Munã wahayi zuwa gare su, daga mutãnen ƙauyuka. Shin fa, ba su yi tafiya a cikin ƙasa ba, dõmin su dũba yadda ãƙibar waɗanda suka kasance daga gabãninsu ta zama? Kuma lalle ne gidan Lãhira shĩ ne mafi alhħri ga waɗanda suka yi taƙawa? Shin fa, bã ku hankalta?
110Har a lõkacin da Manzanni suka yanke tsammãni, kuma suka yi zaton cħwa an jingina su ga ƙarya, sai taimakonMu ya je masu, sa´an nan Mu tsħrar da wanda Muke so, kuma bã a mayar da azãbarMu daga mutãne mãsu laifi.
111Lalle ne haƙĩƙa abin kula yã kasance a cikin ƙissoshinsu ga masu hankali. Bai kasance wani ƙirƙiran lãbãri ba kuma amma shi gaskatãwa ne ga abin da yake a gaba gare shi, da rarrabħwar dukan abũbuwa, da shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suka yi ĩmãni.
Chapter 13 (Sura 13)
1A. L̃. M̃. R. Waɗancan ayõyin littãfi ne, kuma abin da aka saukar gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya, kuma amma mafi yawan mutãne bã su yin ĩmãni.
2Allah Shi ne wanda Ya ɗaukaka sammai, bã da ginshiƙai ba waɗanda kuke ganin su. Sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi, kuma Ya hõre rãnã da watã, kõwane yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce. Yanã shirya al´amari, Yanã rarrabe ãyõyi daki-daki, mai yiwuwa ne ku yi yaƙĩni da haɗuwa da Ubangijinku.
3Kuma shĩ, ne wanda Ya shimfiɗa kasa, kuma Ya sanya duwãtsu da kõguna a cikinta, kuma daga dukan ´ya´yan itãce Ya sanya ma´aura biyu cikinsu. Yanã sanya dare ya rufe yini. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin tunãni.
4Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna mãsu maƙwabtaka, da gõnaki na inabõbi da shũka da dabĩnai iri guda, da waɗanda bã iri guda ba, anã shayar da su da ruwa guda. Kuma Munã fĩfĩta sãshensu a kan sãshe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga muiãne waɗanda suke hankalta.
5Kuma idan ka yi mãmãki, to, mãmãkin kam shi ne maganarsu, "Shin, idan muka kasance turɓãya, zã mu zama a cikin wata halitta sãbuwa?" Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da Ubangijinsu, kuma waɗanda akwai ƙuƙumai a cikin wuyõyinsu, kuma waɗancan ne abõkan wuta. Sũ, a cikinta, mãsu dawwama ne.
6Kuma sunã nħman ka da gaggãwa da azãba a gabãnin rahama, alhãli kuwa abũbuwan misãli sun gabãta a gabãninsu. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Ma´abũcin gãfara ne ga mutãne a kan zãluncinsu, kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Mai tsananin uƙũba ne.
7Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cħwa don me ba a saukar da wata ãyã a gare shi ba daga Ubangijinsa? Abin sani kawai, kai dai mai gargaɗi ne kuma a cikin kõwaɗanne mutãne akwai mai shiryarwa.
8Allah Yanã sanin abin da kõwace mace take ɗauke da shi a cikinta da abin da mahaifu suke ragħwa(1) da abin da suke ƙãrãwa. Kuma dukkan kõme, a wurinSa, da gwargwado yake.
9Shi ne Masanin fake da bayyane, Mai girma, Maɗaukaki.
10Daidai ne daga gare ku, wanda ya asirta magana da wanda ya bayyana game da ita, da wanda yake shi mai nħman ɓõyewa ne da dare, da mai bayyana a cikin ƙãwalwalniyar(2) rãna da rãna.
11(Kowannenku) Yanã da waɗansu malã´iku mãsu maye wa jũna a gaba gare shi da bãya gare shi, sunã tsare shi daga umurnin Allah. Lalle ne Allah bã Ya canja abin da yake ga mutãne sai sun canja abin da yake ga zukatansu. Kuma idan Allah Ya yi nufin wata azãba game da mutãne, to, bãbu mai mayar da ita, kuma bã su da wani majiɓinci(3) baicin Shi.
12Shĩ ne Wanda Yake nũna muku walƙiya dõmin tsõro da tsammãni, kuma Ya ƙãga halittar girãgizai mãsu nauyi.
13Kuma arãdu tanã tasbĩhi game da gõde Masa, da malã´iku dõmin tsoronsa. Kuma Yanã aiko tsãwawwaki, sa´an nan Ya sãmi wanda Yake so da su alhãli kuwa sũ, sunã jãyayya a cikin (al´amarin) Allah kuma shĩ ne mai tsananin hĩla.(4)
14Yanã da kiran gaskiya, kuma waɗanda (kãfirai) suke kira baicinsa, bã su karɓa musu da kõme fãce kamar mai shimfiɗa tãfukansa zuwa ga ruwa (na girgije) dõmin (ruwan) ya kai ga bãkinsa, kuma shi bã mai kaiwa gare shi ba. Kuma kiran kãfirai (ga wanin Allah) bai zama(1) ba fãce yanã a cikin ɓata.
15Kuma sabõda Allah wanda yake a cikin sammai da ƙasa suke yin sujada, so da ƙi, kuma da inuwõyinsu, a sãfe da maraice.
16Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Allah". Ka ce: "Ashe fa, kun riƙi waɗansu masõya baicin Shi, waɗanda ba su mallaka wa kansu wani amfãni ba kuma haka bã su tũre wata cũta?" Ka ce: "Shin makãho da mai gani sunã daidaita? Kõ shin duhu da haske sunã daidaita? ko sun sanya ga Allah waɗansu abõkan tãrayya waɗanda suka yi halitta kamar halittarSa sa´an nan halittar ta yi kama da jũna a gare su?" Ka ce: "Allah ne Mai halitta kõme kuma Shĩ ne Maɗaukaki, Marinjãyi."
17Ya saukar da ruwa daga sama(2) , sai magudanai suka gudãna da gwargwadonsu. Sa´an nan kõgi ya ɗauki kumfa mai ƙãruwa, kuma daga abin da suke zuga a kansa (azurfa ko zinari kõ ƙarfe) a cikin wuta dõmin nħman ado kõ kuwa kãyan ɗãki akwai kumfa misãlinsa (kumfar ruwa). Kamar wancan ne Allah Yake bayyana gaskiya da ƙarya. To, amma kumfa, sai ya tafi ƙħƙasasshe, kuma amma abin da yake amfãnin mutãne sai ya zauna a cikin ƙasa. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana misãlai.
18Ga waɗanda(3) suka karɓa wa Ubangijinsu akwai abu mafi kyau a gare su, kuma waɗanda suke ba su karɓa Masa ba, to, lalle dã sunã da abin da yake a cikin ƙasa gaba ɗaya da misãlinsa tãre da shi, haƙĩƙa, dã sun yi fansa da shi. Waɗancan sunã da mummunan bincike kuma matabbatarsu Jahannama ce, kuma tir da ita ta zama shimfida.
19Shin, fa, wanda yake sanin cħwa lalle abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya yanã zama kamar wanda yake makãho? Abin sani kawai masu hankali sũ ke yin tunãni.
20Sũ ne waɗanda suke cikãwa da alkawarin Allah, kuma bã su warware alkawari.
21Kuma sũ ne waɗanda suke sãdar da abin da Allah Ya yi umurni da shi dõmin a sãdar da shi kuma sunã tsõron Ubangijinsu, kuma sunã tsõron mummũnan bincike.
22Kuma waɗanda suka yi haƙuri dõmin nħman yardar Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar da abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, kuma sunã tunkuɗe mummunan aiki da mai kyau. Waɗancan sunã da ãƙibar gida mai kyau.
23Gidãjen Aljannar zama sunã shigarsu, sũ da waɗanda suka kyautatu daga iyãyensu, da mãtansu da zũriyarsu. Kuma malã´iku sunã shiga zuwa gunsu ta kõwace kõfa.
24"Aminci(1) ya tabbata a kanku sabõda abin da kuka yi wa haƙuri. Sãbõda haka madalla da ni´imar ãƙibar gida."
25Kuma waɗanda(2) suka warware alkawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma sunã yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi dõmin a sãdar da shi kuma sunã ɓarna a cikin ƙasar. Waɗancan sunã da wata la´ana, kuma sunã da mũnin gida.
26Allah ne Yake(3) shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuntatãwa. Kuma sun yi farin ciki da rãyuwar dũniya, alhali kuwa rãyuwar dũniya ba ta zama ba dangane ga ta Lãhira fãce jin dãɗi kaɗan.
27Kuma Waɗanda suka kãfirta, sunã cħwa, "Don me ba a saukar da wata ãyã ba a kansa daga Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Yanã ɓatar da wanda Yake so kuma Yanã shiryar da wanda ya tũba zuwa gare shi."
28Waɗanda suka yi ĩmãni kuma zukãtansu sukan natsu da ambaton Allah.(4) To, da ambaton Allah zukãta suke natsuwa.
29Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata aiki nagari, farin ciki yã tabbata a gare su, da kyakkyawar makõma.
30Kamar wancan ne Muka aika ka a cikin al´umma wanda take waɗansu al´ummai sun shũɗe daga gabaninta, dõmin ka karanta musu abin da Muka yi wahayi zuwa a gare ka, alhãli kuwa sũ, sunã kãfirta da Rahaman.(1) Ka ce: "Shi ne Ubangijĩna, bãbu abin, bautãwa fãce Shi, a gare Shi na dõgara, kuma zuwa gare Shi tũbãta take."
31Kuma dã lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwãtsu game da shi, kõ kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (dã ba su yi ĩmãni ba). ôa ga Allah al´amari yake gabã ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi ĩmãni ba su yanke tsammãni ba da cħwa da Allah Yã so, dã Yã shiryar da mutãne gabã ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kãfirci ba zã su gushe ba wata masĩfa tanã samun su sabõda abin da suka aikata, kõ kuwa ka saukã(2) kusa da gidãjħnsu, har wa´adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah bã ya sãɓã wa lõkacin alkawari.
32Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili da Manzanni kãfinka, sai Na yi jinkiri ga waɗanda suka kãfirta, sa´an nan Na kãma su. To, yãya uƙũbãta take?
33Shin fa, wanda shĩ Yake tsaye a kan kõwane rai game da abin da ya tanada (zai zama kamar wanda ba haka ba)? Kuma suka sanya abõkan tãrayya ga Allah! Ka ce: "Ku ambaci sũnãyensu."Ko kunã bai wa Allah lãbãri ne game da abin da bai sani ba a cikin ƙasa? Kõ da bayyananniyar magana kuke yin shirka, (banda a cikin zũciya)? ôa, an dai ƙawãta wa waɗanda suka kafirta mãkircinsu kuma an kange su daga hanya. Kuma wanda Allah Ya ɓatar to, bãbu wani mai shiryarwa a gare shi!"
34Sunã da wata azãba a cikin rãyuwar dũniya, kuma haƙĩƙa azãbar Lãhira ce mafi tsanani kuma bãbu wani mai tsare su daga Allah.
35Misãlin Aljanna wadda aka yi alkawarinta ga mãsu taƙawa, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinta. Abincinta yana madawwami da inuwarta. Waccan ce ãƙibar waɗanda suka yi taƙawa, kuma ãƙibar kãfirai, ita ce wuta,
36Kuma waɗanda Muka bã su Littãfi sunã farin ciki da abin da aka saukar zuwa gare ka, kuma daga ƙungiyõyi akwai mai musun sãshensa. Ka ce: "Abin sani kawai, an umurce ni da in bauta wa Allah kuma kada in yi shirka da Shi, zuwa gare Shi nake kira, kuma zuwa gare Shi makõmata take."
37Kuma kamar wancan ne Muka saukar da shi,(1) Hukunci a cikin Lãrabci. Kuma lalle ne idan kã bi son zuciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bãbu wani masõyi a gare ka mai kãre ka daga Allah, kuma bãbu matsari.
38Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika waɗansu manzanni, daga gabãninka, kuma Muka sanya mãtan aure a gare su da zũriyya, kuma ba ya kasancħwa ga wani Manzo ya zo da wata ãyã, sai da iznin Allah. Ga kõwane ajali(2) akwai littãfi.
39Allah Yanã shafe abin da Yake so, kuma Yanã tabbatarwa kuma a wurinsa asalin Littãfin yake.
40Kuma imma lalle Mu nũna(3) maka sãshen abin da Muke yi musu wa´adi, kõ kuwa lalle Mu karɓi ranka to abin sani kawai iyarwa ce a kanka, kuma hisãbi yana gare Mu.
41Shin, kuma ba su gani ba cħwa lalle ne, Muna jħ wa ƙasar (su), Munã rage ta daga għfunanta? Kuma Allah ne Yake yin hukuncinsa. Babu mai bincike ga hukuncinsa. Kuma shĩ ne Mai gaggãwar sakamako.(4)
42Kuma lalle ne waɗanda suke a gabãninsu sun yi mãkirci. To, ga Allah mãkircin yake gabã ɗaya. Ya san abin da kõwane rai yake tãnada. Kuma kãfirai zã su sani, ga wane ãƙibar gida take.
43Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Ba a aiko ka ba." Ka ce, "Allah Yã isa zama shaida a tsakãnina da tsakãninku da wanda yake a wurinsa akwai ilmin(1) Littãfi."
Chapter 14 (Sura 14)
1A. L̃. R. Littãfi ne mun saukar da shi zuwa gare ka dõmin ka fitar da mutãne daga duhunhuna zuwa ga haske, da iznin Ubangijinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwãyi,Abin gõdħwa.
2Allah wanda Yake Yanã da abin da ke cikin sammai da cikin ƙasa. Kuma bone yã tabbata ga kãfirai daga azãba mai tsanani.
3Waɗanda suka fi son rãyuwar dũniya fiye da ta Lãhira, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah, kuma sunã nħman ta karkace. Waɗancan na a cikin ɓata mai nĩsa.
4Kuma ba Mu aika wani Manzo ba fãce da harshen mutãnensa dõmin ya bayyanã musu. Sa´an nan Allah Ya ɓatar da wanda Yake so kuma Ya shiryar da wanda Yake so, kuma shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima.
5Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Mũsã game, da ãyõin Mu cħwa, "Ka fitar da mutãnenka daga duhu zuwa ga haske. Kuma ka tunar musu da kwãnukan (masĩfun) Allah." Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi dõmin dukan mai yawan haƙuri, mai gõdiya.
6Kuma a lõkacin da Mũsã yace wa mutãnensa, "Ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da Ya tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, sunã yi muku mummunar azãba, kuma sunã yanyanka ɗiyanku, kuma sunã rãyar da mãtanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabãwa mai girmã daga Ubangijinku."
7Kuma a lõkacin da Ubangijinku Ya sanar, "Lalle ne idan kun gõde, haƙĩƙa, Inã ƙãra muku, kuma lalle ne idan kun kãfirta haƙĩƙa azãbãta, tabbas, mai tsanani ce."
8Kuma Mũsã ya ce: "Idan kun kãfirta kũ da waɗanda suke a cikin ƙasa, gabã ɗaya, to, lalle ne Allah haƙĩƙa Mawadãci ne, Mai yawan gõdiya."
9Shin lãbãrin waɗanda suke a gabãninku, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdawa bai zomuku ba? Kuma da waɗanda suke daga bãyansu bãbu wanda yake sanin su fãce Allah? Manzanninsu sun jħ musu da hujjõji mabayyana, sai suka mayar da hannayensu a cikin bãkunansu, kuma suka ce: "Lalle ne mũ, mun kãfirta da abinda aka aiko ku da shi. Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa munã a cikin shakka da abin do kuke kiran mu zuwa gare shi, mai sanya kõkanto."
10Manzanninsu suka ce "Ashe, akwai shakka a cikin (sha´anin) Allah, Mai ƙãga halittar sammai da ƙasa Yanã kiran ku dõmin Ya gãfarta muku zunubanku, kuma Ya jinkirtã muku zuwa ga ajali ambatacce?" Suka ce: "Ba ku zama ba fãce mutãne misãlinmu kuma nufinku ku kange mu daga abin da iyãyenmu suka kasance sunã bautãwa sai ku zo mana da dalĩli mabayyani."
11Manzanninsu suka ce musu, "Bã mu zama ba fãce mutãne misãlinku, kuma amma Allah Yanã yin falala a kan wanda Yake so daga bãyinsa, kuma bã ya kasancħwa a gare mu, mu zo muku da wani dalĩli fãce da iznin Allah. Kuma ga Allah sai mũminai su dõgara.
12"Kuma mħne ne a gare mu, bã zã mu dõgara ga Allah ba, alhãli kuwa haƙĩƙa Yã shiryar da mu ga hanyõyinmu? Kuma lalle ne munã yin haƙuri a kan abin da kuka cũtar da mu, kuma ga Allah sai mãsu dõgaro su dõgara."
13Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce wa Manzanninsu, "Lalle ne munã fitar da ku daga ƙasarmu, kõ kuwa haƙĩƙa, kunã kõmowã a cikin addininmu." Sai Ubangijinsu Ya yi wahayi zuwa gare su, "Lalle ne, Munã halakar da azzãlumai."
14Kuma haƙĩƙa, Munã zaunar da ku ga ƙasa a bãyansu. Wancan ne abin gargaɗi ga wanda ya ji tsõron matsayiNa, kuma ya ji tsõron ƙyacħwãTa.
15Kuma suka yi addu´ar alfãnu.(1) Kuma kõwane kangararre mai tsaurin kai ya tãɓe.
16Daga bãyansa akwai Jahannama, kuma anã shãyar da shi daga wani ruwa, surkin jini.
17Yanã kwankwaɗarsa, kuma bã ya jin sauƙin haɗiyarsa, kuma mutuwa ta jħ masa daga kõwane wuri kuma bai zama mai mutuwa ba, kuma daga bãyansa akwai azãba mai kauri.
18Misãlin waɗanda suka kãfirta da Ubangijinsu, ayyukansu sun yi kama da tõka wadda iska ta yi tsananin bugãwa da ita a cikin yini mai gũguwa. Ba su iya amfãni daga abin da suka yi tsirfa a kan kõme.Wancan ita ce ɓata mai nĩsa.
19Shin, ba ka gani ba cħwa lalle ne Allah Yã halicci sammai bakwai da ƙasa da mallakarSa.(1) Idan Yã so zai tafiyar da ku, kuma Ya zo da wata halitta sãbuwa.
20Kuma wancan bai zama mabuwãyi ba ga Allah.
21Kuma suka bayyana ga Allah gabã daya, sai mãsu rauni suka ce wa waɗanda suka kangara, "Lalle ne mũ, mun kasance mãsu bi a gare ku, to, shin, kũ mãsu kãrewa ga barinmu ne daga azãbar Allah daga wani abu?"(2) Suka ce: "Dã Allah Ya shiryar da mu, dã mun shiryar da ku, daidai ne a kanmu, mun yi rãki ko mun yi haƙuri ba mu da wata mafaka."
22Kuma Shaiɗan ya ce a lõkacin da aka ƙãre al´amarin, "Lalle ne Allah Ya yi muku wa´adi, wa´adin gaskiyã, kuma na yi muku wa´adi, sa´an nan na sãɓã muku. Kuma bãbu wani dalĩli a gare ni a kanku fãce na kirã ku, sa´an nan kun karɓã mini. Sabõda haka kada ku zarge ni, kuma ku zargi kanku. Ban zama mai amfaninku ba, kuma ba ku zama mãsu amfãnĩna ba. Lalle na barranta da abin da kuka haɗã ni da shi gabanin wannan (matsayi). Lalle azzãlumai sunã da azãba mai raɗaɗi."(3)
23Kuma aka shigar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, a gidãjen Aljanna, kõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu sunã madawwamã a cikinsu da iznin Ubangijinsu, gaisuwarsu a cikinta "Salãm", (wãtau Aminci).
24Shin, ba ka ganĩ ba, yadda Allah Ya buga wani mĩsali, kalma mai kyau(4) kamar itãciya ce mai kyau, asalinta yanã tabbatacce, kuma rħshenta yanã cikin sama?
25Tanã bãyar da abincinta a kõwane lõkaci da iznin Ubangijinta! Kuma Allah Yanã buga misãli ga mutãne, mai yiwuwã ne, sunã tunãwa.
26Kuma misalin kalma mummũnã(1) kamar itãciya mummũnã ce, an tumɓuke ta daga bisa ga ƙasa, bã ta da wata tabbata.
27Allah Yanã tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni da magana tabbatacciya a cikin rãyuwar dũniya, da cikin Lãhira, Kuma Allah Yanã ɓatar da azzãlumai, kuma Allah Yanã aikata abin da Yake so.
28Shin ba ka lura ba da waɗanda suka musanya(2) ni´imar Allah da kãfirci kuma suka saukar da mutãnensu a gidan halakã?
29Sunã ƙõnuwa a wutar jahannama, kuma tir da matabbatarsu.
30Kuma suka sanya wa Allah kĩshiyõyi, dõmin ɓatarwa daga hanyarSa, Ka ce: "Ku ji dãɗi, sa´an nan, lalle ne, makõmarku Wutar ce."
31Ka ce wa bãyĩNa waɗanda suka yi ĩmãni su tsayar da salla kuma su ciyar daga abin da Muka azurtã su, a asirce da bayyane, daga gabãnin wani wuni ya zo, bãbu ciniki a ciki, kuma bãbu abõtaka.
32Allah ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya fitar game da shi, daga ´ya´yan itãce arziki dõminku kuma Ya hõrħ jirgin ruwa dõmin ya yi gudu a cikin tħku da umurninSa, kuma Ya hõrħ muku kõguna.
33Kuma Ya hõrħ muku rãnã da watã sunã madawwama biyu, kuma Ya hõrħ muku dare da wuni.
34Kuma Ya bã ku dukkan abin da kuka rõƙe Shi kuma idan kun ƙidaya, ni´imar Allah bã zã ku lissafe ta ba. Lalle ne mutum, haƙĩƙa, mai yawan zãlunci ne, mai yawan kãfirci.
35Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Yã Ubangijina! Ka sanyã wannan gari(1) amintacce kuma Ka nĩsanta ni, nĩ da ɗiyãna daga bauta wa gumãka.
36"Yã Ubangijina! Lalle ne sũ, sun ɓatar da mãsu yawa daga mutãne sa´an nan wanda ya bĩ ni, to, lalle shi, yanã daga gare ni, kuma wanda ya sãɓa mini, to, lalle ne Kai Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
37"Yã Ubangijinmu! Lalle ne ni, na zaunar da zuriyata ga rãfi wanda ba ma´abũcin shũka ba, a wurin Ɗãkinka mai alfarma. Yã Ubangijinmu! Dõmin su tsayar da salla. Sai Ka sanya zukãta daga mutãne sunã gaggãwar bħgenzuwa gare su, kuma ka azurtã su daga ´ya´yan itãce, mai yiwuwã ne sunã gõdħwã."
38"Yã Ubangijinmu! Lalle ne Kai Kanã sanin abin da muke ɓõyħwa, da abin da muke bayyanãwa. Kuma bãbu abin da yake ɓõyħwa ga A1lah, daga wani abu a cikin ƙasa, kuma bãbu a cikin sama."
39"Gõdiyã ta tabbata ga Allah wanda Yake Ya bã ni inã a cikin tsufa Ismã´ila da Is´hãƙa. Lalle ne Ubangijina, haƙĩƙa, Mai jin addu´a ne."
40"Yã Ubangijina! Ka sanyã ni mai tsayar da salla. Kuma daga zũriyyata. Yã Ubangijinmu! Kuma Ka karɓi addu´ata."
41"Yã Ubangijinmu! Ka yi gãfara gare ni, kuma ga mahaifãna, kuma da mũminai, a rãnar da hisãbi yake tsayãwa."
42"Kuma kada ka yi zaton Allah Mai shagalã ne daga abin da azzalumai suke aikatãwã. Abin sani kawai, Yanã jinkirta musu ne zuwa ga wani wuni, wanda idãnuwa suke fita turu-turu a cikinsa."
43"Sunã mãsu gaggãwa, mãsu ɗaukaka kãwunansu zuwa sama ƙiftawar ganinsu ba ta kõmãwa gare su. Kuma zukãtansu wõfintattu."(1)
44Kuma ka yi gargaɗi ga mutãne ga rãnar da azãba take jħ musu, sai waɗanda suka yi zãlunci su ce: "Yã Ubangijinmu! Ka yi mana jinkiri zuwa ga wani ajali makusanci, mu karɓa wa kiranKa, kuma mu bi Manzanni."(Allah Ya ce musu) "Ashe, ba ku kasance kun yi rantsuwã ba daga gabãni, cħwa bã ku da wata gushħwa?
45"Kuma kuka zaunã a cikin gidãjen waɗanda suka zãlunci kansu, kuma ya bayyana a gare ku yadda Muka aikatã game da su, kuma Muka buga muku misãlai."
46Kuma lalle sun yi mãkirci irin makircinSu kuma a wurin Allah makircinsu, yake, kuma lalle ne makircinsu yã kasance, haƙĩƙa, duwãtsu sunã gushħwã sabõda shi.
47Sabõda haka, kada ka ƙarfafa zaton Allah Mai sãɓa wa´adinSa ne ga ManzanninSa. Lalle ne Allah ne Mabuwãyi, Ma´abũcin azãbar rãmuwa.
48A rãnar da ake musanya ƙasa(2) bã ƙasar nan ba, da sammai kuma su bayyana ga Allah Makaɗaici, Mai tanƙwasãwa.
49Kuma kana ganin mãsu laifi, a rãnar nan, sunã waɗanda aka yi wa ciri daidai a cikin marũruwa.
50Rigunansu daga farar wutã ne, kuma wuta ta rufe fuskõkinsu.
51Dõmin Allah Ya sãkã wa kõwane rai da abin da ya tsuwurwurta. Lalle ne, Allah Mai gaggãwar hisãbi ne.
52Wannan iyarwa ce ga mutãne, kuma dõmin a yi musu gargaɗi da shi, kuma dõmin su sani cħwa, abin sani kawai, shĩ ne abin bautawa guda. Kuma dõmin masu hankali su riƙa tunãwa.
Chapter 15 (Sura 15)
1A. L̃. R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
2Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.(1)
3Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa´an nan da sannu zã su sani.
4Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
5Wata al´umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
6Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur´ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
7"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã´ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
8Bã Mu sassaukar da malã´iku fãce da gaskiya,(2) bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
9Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur´ãni), kuma lalle Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayħwane gare shi.
10Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
11Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
12Kamar wancan ne Muke shigar da shi(3) a cikin zukãtan mãsu laifi.
13Bã su yin ĩmãni da shi,(4) kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
14Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
15Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. ôa, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
16Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
17Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
18Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
19Kuma ƙasa Mun mĩkħ ta kuma Mun jħfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikħli.
20Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã(1) da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
21Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
22Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa´an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacħwa a gare shi ba.
23Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashħwa kuma Mũ ne magada.
24Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
25Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
26Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
27Kuma Aljani Mun haliccħ shi daga gabãni, daga wutar (2) iskar zafi.
28Kuma a l?kacin da Ubangijinka ya ce wa mal?´iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙeƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
29"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa(3) a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
30Sai malã´iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
31Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancħwa daga mãsu yin sujadar.
32Ya ce: "Yã Iblĩs mħne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
33Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
34Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
35"Kuma lalle ne akwai la´ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
36Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
37Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
38"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
39Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
40"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
41Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
42"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
43Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma´alkawartarsu gabã ɗaya.
44Tanã da ƙõfõfi bakwai,(1) ga kõwace ƙõfa akwai wani juz´i daga gare su rababbe.
45Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
46"Ku shigħ ta da aminci, kunã amintattu."
47Kuma Muka ɗħbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama ´yan´uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
48Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga cikinta ba.
49Ka bai wa bãyiNa lãbari cħwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
50Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
51Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
52A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
53Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi maka bushãra game da wani yãro masani."
54Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra(1) ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
55Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
56Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
57Ya ce: "To, mħne ne babban al´amarinku? Yã kũ manzanni!"
58Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
59"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
60"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cħwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
61To, a lõkacin da mazannin suka jħ wa mutãnen Lũɗu,
62Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
63Suka ce: "ôa, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
64"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
65"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka umurce ku."
66Kuma Muka hukunta wancan al´amarin zuwa gare shi cħwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankħwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
67Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
68Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
69"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
70Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
71Ya ce: "Ga waɗannan ´ya´yãna (1) idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
72Rantsuwa da(2) rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
73Sa´an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
74Sa´an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
75Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
76Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a għfen wata hanyã tabbatacciya.(3)
77Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
78Kuma lalle ne ma´abũta Al´aika(4) sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
79Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a għfen wani tafarki mabayyani.
80Kuma lalle ne haƙĩƙa ma´abũta Hijiri(5) sun ƙaryata Manzanni.
81Kuma Muka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirħwa daga gare su.
82Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
83Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
84Sa´an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
85Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã´a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
86Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
87Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu(6) da Alƙur´ãni mai girma.
88Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau´i-nau´i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
89Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
90Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,(7)
91Waɗanda suka sanya Alƙur´ãni tãtsuniyõyi.
92To, rantsuwa da Ubangijinka! (1) Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
93Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
94Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
95Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu(2) izgili.
96Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa´an nan da sannu zã su sani.
97Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cħwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
98Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
99Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
Chapter 16 (Sura 16)
1Al´amarin Allah yã zo, sabõda haka kada ku nħmi hanzartãwarsa. Tsarkin Allah ya tabbata, kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka.
2Yanã sassaukar da malã´iku da Rũhi(3) daga umurninSaa kan wanda Yake so daga bãyinSa, cħwa ku yi gargaɗi cħwa: Lalle ne shĩ, bãbu abin bautãwa fãce Ni, sabõda haka ku bĩ Ni da taƙawa.
3Ya halicci sammai da ƙasa da gaskiya. Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka.
4Ya halicci mutum daga maniyyi, sai gã shi yanã mai husũma bayyananniya.
5Da dabbõbin ni´ima, Ya halicce su dõminku. A cikinsu akwai abin yin ɗumi da waɗansu amfãnõni, kuma daga gare su kuke ci.
6Kuma kunã da kyau a cikinsu a lõkacin da suke kõmõwa daga kĩwo da maraice da lõkacin da suke sakuwã.
7Kuma sunã ɗaukar kãyanku mãsu nauyi zuwa ga wani gari, ba ku kasance mãsu isa gare shi ba, fãce da tsananin wahalar rãyuka, Lalle ne Ubangijinka ne, haƙĩƙa, Mai tausayi, Maijin ƙai.
8Kuma da dawãki(1) da alfadarai da jãkuna, dõmin ku hau su, kuma da ƙawa. Kuma Yana halitta abin da ba ku sani ba.
9Kuma ga Allah madaidaiciyar hanya take kuma daga gare ta akwai mai karkacħwa. Kuma da Yã so, dã Ya shiryar da ku gabã ɗaya.
10Shĩ ne Wanda Ya saukar da ruwa daga sama dõminku, daga gare shi akwai abin sha, kuma daga gare shi itãce yake, a cikinsa kuke yin kĩwo.
11Yanã tsirar da shũka game da shi, dõminku zaitũni da dabĩnai da inabai, kuma daga dukan ´yã´yan itãce. Lalle ne a cikin wancan haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke yin tunãni.
12Kuma Ya hõrħ muku dare da wuni da rãnã da watã kuma taurãri hõrarru ne da umurninSa. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke hankalta.
13Kuma abin da Ya halitta muku a cikin ƙasa, yana mai sãɓãnin launukansa. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke tunãwa.
14Kuma Shĩ ne Ya hõrħ tħku dõmin ku ci wani nama sãbõ daga gare shi, kuma kunã fitarwa, daga gare shi, ƙawã wadda kuke yin ado da ita. Kuma kuna ganin jirãge sunã yankan ruwa a cikinsa kuma dõmin ku yi nħman (fatauci) daga falalarSa. Kuma mai yiwuwa ne kuna gõdħwa.
15Kuma Ya jħfa, a cikin ƙasa, tabbatattun duwatsu dõmin kada ta karkata da ku, da kõguna da hanyõyi, ɗammãninku kunã shiryuwa.
16Kuma da waɗansu alãmõmi, kuma da taurãri sunã mãsu nħman shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci).
17Shin, wanda Yake yin halitta yanã yin kama da wanda ba ya yin halitta? Shin fa, bã ku tunãwa?
18Kuma idan kun ƙidãya ni´imar Allah, bã ku iya lissafa ta. Lalle ne Allah, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
19Kuma Allah Yanã sanin abin da kuke asirtãwa da abin da kuke bayyanãwa.
20Kuma waɗanda suke kira, baicin Allah, ba su halicci kõme ba, kuma sũ ne ake halittawa.
21Matattũ ne, bã su da rai, kuma ba su san a wane lõkaci ake tãyar da su ba.
22Abin bautawarku, abin bautãwa ne guda, to, waɗanda ba su yin ĩmãni da Lãhira, zukãtansu mãsu musu ne, kuma su makangara ne.
23Haƙĩƙa, lalle ne, Allah Yanã sanin abin da suke asirtãwa da abin da suke bayyanãwa. Lalle ne Shi, bã Ya Son mãsu girman kai.
24Idan aka ce musu: "Mħne ne Ubangijinku Ya saukar?" Sai su ce: "Tãtsũniyõyin mutãnen farko."
25Dõmin su ɗauki zunubansu cikakku a Rãnar Ƙiyãma, kuma daga zunuban waɗanda suke ɓatarwa bã da wani ilmi ba. To, abin da suke ɗauka na zunubi ya mũnana.
26Lalle ne waɗanda suke a gabãninsu sun yi mãkirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsãshensa,(1) sai rufi ya fãɗa a kansu daga bisansu, kuma azãba ta jħ musu daga inda ba su sani ba.
27Sa´an nan a Rãnar Ƙiyãma (Allah) Yanã kunyatã su, kuma Yanã cħwa: "Inã abõkan tãrayyaTa, waɗanda kuka kasance kunã gãbã a cikin ɗaukaka sha´aninsu?" Waɗanda aka bai wa ilmi suka ce: "Lalle ne wulãkanci a yau da cũta sun tabbata a kan kãfirai."
28Waɗanda malãiku suke karɓar rãyukansu sunã mãsu zãluntar kansu. Sai suka jħfa nħman sulhu (suka ce) "Ba mu kasance muna aikata wani mummũnan aiki ba." Kayya! Lalle Allah ne Masani ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
29Sai ku shiga ƙõfõfin Jahannama, kunã madawwama a cikinta. Sa´an nan tir da mazaunin mãsu girman kai.
30Kuma aka ce wa waɗanda suka yi taƙawa, "Mħne ne Ubangijinku Ya saukar?" Suka ce, "alhħri Ya saukar, ga waɗanda suka kyautata a cikin wannan dũniya akwai wani abu mai kyau, kuma haƙĩƙa, Lãhira ce mafi alhħri." Kuma haƙĩƙa, mãdalla da gidan mãsu taƙawa.
31Gidãjen Aljannar zama sunã shigarsu, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã da abin da suke so a cikinsu. Kamar haka Allah ke sãkã wa mãsu taƙawa.
32Waɗanda malã´iku suke karɓar rãyukansu sunã mãsu jin dãɗin rai, malã´ikun sunã cħwa. "Aminci ya tabbata a kanku. Ku shiga Aljanna sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa."
33Shin sunã jiran wani abu? Fãce malã´iku su jħ musu kõ kuwa umurnin Ubangijinka. Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu, suka aikata. Kuma Allah bai zãlunce su ba, kuma amma kansu suka kasance sunã zãlunta.
34Sai mũnãnan abũbuwan da suka aikata ya sãme su, kuma abin da suka kasance sunã yi na izgili ya wajaba a kansu.
35Kuma waɗanda suka yi shirki suka ce: "Dã Allah Yã so, dã bamu bautã wa kõme ba, baicinSa, mũ ko ubannimmu kuma dã ba mu haramta kõme ba, baicin abin da Ya haramta." Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka aikata. To, shin, akwai wani abu a kan Manzanni, fãce iyarwa bayyananniyã?
36Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al´umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci Ɗãgũtu." To, daga gare su akwai wanda Allah Ya shiryar, kuma daga cikinsu akwai wanda ɓata ta wajaba a kansa. Sai ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa´an nan ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance.
37Idan ka yi kwaɗayi a kan shiryuwarsu, to, lalle ne, Allah bã Ya shiryar da wanda yake ɓatarwa, kuma bã su da waɗansu mataimaka.
38Kuma suka rantse da Allah iyãkar rantsuwarsu (cħwa) Allah bã ya tãyar da wanda yake mutuwa! Na´am, Yanã tãyarwa. Wa´adi ne (Allah) Ya yi a kanSa tabbatacce, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
39Dõmin Ya bayyana musu abin da suke sãɓã wa jũna a cikinsa, kuma dõmin waɗanda suka kãfirta su sani cħwa lalle sũ ne suka kasance maƙaryatã.
40Abin sani kawai, MaganarMu ga wani abu idan Mun nufe shi, Mu ce masa, "Ka kasance; sai yanã kasancħwa.
41Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin sha´anin Allah daga bãyan an zãlunce su, haƙĩƙa Munã zaunar da su a cikin dũniya da alhħri kuma lalle lãdar Lãhira ce mafi girmã, dã sun kasance sunã sani.
42Waɗanda suka yi haƙuri, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara.
43Kuma ba Mu aika daga gabaninka ba, fãce waɗansu mazãje Muna yin wahayi zuwa gare su. Sai ku tambayi mutãnen Ambato idan kun kasance ba ku sani ba.
44Da hujjõji bayyanannu da littattafai kuma Mun saukar da Ambato zuwa gare ka, dõmin ka bayyana wa mutãne abin da aka sassaukar zuwa gare su, kuma don ɗammãninsu su yi tunãni.
45Shin fa, waɗanda suka yi mãkircin mũnãnan ayyuka sun amince da Allah, bã zai shafe ƙasa da su ba ko kuwa azãba bã zã ta je musu daga inda ba su sani ba?
46Ko kuwa Ya kama su a cikin jujjuyawarsu? Sabõda haka ba su zama masu buwãya ba.
47Ko kuwa Ya kama su a kan naƙasa? To, lalle ne Ubangijinka haƙĩƙa Mai tausayi ne, Mai jin ƙai.
48Shin, ba su Iura ba da abin da Allah Ya halitta kõ mene ne inuwõyinsu suna karkata daga dãma da wajãjen hagu, suna masu sujada ga Allah, alhãli suna masu ƙasƙantar da kai?
49Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala´iku, suke yin sujada, kuma bã su kangara.
50Suna tsõron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umuruin su.
51Kuma Allah Ya ce: "Kada ku riƙi abũbuwan bautãwa biyu. Abin sani kawai, wanda ake bautãwa guda ne, sa´an nan sai kuji tsõroNa, Ni kawai."
52Kuma Yana da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, kuma Yana da addini wanda yake dawwamamme. Shin fa, wanin Allah kuke bĩ da taƙãwa?
53Kuma abin da yake a gare ku na ni´ima, to, daga Allah ne. Sa´an nan kuma idan cũta ta shãfeku, to, zuwa gare Shi kuke hargõwa.
54sa´an nan idan Ya kuranye cũtar daga gare ku, sai gã wani ɓangare daga gare ku game da Ubangijinsu sunã shirki.
55Dõmin su kãfirta da abin da Muka bã su. To, ku ji dãɗi, sa´an nan da sannu zã ku sani.
56Kuma sunã sanya rabõ(1) ga abin da ba su sani ba daga abin da Muka azurtã su. Ranstuwa da Allah! Lalle ne zã a tambaye ku daga abin da kuka kasance kunã ƙirƙirãwa.
57Kuma sunã danganta ´ya´ya mãta ga Allah. Tsarkinsa yã tabbata! Kuma sũ ne da abin da suke sha´awa.
58Kuma idan aka yi wa ɗayansu bushãra da mace(2) sai fuskarsa ta wuni baƙa ƙirin, alhãli kuwa yanã mai cike da baƙin ciki.
59Yanã ɓõyħwa daga mutãne dõmin mũnin abin da aka yimasa bushãra da shi. Shin, zai riƙe shi a kan wulãkanci kõ zai turbuɗe shi a cikin turɓãya To, abin da suke hukuntãwa ya mũnana.
60Ga waɗanda ba su yi ĩmãni (3) da Lãhira ba akwai sifar cũta kuma ga Allah akwai sifa mafi ɗaukaka. Kuma shi ne Mabuwãyi, Mai hikima.
61Kuma dã Allah Yanã kãma mutãne da zãluncinsu,(4) dã bai bar wata dabba ba a kan ƙasa. Kuma amma Yanã jinkirta musu zuwa ga ajali ambatacce. Sa´an nan idan ajalinsu ya zo, bã zã a yi musu jinkiri ba kõ da sa´a guda, kuma bã zã su gabãta ba.
62Kuma sunã sanyã wa Allah abin da suke ƙi, kuma harsunansu na siffanta ƙarya cħwa lalle ne sunã da abũbuwa mãsu kyau. Bãbu shakka lalle ne sunã da wuta, kuma lalle sũ, waɗanda ake ƙyãlħwa ne (a cikinta) .
63Rantsuwar Allah! Lalle ne haƙĩƙa Mun aika zuwa ga al´ummomi daga gabãninka, sai Shaiɗan ya ƙawãce musu ayyukansu, sabõda haka shĩ ne majiɓincinsu, a yau, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
64Lalle ba Mu saukar da Littafi ba a kanka, fãce dõmin ka bayyanã musu abin da suka sãɓã wa jũna a cikinsa, kuma dõmin shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni.
65Kuma Allah Yã saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta. Lalle ne a cikin wannan haƙĩƙa akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke saurãre.
66Kuma lalle ne, kunã da abin lũra a cikin dabbõbin ni´ima;Munã shãyar da ku daga abin da yake a cikin cikunansu, daga tsakãnin tukar tumbi da jini nõno tsantsan mai sauƙin haɗiya ga mãsu shã.
67Kuma daga ´ya´yan itãcen dabĩno da inabi. Kunã sãmudaga gare shi, abin mãye(1) da abinci mai kyau. Lalle a cikin wannan, haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke hankalta.
68Kuma Ubangjinka Yã yi wahayi(2) zuwa ga ƙudan zuma cħwa: "Ki riƙi gidãje daga duwãtsu, kuma daga itãce, kuma daga abin da suke ginãwa."
69"Sa´an nan ki ci daga dukan ´ya´yan itãce, sabõda haka ki shiga hanyõyin Ubangijinka, sunã hõrarru." Wani abin shã yanã fita daga cikunanta, mai sãɓãwar launukansa a cikinsa akwai wata warkewa ga mutãne. Lalle ne, a cikin wannan, haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin tunãni.
70Kuma Allah ne Ya halicce ku, sa´an nan Yanã karɓar rãyukanku, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwã zuwa ga mafi ƙasƙncin rãyuwa, dõmin kada ya san kõme a bãyan dã ya zama mai ilmi. Lalle Allah ne Masani Mai ĩkon yi.
71Kuma Allah Ya fifita sãshenku(3) a kan sãshe a arziki. Sa´an nan waɗanda aka fĩfĩta ba su zama mãsu mayar da arzikinsu a kan abin da hannãyensu na dãma suka mallaka ba, har su zama daidai a cikinsa. Shin fa, da ni´imar Allah suke musu?
72Kuma Allah Yã sanya muku mãtan aure daga kãwunanku, kuma Ya sanya muku daga mãtan aurenku ɗiyã da jĩkõki, kuma Ya arzũta ku daga abũbuwa mãsu dãɗi. Shin fa, da ƙarya suke yin ĩmãni, kuma da ni´imar Allah sũ, suke kãfirta?
73Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da yake bã ya mallakar wani arziki dõminsu, daga sammai da ƙasa game da kõme, kuma bã su iyawa (ga aikata kõme) .
74Sa´an nan kada ku bãyar da waɗansu misãlai ga Allah. Lalle ne Allah Yanã sani, kuma kũ, ba ku sani ba.
75Allah Yã buga wani misali da wani bãwa wanda bã ya iya sãmun ĩko a kan yin kõme, da (wani bãwa) wanda Muka azurtã shi daga gare Mu da arziki mai kyau. Sa´an nan shĩ yanã ciyarwa daga arzikin, a asirce da bayyane. Shin sunã daidaita? Gõdiya ta tabbata ga Allah. ôa mafi yawansu ba su sani ba.
76Kuma Allah Ya buga wani misãli, maza biyu, ɗayansu bħbe ne, ba ya iya sãmun ikon yin kõme, kuma shi nauyi ne a kan mai mallakarsa, inda duk ya fuskantar da shi, bã ya zuwa da wani alhħri. Shin, yanã daidaita, shi da (namiji na biyu) wanda yake umurni da a yi ãdalci kuma yanã a kan tafarki madaidaici?
77Kuma ga Allah gaibin(1) sammai da ƙasa yake, kuma al´amarin Sã´a bai zama ba fãce kamar walƙãwar gani, kõ kuwa shĩ ne mafi kusa! Lalle Allah a kan dukan kõme Mai ikon yi ne.
78Kuma Allah ne Ya fitar da ku daga cikunan iyãyenku, ba da kunã sanin kõme ba, kuma Ya sanya muku ji da gannai da zukãta, tsammãninku zã ku gõde.
79Shin ba su ga tsuntsãye(2) ba sunã hõrarru cikin sararin sama bãbu abin da yake riƙe su fãce Allah? Lalle ne a cikin wancan haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni.
80Kuma Allah ne Ya sanya muku daga gidajenku wurin natsuwa, kuma Ya sanya muku daga fatun dabbõbin ni´ima wasu gidãje kunã ɗaukar su da sauƙi a rãnar tafiyarku da rãnar zamanku, kuma daga sũfinsu(1) da gãshinsu da għzarsu (Allah) Ya sanya muku kãyan ɗãki da na jin dãɗi zuwa ga wani lõƙaci.
81Kuma Allah ne Ya sanyã muku inuwa daga abin da Ya halitta, kuma Ya sanyã muku ɗãkuna daga duwãtsu, kuma Ya sanyã muku waɗansu riguna(2) sunã tsare muku zãfi, da waɗansu rĩguna sunã tsare muku makãminku. Kamar wancan ne (Allah) Yake cika ni´imarSa a kanku, tsammãnin ku, kuna sallamawa.
82To, idan sun jũya, to, abin da ya wajaba a kanka, shi ne iyarwã kawai, bayyananniyã.
83Suna sanin ni´imar Allah, sa´an nan kuma sunã musunta, kuma mafi yawansu kãfirai ne.
84Kuma a rãnar da Muke tãyar da mai shaida daga kõwace al´umma, sa´an nan kuma bã zã a yi izni ba ga waɗanda suka kãfirta, kuma ba su zama ana nħman kõmawarsu ba.
85Kuma idan waɗanda suka yi zãlunci suka ga azãba, sa´an nan bã za a saukake ta daga gare su ba, kuma bã su zama anã yi musu jinkiri ba.
86Kuma idan waɗanda suka yi shirka suka ga abũbuwan shirkarsu sai su ce: "Yã Ubangijinmu! Waɗannan ne abũbuwan shirkarmu waɗanda muka kasance munã kira baicinKa". Sai su jħfa magana zuwa gare su, "Lalle ne ku, haƙĩƙa, maƙaryata ne."
87Kuma su shiga nħman sulhu zuwa ga Allah a rãnar nan, kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa ya ɓace daga gare su.
88Waɗanda suka kãfirta kuma suka kange daga hanyar, Alla, Mun ƙãra musu wata azãba bisa ga azãbar, sabõda abin da suka kasance sunã yi na fasãdi.
89Kuma a rãnar da Muke tãyar da shaidu a cikin kõwace al´umma a kansu daga kãwunansu, kuma Muka zo da kai kanã mai bãyar da shaida a kan waɗannan, kuma Mun saussaukar da Littãfi a kanka dõmin yin bãyani ga dukkan kõme da shiriya da rahama da bushãra ga mãsu mĩƙa wuya (Musulmi).
90Lalle Allah nã yin umurni da ãdalci da kyautatãwa, da bai wa ma´abũcin zumunta, kuma yanã hani ga alfãsha da abin da aka ƙi da rarrabe jama´a. Yanã yi muku gargaɗi, ɗammãnin ku, kunã tunãwa.
91Kuma ku cika da alkãwarin(1) Allah idan kun yi alkawari, kuma kada ku warware rantsuwõyinku a bãyan ƙarfafa su, alhãli kuma haƙĩƙa kun sanya Allah Mai lãmuncħwa a kanku. Kuma lalle Allah ne Yake sanin abin da kuke aikatãwa.
92Kuma kada ku kasance kamar wadda ta warware zarenta a bãyan tukka, ya zama warwararku, kunã riƙon rantsuwõyinku dõmin yaudara a tsakãninku, dõmin kasancħwar wata al´umma tãfi rĩba daga wata al´umma! Abin sani kawai Allah Yanã jarrabar ku da shi, kuma lalle ne yanã bayyana muku a Rãnar Ƙiyãma, abin da kuka kasance, a cikinsa, kunã sãɓã wa jũna.
93Kuma dã Allah Ya so, haƙĩ ƙa, dã Ya sanya ku al´umma gudã, kuma Yanã ɓatar da wanda Ya so. Kuma Yanã shiryar da wanda Ya so. Lalle ne anã tambayarku abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
94Kada ku riƙi rantsuwõyinku dõmin yaudara a tsakãninku, har ƙafa ta yi sulɓi a bãyan tabbatarta, kuma ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kange daga hanyar Allah. Kuma kunã da wata azãba mai girma.(1)
95Kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da alkawarin Allah. Lalle ne abin da yake a wurin Allah shi ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kunã sani.
96Abin da yake a wurinku yanã ƙãrħwa, kuma abin da yake a wurin Allah ne mai wanzuwã. Kuma lalle ne, Munã sãka wa waɗanda suka yi haƙuri da lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa.
97Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa.
98Sa´an nan idan ka karantã(2) Alƙur´ãni, sai ka nħmi tsari ga Allah daga shaiɗan jħfaffe.
99Lalle ne shi, bã shi da wani ƙarfi a kan waɗanda suka yi ĩmãni, kuma sunã dõgara ga Ubangijinsu.
100Abin sani kawai ƙarfinsa yanã a kan waɗanda suke jiɓintar sa, kuma waɗanda suke sũ, game da shi, mãsu shirki ne.
101Kuma idan Muka musanya wata ãyã a matsayin wata ãyã, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da Yake saukarwa sai su ce: "Abin sani kawai, kai, maƙirƙiri ne." ôa, mafi yawansu bã sa sani.
102Ka ce: "Rũhul Ƙudusi(3) ne ya sassaukar da shi, daga Ubangijinka da gaskiya, dõmin ya tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma(dõmin) shiriya da bushãra ga Musulmi."
103Kuma lalle ne, haƙĩƙa Munã sanin (cħwa) lalle ne sũ, sunã cħwa, "Abin sani kawai wani mutum ne yake karantar da shi." Harshen wanda suke karkatar da maganar zuwa gare shi, Ba´ajame (1) ne, kuma wannan (Alƙur´ãni) harshe ne Balãrabe bayyananne.
104Lalle ne waɗanda bã su yin ĩmãni da ãyõyin Allah, Allah bã zai shiryar da su ba, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
105Abin sani kawai waɗanda bã su yin ĩmãni da ãyõyin Allah, sũ ne suke ƙirƙira ƙarya. Kuma waɗannan sũ ne maƙaryata.
106Wanda ya kãfirta da Allah daga bãyan ĩmãninsa,(2) fãce wanda aka tĩlasta alhãli kuwa zũciyarsa tanã natse da ĩmãni kuma wanda ya yi farin ciki da kãfirci, to, akwai fushi a kansa daga Allah, kuma sunã da wata azãba mai girma.
107Waɗancan ne kãfirai dõmin sun fĩfĩta son dũniya a kan Lãhira, kuma lalle ne Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai.
108Waɗancan ne waɗanda Allah Ya bice hasken zukãtansu da jinsu da gannansu. Kuma waɗancan sũ ne gafalallu.
109Bãbu shakka lalle ne a Lãhira sũ ne mãsu hasãra.
110Sa´an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka yi hijirã daga bãyan an fitine su, sa´an nan kuma suka yi jihãdi, kuma suka yi haƙuri, lalle ne Ubangijinka, daga bãyanta(3) haƙĩƙa Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
111A rãnar da kõwane rai zai je yanã jãyayyar tunkuɗħwa daga kansa, kuma a cika wa kõwane rai (sakamakon) abin da ya aikata, kuma sũ bã zã a zãlunce su ba.
112Kuma Allah Ya buga misãli,(1) wata alƙarya ta kasance amintacciyã, natsattsiyã, arzikinta yanã je mata a wadãce daga kõwane wuri sai ta kãfirta da ni´imõmin Allah, sabõda haka Allah ya ɗanɗana mata tufãfin yunwa da tsõro, sabõda abin da suka kasance sunã sanã´antãwa.
113Kuma lalle ne haƙĩƙa wani Manzo daga gare su, ya jħmusu, sai suka ƙaryata shi, sabõda haka azãba ta kãma su, alhãli kuwa sũ ne mãsu zãlunci.
114Sa´an nan ku ci daga(2) abin da Allah Ya azurta ku da shi, halas, kuma mai dãɗi, kuma ku gõde wa ni´imar Allah idan kun kasance shi kuke bautãwa.
115Abin sani kawai (Allah) Ya haramta(3) muku mussai da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah game da shi. Sa´an nan wanda aka tĩlasta a kan jama´a kuma baicin mai zãlunci, to, lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.
116Kuma kada ku ce, dõmin abin da harsunanku suke siffantawa da ƙarya, "Wannan halas ne, kuma wannan harãmun ne." Dõmin ku ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne, waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah bã zã su ci nasara ba.
117Jin dãɗi ne kaɗan. Kuma sunã da wata azãba mai raɗaɗi.
118Kuma kan waɗanda suka tũba (Yãhũdu) Mun haramta abin da Muka bãyar da lãbari a gare ka daga gabãni,(4) kuma ba Mu zãlunce su ba, amma sun kasance kansu suke zãlunta.
119Sa´an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka aikata mummunan aiki(1) da jãhilci, sa´an nan suka tũba daga bãyan wancan, kuma suka gyãra, lalle ne Ubangijinka, daga bãyanta haƙĩƙa Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
120Lalle ne Ibrãhĩm(2) ya kasance shũgaba, mai ƙasƙantar da kai ga Allah, mai karkatã zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba.
121Mai gõdiya(3) ga ni´imominSa (Allah), Ya zãɓe shi, kuma Ya shiryar da shi zuwa ga tafarki madaidaici.
122Kuma Muka ba shi alhħri a cikin dũniya. Kuma lalle shĩ, a Lãhira, yanã daga sãlihai.
123Sa´an nan kuma Muka yi wahayi zuwa gare ka (cħwa), "Ka(4) bi aƙĩdar Ibrahĩm, mai karkatã zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba.´
124Abin sani kawai, an sanya Asabar a kan waɗanda suka sãɓã wa jũna a cikin sha´aninsa.(5) Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa,Yanã yin hukunci a tsakaninsu a Rãnar Ƙiyãma a cikin abin da suka kasance a cikinsa sunã sãɓã wa jũnã.
125Ka yi kira zuwa ga hanyar Ubangijinka da hikima(6) da wa´azi mai kyau kuma ka yi jãyayya da su da magana wadda take mafi kyau. Lalle ne Ubangijinka Shĩ neMafi sani ga wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
126Kuma idan kuka sãka(7) wa uƙũba to ku sãka wa uƙũba da misãlin abin da aka yi muku uƙũbar da shi. Kuma idan kun yi haƙuri, lalle shĩ ne mafi alhħri ga mãsu haƙuri.
127Kuma ka yi haƙuri, kuma haƙurinka bã zai zama ba fãce dõmin Allah, kuma kada ka yi baƙin ciki sabo da su, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke yi na mãkirci.
128Lalle Allah Yanã tãre da waɗanda suka yi taƙawa da waɗanda suke sũ mãsu kyautatãwa ne.
Chapter 17 (Sura 17)
1Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare(1) da bãwanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nĩsa(2) wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ãyõyinMu. Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani.
2Kuma Mun bai wa Mũsã(3) littafi, kuma Mun sanya shi shiriya ga Banĩ Isrã´ila, cħwa kada ku riƙi wani wakĩli baiciNa.
3Zuriyar waɗanda Muka ɗauka tãre da Nũhu. Lalle ne shi ya kasance wani bãwa mai gõdiya.
4Kuma Mun hukunta zuwa ga Bani Isrã´ĩla a cikin Littãfi, cewa lalle ne, kunã yin ɓarna a cikin ƙasa sau biyu, kuma lalle ne kunã zãlunci, zãlunci mai girma.
5To idan wa´adin na farkonsu yajħ, za Mu aika, a kanku waɗansu bãyi(4) Nãmu, ma´abũta yãƙi mafĩ tsanani, har su yi yãwo a tsakãnin gidãjenku, kuma yã zama wa´adi abin aikatawa.
6Sa´an nan kuma Mu mayar da ɗauki a gare ku a kansu, kuma Mu taimake ku da dũkiyõyi da ɗiya kuma Mu sanya ku mafiya yawan mãsu fita yãƙi.
7Idan kun kyautata, kun kyautata dõmin kanku, kuma idan kun mũnana to dõmĩnsu. Sa´an nan idan wa´adin na ƙarshe(5) ya jħ, (za su je) dõmin su baƙanta fuskokinku, kuma su shiga masallaci kamar yadda suka shige shi a farkon lõkaci, kuma dõmin su halakar da abin da suka rinjaya a kansa, halakarwa.
8Akwai tsammãnin Ubangijinku Ya yi muku rahama. Kuma idan kun sãke Mu sãke. Kuma Mun sanya Jahannama matsara ga kãfirai.
9Lalle ne wannan Alƙur´ãni yanã shiryarwa ga (hãlaye) waɗanda suke mafi daidaita(1) kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cħwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."
10Kuma lalle ne, waɗanda ba su yin ĩmãni da Lãhira, Mun yi musu tattalin wata azãba mai raɗaɗi.
11Kuma mutum yanã(2) yin addu´a da sharri kamar addu´arsa da alhħri, kuma mutum ya kasance mai gaggãwa.
12Kuma Mun sanya dare da rãna, ãyõyi biyu, sa´an nan Muka shãfe ãyar dare, kuma Muka sanya ãyar rãna mai sanyãwa a yi gani, dõmin ku nħmi falala daga Ubangijinku, kuma dõmin ku san ƙidãyar shħkara da lissafi. Kuma dukan kõme Mun bayyana shi daki-dakin bayyanãwa.
13Kuma kõwane mutum Mun lazimta masa abin rekõdinsa a cikin wuyansa, kuma Mu fitar masa a Rãnar Ƙiyãma da littãfi wanda zai haɗu da shi buɗaɗɗe.
14"Karanta Littãfinka. Ranka ya isa ya zama mai hisãbi a kanka a yau."
15Wanda ya nħmi shiryuwa, to, ya nħmi shiryuwa ne dõmin kansa kawai kuma wanda ya ɓace, to, ya ɓace ne a kansa kawai kuma rai mai ɗaukar nauyi bã ya ɗaukar nauyin wani ran, kuma ba Mu zama mãsu yin azãba ba, sai Mun aika wani Manzo.
16Kuma idan Mun yi nufin Mu halakar da wata alƙarya, sai Mu umurci mawadãtanta, har su yi fãsikanci a cikinta, sa´an nan maganar azãba ta wajaba a kanta, sa´an nan Mu darkãke ta, darkãkħwa.
17Kuma da yawa Muka halakar da al´ummomi a bãyan Nũhu. Kuma Ubangijinka Ya isa ya zama Mai ƙididdigewa ga zunubban bãyinSa, Mai gani.
18Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa,(1) sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa´an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa.
19Kuma wanda ya nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita irin aikinta alhãli kuwa yanã mũmĩni, to, waɗannan aikinsu ya kasance gõdadde.
20Dukkansu Munã taimakon waɗannan da waɗancan daga kyautar Ubangijinka, kuma kyautar Ubangijinka ba ta kasance hananna ba.
21Ka duba yadda Muka fĩfĩtar da sãshensu a kan sãshe! Kuma lalle ne Lãhira ce mafi girman darajõji, kuma mafi girman fĩfĩtãwa.
22Kada ka sanya wani abin bautawa na dabam tãre da Allah har ka zauna kana abin zargi, yarɓaɓɓe.
23Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kuma game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu ´tir´ kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci.
24Kuma ka sassauta musu fikãfikan tausasãwa na rahama. Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka yi musu rahama, kamar yadda suka yi rħnõna, ina ƙarami."
25Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da yake a cikin rãyukanku. Idan kun kasance sãlihai to lalle ne shĩ Ya kasance ga mãsu kõmawa gare Shi, Mai gãfara.
26Kuma ka bai wa ma´abũcin zumunta hakkinsa(2) da miskĩni da ɗan hanya. Kuma kada ka bazzara dũkiyarka, bazzarãwa.
27Lalle ne mubazzarai sun kasance ´yan´uwan shaiɗanu. Kuma Shaiɗan ya kasance ga Ubangijinsa, mai yawan kãfirci.
28Ko dai ka kau da kai daga gare su dõmin nħman rahama daga Ubangijinka, wadda kake fãtanta, to sai ka gaya musu magana mai laushi.
29Kuma kada ka sanya hannunka ƙuƙuntacce zuwa ga wuyanka, kuma kada ka shimfiɗa shi dukan shimfiɗãwa har ka zama abin zargi, wanda ake yanke wa.(1)
30Lalle ne Ubangijinka Yanã shimfiɗa arzĩki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuƙuntãwa. Lalle Shi, Yã kasance Mai sani ga bãyinSa, Mai gani.
31Kuma kada ku kashe ´yã´yanku dõmin tsõron talauci. Mu ne ke arzũta su, su da ku. Lalle ne kashe su yã kasance kuskure babba.
32Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance alfãsha ce kuma tã mũnãna ga zama hanya.
33Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da haƙƙi, kuma wanda aka kashe, yanã wanda aka zãlunta to, haƙĩƙa Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai dai kada ya ƙħtare haddi a cikin kashħwar. Lalle shĩ ya kasance wanda ake taimako.
34Kuma kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce dai da sifa wadda take ita ce mafi kyau, har ya isa ga mafi ƙarfinsa. Kuma ku cika alkawari. Lalle alkawari yã kasance abin tambayãwa ne.
35Kuma ku cika mũdu idan kun yi awo, kuma ku auna nauyi da sikħli madaidaici. Wancan ne mafi alhħri, kuma mafi kyau ga fassara.
36Kuma kada ka bi abin da bã ka da ilmi game da shi. Lalle ne jĩ da gani da zũciya, dukan waɗancan (mutum) yã kasance daga gare shi wanda ake tambaya.
37Kuma kada ka yi tafiya a cikin ƙasa da alfahari. Lalle kai bã zã ka hũda ƙasa ba kuma bã zã ka kai a duwãtsu ba ga tsawo.
38Dukan wancan mai mũninsa yã kasance abin ƙyãma a wurin Ubangijinka.
39Wancan yãnã daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah har a jħfa ka a cikin Jahannama kanã wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗħwa(1)
40Shin fa, Ubangijinku Ya zãɓe ku da ɗiya maza ne, kuma Ya riƙi ´ya´ya mãta daga malã´iku?(2) Lalle ne kũ, haƙĩƙa, kunã faɗar magana mai girma!
41Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarrafa bayãni a cikin wannan Alƙur´ãni dõmin su yi tunãni, kuma bã ya ƙãra musu kõme fãce gudu.
42Ka ce: "Dã akwai waɗansu abũbuwan bautãwa tãre da shi, kamar yadda suka faɗa, a lõkacin, dã (abũbuwan bautãwar) sun nħmi wata hanya(3) zuwa ga Ma´abũcin Al´arshi."
43TsarkinSa yã tabbata kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke faɗã, ɗaukaka mai girma.
44Sammai bakwai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sunã yi Masa tasbĩhi. Kuma bãbu wani abu fãce yanã tasbĩhi game da gõde Masa, kuma amma ba ku fahimtar tasbĩhinsu. Lalle ne shĩ, Ya kasance Mai haƙuri ne, Mai gãfara.
45Kuma idan ka karanta Alƙur´ani,(4) sai Mu sanya a tsakãninka da tsakanin waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira wani shãmaki mai suturcħwa.
46Kuma Mu sanya marufai a kan zukãtansu dõmin kada su fahimce shi, da, wani nauyi a cikin kunnuwansu, kuma idan ka ambaci Ubangijinka, a cikin Alƙur´ãni shĩ kaɗai, sai su jũya a kan bayayyakinsu dõmin gudu.
47Mũ ne Mafi sani game da abin da suke saurãre da shi a lõkacin da suke yin saurãren zuwa gare ka, kuma a lõkacin da suke mãsu gãnãwa a tsakãninsu a lõkacin da azzãlumai suke cħwa, "Bã ku biyar kõwa fãce wani namiji sihirtacce."
48Ka dũba yadda suka buga maka misãlai, sai suka ɓace bã su iya sãmun hanya.
49Kuma suka ce: "Shin, idan mun kasance ƙasũsuwa da, niƙaƙƙun gaɓãɓuwa ashe, lalle ne mũ haƙĩƙa, waɗanda ake tãyarwa ne a wata halitta sãbuwa?"
50Ka ce: "Ku kasance duwãtsu ko kuwa baƙin ƙarfe."
51"Kõ kuwa wata halitta daga abin da yake da girma a cikin ƙirazanku." To zã su ce "Wãne ne zai mayar da mu?" Ka ce: "Wanda Ya ƙaga halittarku a farkon lõkaci." To, zã su gyaɗa kansu zuwa gare ka, kuma sunã cħwa, "A yaushe ne shi?" Ka ce: "Akwai tsammãninsa ya kasance kusa."
52"A rãnar da Yake kiran ku, sa´an nan ku riƙa karɓãwa game dã gõde Masa, kuma kunã zaton ba ku zauna ba fãce kaɗan."
53Kuma ka cħ wa bãyiNa, su faɗi kalma(1) wadda take mafi kyau. Lalle ne Shaiɗan yanã sanya ɓarna a tsakãninsu. Lalle ne Shaiɗan ya kasance ga mutum, maƙiyi bayyananne.
54Ubangijinku ne Mafi sani game da ku. Idan Ya so, zai yi muku rahama, kõ kuwa idan Yã so zai azabtãku. Kuma ba Mu aika ka kanã wakĩli a kansu ba.
55Kuma Ubangijinka ne Mafi sani game da wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun fĩfĩta sãshen Annabãwa a kan sãshe kuma Mun bai wa Dãwũda Zabũra.(2)
56Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya, baicinSa." To, ba su mallakar kuranyħwar cũta daga gare ku, kuma haka jũyarwa."(3)
57Waɗancan, waɗanda suke kiran,(4) sunã nħman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce.
58Kuma bãbu wata alƙarya fãce, Mu ne mãsu halaka ta a gabãnin Rãnar Ƙiyãma kõ kuwa Mũ mãsu azãbta ta ne da azãba mai tsanani. Wancan ya kasance a cikin littãfi rubũtacce.
59Kuma bãbu abin da ya hana Mu, Mu aika da ãyõyi fãce sabõda mutãnen farko sun ƙaryata game da su. Kuma Mun bai wa Samũdãwa tãguwa, ãyã bayyananna, sai suka yi zãlunci game da ita. Kuma bã Mu aikãwa da ãyõyi fãce dõmin tsõratarwa.
60Kuma a lõkacin da Muka ce maka, "Lalle ne Ubangijinka Yã kħwaye mutãne." Kuma ba Mu sanya abin da ka gani wanda(1) Muka nũna maka ba, fãce dõmin fitina ga mutãne, da itãciya wadda aka la´anta a cikin Alƙur´ani. Kuma Munã tsõratar da su, sa´an nan (tsõratarwar) bã ta ƙãra su fãce da kangara mai girma.
61Kuma a lõkacin(2) da Muka cħ wa malã´iku, "Ku yi sujada ga Ãdamu," sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa, ya ce: "shin, zan yi sujada ga wanda ka(3) halitta shi yanã lãka?"
62Ya ce: "Shin, kã gan ka(4) ! Wannan wanda ka girmama a kaina, lalle ne idan ka jinkirtã mini zuwa ga Rãnar Ƙiyãma lalle ne, zan tumɓuke zuriyarsa, fãce kaɗan."
63Ya ce: "Ka tafi. Sa´an nan wanda ya bĩ ka daga gare su, to, Jahannama ce sakamakonku, (Mu ba ku shi) sakamako cikakke."
64"Kuma ka rikitar da wanda ka sãmi ĩko a kansa, daga gare su, da sautinka, kuma ka yi hari a kansu da dawãkinka da dãkãrunka kuma ka yi tãrħwa da su a cikin dũkiyõyi da ɗiyã, kuma ka yi musu wa´adi. Alhãli kuwa Shaiɗan bã ya yi musu wa´adin kõme fãce da ruɗi."
65"Lalle ne bãyiNa, bã ka da wani ƙarfi a kansu. Kuma Ubangijinka Ya isa Ya zama wakĩli."
66Ubangijinku ne Yake gudãnar da jirgi a cikin tħku, dõmin ku nema daga falalarSa. Lalle ne Shĩ, Yã kasance a gare ku Mai jin ƙai.
67Kuma idan cũta ta shãfe ku, a cikin tħku, sai wanda kuke kira ya ɓace fãce Shi. To, a lõkacin da Ya tsirar da ku zuwa, ga tudu sai kuka bijire. Kuma mutum ya kasance mai yawan butulci.
68Shin fa kun amince cħwa (Allah) bã Ya shãfe għfen ƙasa game da ku kõ kuwa Ya aika da iska mai tsakuwa a kanku, sa´an nan kuma bã zã ku sãmi wani wakĩli ba dõminku?
69Ko kun amince ga Ya mayar da ku a cikin tħkun a wani lõkaci na dabam, sa´an na Ya aika wata gũguwa mai karya abũbuwa daga iska, har ya nutsar da ku sabõda abin da kuka yi na kãfirci? Sa´an nan kuma bã ku sãmun mai bin hakki sabõda ku, a kanMu, game da Shi.
70Kuma lalle ne Mun girmama ´yan Adam,(1) kuma Muka ɗauke su a cikin ƙasa da tħku kuma Muka azurta su daga abũbuwa mãsu dãɗi kuma Muka fĩfĩta su a kan mãsu yawa daga waɗanda Muka halitta, fĩfĩtãwa.
71A rãnar da Muke kiran(2) kõwane mutãne da lĩmãminsu to, wanda aka bai wa littafinsa a dãmansa, to, waɗannan sunã karãtun littãfinsu, kuma bã a zãluntar su da zaren bãkin gurtsin dabĩno.
72Kuma wanda ya kasance makãho(3) a cikin wannan sabõda haka shi a Lãhira makãho ne kuma mafi ɓata ga hanya.
73Kuma lalle ne sun yi kusa haƙĩƙa, su fitinħ ka daga abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, dõmin ka ƙirƙira waninsa a gare Mu, a lõkacin, haƙĩƙa, dã sun riƙe ka masoyi.
74Kuma bã dõmin(4) Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙĩƙa, dã kã yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan.
75A lõkacin, lalle ne, dã Mun ɗanɗana maka ninkin azãbar rãyuwa da ninkin azãbar mutuwa, sa´an nan kuma bã zã ka sãmi mataimaki ba a kanMu.
76Kuma lalle ne, sun(1) yi kusa, haƙĩƙa, su tãyar da hankalinka daga ƙasar, dõmin su fitar da kai daga gare ta. Kuma a lõkacin, bã zã su zauna ba a kan sãɓãninka fãce kaɗan.
77Hanyar waɗanda, haƙĩƙa, Muka aika a gabãninka, daga ManzanninMu, kuma bã zã ka sãmi jũyarwa ba ga hanyarMu.
78Ka tsayar da salla(2) a karkatar rãnã zuwa ga duhun dare da lõkacin fitar alfijir lalle ne karãtun fitar alfijir(3) ya kasance wanda ake halarta.
79Kuma da dare, sai ka yi hĩra(4) da shi (Alƙur´ãni) akan ƙãri gare ka. Akwai tsammãnin Ubangijinka Ya tãyar da kai a wani matsayi gõdadde.
80Kuma ka ce: "Yã Ubangijĩna!(5) Ka shigar, da ni shigar gaskiya, kuma Ka fitar da ni fitar gaskiya. Kuma Ka sanya mini, daga gunKa, wani ƙarfi mai taimako."
81Kuma ka ce: "Gaskiya tã zo, kuma ƙarya ta lãlãce. Lalle ne ƙarya ta kasance lãlãtacciya."
82Kuma Munã sassaukarwa daga Alƙur´ãni, abin da yake waraka ne da rahama ga mũminai. Kuma bã ya ƙãra wa azzãlumai (kõme) fãce hasãra.
83Kuma idan Muka yi ni´ima a kan mutum,(6) sai ya hinjire, kuma ya nĩsanta da gefensa, kuma idan sharri ya shãfe shi, sai ya kasance mai yanke ƙauna.
84Ka ce: "Kõwa ya yi aiki a kan hanyarsa. Sa´an nan Ubangijinka ne Mafi sani ga wanda yake mafi shiryuwa ga hanya."
85Sunã tambayar ka ga rũhi. Ka ce: "Rũhi daga al´amarin Ubangijina ne, kuma ba a bã ku (kõme) ba daga ilmi fãce kaɗan."
86Kuma lalle ne idan Mun so, haƙĩƙa, Munã tafiya da abinda Muka yi wahayi zuwa gare ka. Sa´an nan kuma bã za ka sãmi wani wakĩli ba dõminka game da shi a kanMu.
87Fãce da rahama daga Ubangijinka. Lalle ne falalarSa ta kasance mai girma a kanka.
88Ka ce: "Lalle ne idan mutãne da aljannu sun tãru a kan su zo da misãlin wannan Alƙur´ãni bã zã su zo da misãlinsa ba, kuma kõ dã sãshinsu yã kasance, mataimaki ga sãshi."
89Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun caccanza dõmin mutãne, a cikin wannan Alƙur´ãni, daga kõwane misãli sai mafi yawan mutãne suka ƙi (kõme) fãce kãfirci,
90Kuma suka ce: "Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka sai kã ɓuɓɓugar(1) da idan ruwa daga ƙasa.
91"Kõ kuma wata gõna daga dabĩnai da inabi ta kasance a gare ka. Sa´an nan ka ɓuɓɓugar da ƙõramu a tsakãninta ɓuɓɓugarwa."
92"Kõ kuwa ka kãyar da sama a kanmu kaɓukka kõ kuwa ka zo da Allah, da malã´iku banga-banga."
93"Kõ kuwa wani gida na zĩnãriya ya kasance a gare ka, kõ kuwa ka tãka a cikin sama. Kuma bã zã mu yi ĩmãni ba ga tãkawarka, sai ka sassaukõ da wani littãfi a kanmu, munã karantã shi." Ka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijĩna! Ban kasance ba fãce mutum, Manzo."
94Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni, a lõkacin da shiriya ta jħ musu, fãce sun ce, "Shin, Allah zai aiko mutum ya zamo yana Manzo."
95Ka ce: "Dã malã´iku sun kasance a cikin ƙasa, kuma sunã tafiya, sunã masu natsuwa, lalle ne dã mun saukar da malã´ika daga sama ya zama manzo a kansu."
96Ka ce: "Allah Yã isa zama shaida a tsakãnina da ku. Lalle Shi Ya kasance ga bãyinsa, mai ƙididdigewa ne Mai gani."
97Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, shĩ ne shiryayye, kuma wanda Ya ɓatar to bã zã ka sãmi waɗansu masõya gare su ba baicinSa. Kuma Munã tãra su a Rãnar Ƙiyãma a kan fuskõkinsu, sunã makãfi, kuma bħbãye da kurãme. Matattararsu Jahannama ce, kõ da yaushe ta bice, sai Mu ƙãra musu wata wuta mai tsanani.
98Wancan ne sãkamakonsu sabõda lalle sũ, sun kãfirta da ãyõyinMu, kuma suka ce: "Shin idan muka kasance ƙasũsuwa da nĩƙaƙƙun gaɓũɓuwa, shin lalle mũ, haƙĩka, waɗanda ake tãyarwa ne a cikin wata halitta sãbuwa?"
99Shin, kuma ba su ganĩ(1) ba (cħwa) lalle ne Allah, wandaYa halicci sammai da ƙasa, Mai ikon yi ne a kan Ya halicci misãlinsu? Kuma Ya sanya wani ajali wanda bãbu kõkwanto a cikinsa? Sai azzãlumai suka ƙi fãce kãfirci.
100Ka ce: "Dã dai kũ, kunã mallakar(2) taskõkin rahamar Ubangijĩna, a lõkacin, haƙĩƙa dã kun kãme dõmin tsõron ƙãrħwar taskõkin. Kuma mutum yã kasance mai ƙwauro ne."
101Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun bai wa Mũsã ãyõyi(3) guda tara bayyanannu, sai ka tambayi Banĩ Isrã´ila, a lõkacin da ya jħ musu, sai Fir´auna ya ce masa, "Lalle nĩ, inã zaton ka, ya Mũsã, sihirtacce."
102Ya ce: "lalle ne haƙĩƙa ka sani bãbu wanda ya saukar da waɗannan, fãce Ubangijin sammai da ƙasa dõmĩn su zama abũbuwan lũra. Kuma lalle ne ni, haƙĩƙa, ina zaton ka, yã Fir´auna, halakakke."
103Sai ya yi nufin fitar da su daga ƙasar, sai Muka nutsar da shi, shi da wanda yake tãre da shi gabã ɗaya.
104Kuma Muka ce: daga bãyansa ga Banĩ Isrã´ĩla, "Ku zauni ƙasar. Sa´an nan idan wa´adin ƙarshe ya zo, zã Mu jħ da ku jama´a-jama´a."(4)
105Kuma da gaskiya Muka saukar da shi, kuma da gaskiya ya sauka. Kuma ba Mu aike ka ba fãce kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi.
106Kuma yanã abin karãtu Mun rarraba shi dõmin ka karanta shi ga mutane a kan jinkiri kuma Mun sassaukar da shi sassaukarwa.(1)
107Ka ce: "Ku yi ĩmãni(2) da Shi, ko kuwa kada ku yi ĩmãni, lalle ne waɗanda aka bai wa ilmi daga gabãninsa, idan anã karãtunsa a kansu, sunã fãɗuwa ga haɓõɓinsu, sunã mãsu sujada."
108"Kuma sunã cħwa: Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle ne wa´adin Ubangijinmu ya kasance, haƙĩƙa ,abin aikatãwa."
109Kuma sunã fãɗuwa ga haɓõɓinsu sunã kũka, kuma yanã ƙara musu tsõro.
110Ka ce: "Ku kirayi Allah(3) kõ kuwa ku kirãyi Mai rahama. Kõwane kuka kira to Yanã da sũnãye mafi kyau. Kuma, kada ka bayyana(4) ga sallarka, kuma kada ka ɓõye ta. Ka nħmi hanya a tsakãnin wancan."
111Kuma ka ce: "Gõdiyã(5) ta tabbata ga Allah wanda bai riƙi ɗã ba kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa, kuma wani masõyi sabõda wulãkancin bai kasance a gare Shi ba." Kuma ka girmama Shi, girmamãwa.
Chapter 18 (Sura 18)
1Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bãwansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi.
2Madaidaici, dõmin Ya yi gargaɗi da azãba mai tsanani daga gare shi, kuma Ya yi bushãra ga mũminai, waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai da (cħwa) sunã da wata lãdã mai kyau.
3Sunã mãsu zama a cikinta har abada.
4Kuma Ya yi gargaɗi ga waɗanda(6) suka ce: "Allah yanã da ɗa."
5Ba su da wani ilmi game da wannan magana, kuma iyãyensu bã su da shi, abin da ke fita daga bãkunansu ya girma ga ya zama kalmar faɗa! Ba su faɗan kõme fãce ƙarya.
6To, kã yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai dõmin ba su yi ĩmãni da wannan lãbãri ba sabõda baƙin ciki.
7Lalle ne Mũ, Mun sanya abin da ke kan ƙasa wata ƙawa(1) ce gare ta, dõmin Mu jarraba su; wanne daga cikinsu zai zama mafi kyau ga aiki.
8Kuma lalle Mũ, Mãsu sanya abin da ke a kanta (ya zama) turɓãya ƙeƙasasshiya ne.
9Ko kuwa kã yi zaton cħwa ma´abũta kõgo(2) da allo sun kasance abin mãmãki daga ãyõyin Allah?
10A lõkacin da samarin suka tattara zuwa ga kõgon, sai suka ce: "Ya Ubangijinmu!(3) Ka bã mu wata rahama daga gare Ka, kuma Ka sauƙaƙe mana (sãmun) shiriya daga al´amarinmu."
11Sai Muka yi dũka a kan kunnunwansu,(4) a cikin kõgon, shħkaru mãsu yawa.
12Sa´an nan Muka tãyar da su, dõmin Mu san wane ɗayan ƙungiyõyin biyu suka fi lissãfi ga abin da suka zauna na lõkacin.
13Mu ne ke jħranta maka lãbãrinsu da gaskiya. Lalle ne sũ, waɗansu samãri ne. Sun yi ĩmãni da Ubangijinsu, kuma Muka ƙãra musu wata shiriya.
14Kuma Muka ɗaure a kan zukãtansu, a lõkacin da suka tsayu, sa´an nan suka ce: "Ubangijinmu Shĩ ne Ubangijin sammai daƙasa. Bã zã mu kirãyi waninSa abin bautawa ba. (Idan mun yi haka) lalle ne, haƙĩƙa, mun faɗi abin da ya ƙħtare haddi a sa´an nan."
15"Ga waɗannan mutãnenmu sun riƙi waninSa abin bautãwa! Don me bã su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar) ? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙãga ƙarya ga Allah?"
16"Kuma idan kun nĩsance su sũ da abin da suke bautãwa, fãce Allah, to, ku tattara zuwa ga kõgon sai Ubangijinku Ya watsa muku daga rahamarSa kuma Ya sauƙaƙe muku madõgara daga al´amarinku."
17Kuma kanã ganin rãnã idan ta fito tanã karkata daga kõgonsu wajen dãma kuma idan ta fãɗi tanã gurgura su wajen hagu, kuma su, sunã a cikin wani fili daga gare shi. Wannan abu yanã daga ãyõyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to shĩ ne mai shiryuwa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmar masa wani majiɓinci mai shiryarwa ba.
18Kuma kanã zaton su farkakku ne, alhãli kuwa sũ mãsu barci ne. Munã jũya su wajen dãma da wajen hagu, kuma karensu yanã shimfiɗe da zirã´õ´in ƙafãfuwansa ga farfãjiya (ta kõgon). Dã ka lħka (a kan) su (dã) lalle ne, ka jũya daga gare su a guje kuma (dã) lalle ne ka cika da tsõro daga gare su.
19Kuma kamar wannan ne Muka tãyar da su, dõmin(1) su tambayi jũna a tsakãninsu. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Mħne ne lõkacin da kuka zauna?" Suka ce: "Mun zauna yini ɗaya ko sãshen yini." Suka ce: "Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da kuka zauna. To, ku aika da ɗayanku, game da azurfarku wannan, zuwa ga birnin.(2) Sai ya dũba wanne ne mafi tsarki ga abin dafãwa, sai ya zo muku da abinci daga gare shi. Kuma sai ya yi da hankali, kada ya sanar da ku ga wani mutum."
20"Lalle ne sũ idan sun kãmã ku, zã su jħfħ ku, kõ kuwa su mayar da ku a cikin addininsu kuma bã zã ku sãmi babban rabo ba, a sa´an nan har abada."
21Kuma kamar wancan ne, Muka nũna su (gare su) dõmin su san lalle wa´adin Allah gaskiya ne, kuma lalle ne Sa´a bãbu shakka a cikinta. A lõkacin da suke jãyayyar al´amarinsu a tsakãninsu(1) sai suka ce: "Ku gina wani gini a kansu, Ubangijinsu ne Mafi sani game da su." Waɗanda suka rinjãya a kan al´amarinsu suka ce: "Lalle mu riƙi masãllãci a kansu."
22Zã su ce: "Uku ne da na huɗunsu karensu."Kuma sunã cħwa, "Biyar ne da na shidansu karensu," a kan jĩfa a cikin duhu. Kuma sunã cħwa, "Bakwaine da na takwas ɗinsu karensu. "Ka ce: "Ubangijĩna(2) ne Mafi sani ga ƙidãyarsu, bãbu wanda ya san su fãce kaɗan. "Kada ka yi jãyayya a cikin al´amarinsu, sai jayayya bayyananna. Kuma kada ka yi fatawa(3) ga kõwa daga gare su a cikin al´amarinsu.
23Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatãwa ne ga wancan a gõbe."
24Fãce idan Allah Ya so. Kuma ka ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: "Ɗammãni ga Ubangijĩna, Ya shiryar da ni ga abin da yake shi ne mafi kusa ga wannan na shiriya."
25Kuma suka zauna a cikin kõgonsu shħkaru ɗarĩ uku kuma suka daɗa tara.
26Ka ce: "Allah ne Mafi sani ga abin da suka zauna. Shĩ ne da (sanin) gaibin sammai da ƙasa. Mene ne ya yi ganinSa da jinSa! Bã su da wani majiɓinci baicinSa kuma bã Ya tãrayya da kõwa a cikin hukuncinsa."
27Ka karanta abin da aka yi wahayi zuwa gare ka, na littãfin Ubangijinka. Bãbu mai musanyãwa ga kalmõminSa kuma bã zã kã sãmi wata madõgara ba daga waninsa.
28Ka haƙurtar da ranka tãre da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa. Kuma kada idãnunka su jũya daga barinsu, kanã nufin ƙawar rãyuwar dũniya.(1) Kuma kada ka bi wanda Muka shagaltar da zũciyarsa daga hukuncinMu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhãli kuwa al´amarinsa ya kasance yin ɓarna.
29Kuma ka ce: "Gaskiya daga Ubangijinku take." Sabõda haka wanda ya so, to, ya yi ĩmãni, kuma wanda ya so, to, ya kãfirta. Lalle ne Mũ, Mun yi tattali dõmin azzãlumai wata wuta wadda shãmakunta, sun ƙħwaye da su. Kuma idan sun nħmi taimako sai a taimake su da wani ruwa kamar dabzar mai, yanã sõye fuskõki. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi mũnin zama mahũtarsu.
30Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai lalle ne Mũ bã Mu tõzartar da lãdar wanda ya kyautata aiki.
31Waɗannan sunã da gidãjen Aljannar zama, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu, anã sanya musu ƙawa, a cikinsu, daga mundãye na zinariya, kuma sunã tufantar waɗansu tũfãfi kõre, na alharĩni raƙĩƙi da alharini mai kauri sunã kishingiɗe a cikinsu, a kan, karagu. Mãdalla da sakamakonsu. Kuma Aljanna ta kyautatu da zama wurin hutãwa.
32Kuma ka buga musu misãli(2) da waɗansu maza biyu. Mun sanya wa ɗayansu gõnaki biyu na inabõbi, kuma Muka kħwayesu da itãcen dabĩnai, kuma Muka sanya shũka a tsakãninsu (sũ gõnakin).
33Kõwace gõna daga biyun, tã bãyar da amfãninta, kuma ba ta yi zãluncin kõme ba daga gare shi. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakãninsu.
34Kuma ɗan ĩtãce ya kasance gare shi. Sai ya ce wa abõkinsa, alhali kuwa yanã muhãwara da shi, "Nĩ ne mafĩfĩci daga gare ka a wajen dũkiya, kuma mafi izza a wajen jama´a."
35Kuma ya shiga gõnarsa, alhãli yanã mai zãlunci ga kansa, ya ce: "Bã ni zaton wannan zã ta halaka har abada."
36"Kuma bã ni zaton sa´a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiĩna, to, lalle ne, zan sãmi abin da yake mafi alhħri daga gare ta ya zama makõma."
37Abõkinsa ya ce masa, alhãli kuwa yanã muhãwara da shi, "Ashe kã kãfirta da wanda Ya halitta ka daga turɓaya, sa´an nan daga ɗigon maniyi, sa´an nan Ya daidaita ka, ka zama mutum?"
38"Amma ni, shĩ ne Allah Ubangijina, kuma bã zan tãra kõwa da Ubangijina ba"
39"Kuma don me, a lõkacin da ka shiga gõnarka, ka ce, ´Abin da Allah ya so (shi ke tabbata) bãbu wani ƙarfi fãce game da Allah.´ Idan ka gan ni, ni ne mafi ƙaranci daga gare ka a wajen dũkiya da ɗiya."
40"To, akwai fãtan Ubangijĩna Ya ba ni abin da yake mafi alhħri daga gõnarka, kuma ya aika azãba a kanta (ita gõnarka) daga sama, sai ta wãyi gari turɓãya mai santsi."
41"Kõ kuma ruwanta ya wãyi gari faƙaƙƙe, sabõda haka, bã zã ka iya nħmo shi ba dõminta."
42Kuma aka halaka dukan ´ya´yan itãcensa, sai ya wãyi gari yanã jũyar da tãfunansa biyu, sabõda abin da ya kashe a cikinta, alhãli kuwa ita tanã kwance a kan rassanta, kuma yanã cħwa, "Kaitõna, dã dai ban tãra(1) wani da Ubangijina ba!"
43Kuma wata jama´a ba ta kasance a gare shi ba, waɗanda ke taimakon sa, baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba.
44A can taimako da jiɓinta ga Allah yake. Shĩ ne kawai Gaskiya, shĩ ne Mafĩfĩci ga lãda kuma Mafĩfĩci ga ãƙiba.
45Ka buga musu misãlin rãyuwar dũniya, kamar ruwa ne wanda Muka saukar da shi daga sama sa´an nan tsirin ƙasa ya garwaya da shi, sa´an nan ya wãyi gari dudduga, iska tanã shiƙar sa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan ĩkon yi ne a kan dukan kõme.
46Dũkiya da ɗiya,(1) sũ ne ƙawar rãyuwar dũniya, kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai sun fi zama alhħri a wurin Ubangijinka ga lãda kuma sun fi alhħri ga bũri.
47Kuma a rãnar da Muke tafiyar da duwãtsu, kuma ka ga ƙasa bayyane, kuma Mu tãra su har ba Mu bar kõwa ba daga gare su.
48Kuma a gittã(2) su ga Ubangijinka sunã sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙĩƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lõkaci. ôa, kun riya cħwa bã zã Mu sanya muku wani lõkacin haɗuwa ba."
49Kuma aka aza littãfin ayyuka, sai ka ga mãsu laifi sunã mãsu jin tsõro daga abin da ke cikinsa, kuma sunã cħwa "Kaitonmu! Mħne ne ga wannan littãfi, bã ya barin ƙarama, kuma bã ya barin babba, fãce yã ƙididdige ta?" Kuma suka sãmi abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka bã Ya zãluntar kõwa.
50Kuma a lõkacin da Muka ce wa malãiku, "Ku yi sujada ga Ãdamu." Sai suka yi sujada fãce Iblĩsa, yã kasance daga aljannu sai ya yi fãsiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa. To fa, ashe, kunã riƙon sa, shi da zũriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhãli kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzãlumai.(3)
51Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rãyukansu ba kuma ban kasance mai riƙon mãsu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba.
52Kuma da rãnar da Allah Yake cħwa, "Ku kirãyi abõkan tarayyãTa, waɗanda kuka riya." Sai su kirãye su, sai bã zã su karɓa musu ba, kuma Mu sanya Maubiƙa(4) (Mahalaka) a tsakãninsu,
53Kuma mãsu laifi suka ga wutã suka tabbata lalle ne, sũ Mãsu auka mata ne, kuma ba su sãmi majũya ba daga gare ta.
54Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun jujjũya, a cikin wannan Alƙur´ãni, daga kõwane irin misãli ga mutãne (dõmin su gãne, su bi sharĩ´a), kuma mutum yã kasance mafi yawan abu ga jidãli.(1)
55Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni a lõkacin da shiriya ta zo musu, kuma su nħmi gãfara daga Ubangijinsu, fãce hanyar farko(2) ta je musu kõ kuma azãba ta jħ musu nau´i-nau´i.
56Kuma ba Mu aika Manzanni ba fãce sunã mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi, kuma waɗanda suka kãfirta sunã jidãli da ƙarya dõmin su ɓãta gaskiya da ita, kuma suka riƙi ãyõyiNa da abin da aka yi musu gargaɗi da shi abin izgili.
57Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda aka tunãtar game da ãyõyin Ubangijinsa, sai ya bijire daga barinsu, kuma ya manta abin da hannãyensa suka gabãtar? Lalle ne Mũ, Mun sanya abũbuwan rufi a kan zukãtansu dõmin kada su fahimcħ shi, kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi, kuma idan kã kĩrayħ su zuwa ga shiriya, to, bã zã su shiryu ba, a sa´an nan, har abada.
58Kuma Ubangijinka Mai gãfara ne, Ma´abũcin rahama. Dã Yanã kãma su sabõda abin da suka sanã´anta, lalle ne, dã Ya gaggauta azãba a gare su. ôa, sunã da lõkacin alkawari, (wanda) bã zã su sãmi wata makõma ba, baicinSa.(3)
59Kuma waɗancan alƙaryu(4) Mun halaka su, a lõkacin da suka yi zãlunci, kuma Muka sanya lõkacin alkawarin, ga halaka(5) su.
60Kuma a lõkacin da Mũsã(6) ya ce wa yãronsa, "Bã zan gushe ba sai na isa mahaɗar tħku biyu, kõ in shũɗe da tafiya shekara da shħkaru."
61To, a lõkacin da suka isa mahaɗar tsakãninsu sai suka manta kĩfinsu, sai ya kãma tafarkinsa a cikin tħku kamar bĩga.
62To, a lõkacin da suka wuce ya ce wa yãronsa, "Ka kãwo mana kãlãcinmu. Lalle ne haƙĩƙa mun haɗu da wahala daga tafiyarmu wannan."
63(Yãron) ya ce: "Kã gani! A lõkacin da muka tattara zuwa ga falalen nan to, lalle nĩ, na manta kĩfin, kuma bãbu abin da ya mantar da nĩ shi, fãce Shaiɗan, dõmin kada in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a cikin tħku, da mãmãki!"
64Ya ce: "Wancan ne abin da muka kasance munã biɗã." Sai suka kõma a kan gurãbunsu, sunã bĩbiya.
65Sai suka sãmi wani bãwa daga bãyinMu, Mun bã shi wata rahama(1) daga wurinMu, kuma Mun sanar da shi wani ilmi daga gunMu.
66Mũsã ya ce masa, "Ko in bĩ ka a kan ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya?"
67Ya ce: "Lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ, ba."
68"Kuma yãya zã ka yi haƙuri a kan abin da ba ka kħwayeda shi ba ga jarrabãwa?"
69Ya ce: "Za ka sãme ni, in Allah Yã so mai haƙuri kuma bã zan sãɓa maka ba ga wani umurni."
70Ya ce: "To idan ka bĩ ni to kada ka tambaye ni daga kõme sai na lãbarta maka ambato(2) daga gare shi."
71Sai suka tafi har a lõkacin da suka hau a cikin jirgi, ya hũje shi, ya ce, "Kã hũje shi dõmin ya nutsar da mutãnensa? Lalle ne, haƙĩƙa, kã zo da wani babban abu!"
72Ya ce: "Ashe ban ce, lalle kai, bã za ka iya yin haƙuri tãre da ni ba?"
73Ya ce: "Kada ka kãma ni da abin da na manta kuma kada ka kallafa mini tsanani ga al´amarĩna."
74Sai suka tafi, har suka haɗu da wani yãro, sai ya kashe shi. Ya ce: "Ashe kã kashe rai tsarkakakke, bã da wani rai ba? Lalle ne haƙĩƙa ka zo da wani abu na ƙyãma."
75Ya ce: "Shin, ban ce maka ba, lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ ba?"
76Ya ce: "Idan na tambaye(1) ka daga wani abu a bãyanta, to, kada ka abũce ni. Lalle ne, kã isa ga iyakar uzuri daga gare ni."
77Sai suka tafi, har a lõkacin da suka je wa mutãnen wata alƙarya, suka nħmi mutãnenta da su bã su abinci, sai suka ƙi su yi musu liyãfa. Sai suka sãmi wani bango a cikinta yanã nufin ya karye, sai (Halliru) ya tãyar da shi mĩƙe. (Mũsã) ya ce: "Dã kã so, lalle ne dã kã karɓi ijãra a kansa."
78Ya ce: "Wannan shi ne rabuwar tsakanina da tsakaninka. Zã ni gaya maka fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa."
79"Amma Jirgin, to, ya zama na waɗansu matalauta ne sunã aiki(2) a cikin tħku, sai na yi niyyar in aibanta shi, alhãli kuwa wani sarki ya kasance a gaba gare su, yanã karɓħwar kõwane jirgi (lãfiyayye) da ƙwãce.
80"Kuma amma yaron, to, uwãyensa sun kasance mũminai, to, sai muka ji tsõron ya kallafa musu kangara da kãfirci."
81"Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu mafi alhħri daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma mafi kusantar tausayi."
82"Kuma amma bangon, to, yã kasance na waɗansu yãra biyu ne, marãyu a cikin birnin, kuma akwai wata taska tãsu a ƙarƙashinsa, kuma ubansu ya kasance salĩhin mutum(3) ne, dõmin haka Ubangijinka Ya yi nufin su isa iyãkar ƙarfinsu, kuma sũ, su fitar da taskarsu, sabõda rahama ne daga Ubangijinka. Kuma ban yi shi ba daga umurnĩna. Wancan shĩ ne fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa."
83Kuma suna tambayar ka daga Zulƙarnaini,(4) ka ce: "Zan karanta muku ambato daga gare shi."
84Lalle ne Mũ Mun bã shi mulki a cikin ƙasa kuma Muka bã shi daga kõwane abu, hanya (zuwa ga murãdinsa).
85Sai ya bi hanya.
86Har a lõkacin da ya isa ga mafãɗar rãnã, kuma ya sãme ta tanã ɓacħwa a cikin wani ruwa mai baƙar lãkã, kuma ya sãmi waɗansu mutãne a wurinta. Muka ce: "Yã Zulƙarnaini imma dai ka azabtar kuma imma ka riƙi kyautatãwa a cikinsu."
87Ya ce: "Amma wanda ya yi zãlunci, to zã mu azabta shi, sa´an nan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa, sai kuma Ya yi masa azãba, azãba abar ƙyãma."
88"Kuma amma wanda ya yi ĩmãni kuma ya aikata aikin ƙwarai to, zã mu yi sakamako a gare shi (watau kyauta) mai kyau,(1) kuma zã mu gaya masa sauƙi daga umurninmu."
89Sa´an nan kuma ya bi hanya.
90Har a lõkacin da ya isa ga mafitar rãnã, ya sãme ta tanã fita a kan waɗansu mutãne (waɗanda) ba Mu sanya musu wata kãriya ba daga barinta.
91Kamar wancan alhãli kuwa haƙĩƙa, Mun kħwaye da jarrabãwa ga abin da ke gunsa.
92Sa´an nan kuma ya bi hanya.
93Har a lõkacin da ya isa a tsakãnin duwãtsu biyu, ya sãmi waɗansu mutãne daga gabãninsu. Ba su yi kusa su fahimci magana ba.
94Suka ce: "Yã Zulƙarnaini! Lalle ne Yãjũja da Majũja mãsu ɓarna ne a cikin ƙasa. To, ko zã mu sanya harãji sabõda kai, a kan ka sanya wani danni a tsakãninmu da tsakãninsu?"
95Ya ce: "Abin da Ubangijĩna Ya mallaka mini, a cikinsa yã fi zama alhħri. Sai ku taimakeni da ƙarfi, in sanya babbar katanga a tsakãninku da tsakãninsu."
96"Ku kãwo mini guntãyen baƙin ƙarfe". (Suka kai masa) har a lõkacin da ya daidaita a tsakãnin duwãtsun biyu (ya sanya wutã a cikin ƙarfen) ya ce: "Ku hũra (da zugãzugai)." Har a lõkacin da ya mayar da shi wutã, ya ce: "Ku kãwo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa."
97Dõmin haka bã za su iya hawansa ba, kuma bã zã su iya hujħwa gare shi ba.
98Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijĩna. Sai idan wa´adin(1) Ubangijĩna ya zo, ya mayar da shi niƙaƙƙe. Kuma wa´adin Ubangijĩna ya kasance tabbatacce."
99Kuma Muka bar sãshensu a rãnar nan, yanã garwaya a cikin sãshe, kuma aka bũsa a cikin ƙaho sai muka tãra su, tãrãwa.(2)
100Kuma Muka gitta Jahannama, a rãnar nan ga kãfirai gittãwa.
101Waɗanda idãnunsu suka kasance a cikin rufi daga tunã(3) Ni, kuma sun kasance bã su iya saurãrãwa.
102Shin fa, waɗanda suka kãfirta sun yi zaton (daidai ne) su riƙi waɗansu bãyĩNa,(4) majiɓinta baiciNa? Lalle ne, Mun yi tattalin Jahannama ta zama liyãfa ga kãfirai.
103Ka ce: "Kõ mu gaya muku game da mafĩfita hasãra ga ayyuka?"
104"Waɗanda aikinsu ya ɓace a cikin rãyuwar dũniya, alhãli kuwa sunã zaton lalle ne sũ, sunã kyautata, (abin da suke gani) aikin ƙwarai?"
105Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓãci. Sabõda haka bã zã Mu tsayar musu da awo(5) ba a Rãnar Ƙiyãma.
106Wancan ne sakamakonsu shĩ ne Jahannama, sabõda kãfircinsu, kuma suka riƙi ãyõyiNa da ManzanniNa abin izgili.
107Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Aljannar Firdausi ta kasance ita ce liyãfa a gare su.
108Suna madawwama a cikinta, bã su nħman makarkata daga barinta.
109Ka ce: "Dã tħku(6) ta kasance tawada ga (rubũtun) kalmõmin Ubangijina, lalle ne dã tħkun ta ƙãre a gabãnin kalmõmin Ubangijĩna su ƙãre, kuma kõda mun jħ da misãlinsa dõmin ƙari."
110Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa."(7)
Chapter 19 (Sura 19)
1K̃. H. Y. I . Ṣ̃.
2Ambaton rahamar Ubangijinka ne ga BawanSa Zakariyya.
3A lõkacin da ya kirãyi Ubangijinsa, kira ɓõyayye.
4Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, ƙashi na daga gare ni ya yi rauni, kuma kaina ya kunnu da furfura, kuma ban kasance marashin arziki ba game da kiranKa, yã Ubangiji!"
5"Kuma lalle nĩ, na ji tsõron(1) dangi a bãyãna, kuma mãtãta ta kasance bakarãriya! Sai ka bã ni wani mataimaki daga wajenKa."
6"Ya gãjħ ni, kuma ya yi gãdo daga gidan Yãƙũba. Kuma Ka sanya shi yardajje, yã Ubangiji!"
7(Allah Ya karɓa) "Yã zakariyya! Lalle ne Mũ, Munã yi maka bushãra da wani yãro, sunansa Yahaya. Ba Mu sanya masa wani takwara ba a gabãni."
8Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Yãya wani yãro zai kasance a gare ni, alhãli kuwa mãtãta ta kasance bakarãriya, kuma gã shi nã kai ga matuƙa ta tsũfa?"
9Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinka Ya ce. Shĩ, a gare Ni mai sauƙi ne, kuma haƙĩƙa Na halitta ka a gabãnin haka, alhãli ba ka kasance kõme ba."
10Ya ce: "Yã Ubangijina! Ka sanya mini alãma." Ya ce: "Alamarka ita ce ka kãsa yi wa mutãne magana a darũruwa uku daidai."
11Sai ya fita a kan mutãnensa daga masallãci, sa´an nan ya yi ishãra zuwa gare su da cħwa, "Ku yi tasbĩhi sãfe da yamma."
12Yã Yahaya! Ka kãma littãfi da ƙarfi. Kuma Muka bã shi hukunci yanã yãro.(1)
13Kuma (Muka sanya shi) abin girmamãwa daga gunMu, kuma mai albarka, kuma ya kasance mai ɗã´ã da taƙawa.
14Kuma mai biyayya ga mahaifansa biyu, kuma bai kasance mai girman kai mai sãɓo ba.
15Kuma aminci ya tabbata a gare shi a rãnar da aka haife shi da rãnar da yake mutuwa da rãnar da ake tãyar da shi yanã mai rai.
16Kuma ka ambaci Maryamu(2) a cikin Littãfi, a lõkacin da ta tsallake daga mutãnenta a wani wuri, a għfen gabas.
17Sa´an nan ta riƙi wani shãmaki daga barinsu. Sai Muka aika rũhinMu zuwa gare ta. Sai ya bayyana a gare ta da siffar mutum madaidaci.
18Ta ce: "Lalle nĩ inã nħman tsari ga Mai, rahama daga gare ka, idan ka kasance mai tsaron addini!"
19Ya ce: "Abin sani kawai, ni Manzon Ubangijinki ne dõmin in bãyar da wani yãro tsarkakke gare ki."
20Ta ce: "A inã yãro zai kasance a gare ni alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba, kuma ban kasance kãruwa ba?"
21Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinki Ya ce. Shĩ, a gare Ni mai sauƙi(3) ne. Kuma dõmin Mu sanya shi wata alãma ga mutãne, kuma wata rahama ce daga gare Mu.´ Kuma abin yã kasance wani al´amari hukuntacce."
22Sai ta yi cikinsa, sai ta tsallake da shi ga wani wuri mai nĩsa.
23Sai nãƙuda ta kai ta zuwa ga wani kututturen dabĩniya, ta ce "Kaitona, dã dai na mutu a gabãnin wannan kuma na kasance wani abu wulakantacce wanda aka manta!"
24Sai (yãron da ta haifa) ya(4) kira ta daga ƙarƙashinta, "Kada ki yi baƙin ciki! Haƙĩƙa Ubangijinki Ya sanya wani marmaro a ƙarƙashinki.
25"Kuma ki girgiza zuwa gare ki game da kututturen dabĩnon ya zuba a kanki yanã ´ya´yan dabĩno, ruɗabi nunannu."
26"Sai ki ci kuma ki sha kuma ki ji sanyi ga idãnunki.(1) To, idan kin ga wani aya daga mutãne, sai ki ce, ´Lalle nĩ, na yi alwãshin azumi dõmin Mai rahama sabõda haka bã zan yi wa wani mutum magana ba."
27Sai ta je wa mutãnenta tanã auke da shi. Suka ce: "Yã Maryamu! Lalle ne, haƙĩƙa kin zo da wani abu mai girma!
28"Yã ´yar´uwar Hãrũna! Ubanki bai kasance mutumin alfãsha ba, kuma uwarki ba ta kasance kãruwa ba."
29Sai ta yi ishãra zuwa gare shi, suka ce: "Yãya zã mu yi magana da wanda ya kasance a cikin shimfiar tsumma yanã jãrĩri?"
30Ya ce: "Lalle ne, nĩ bãwan Allah ne Allah Yã bã ni Littãfi kuma Ya sanya ni Annabi."(2)
31"Kuma Yã sanya ni mai albarka a inda duk na kasance kuma Ya umurce ni da yin salla da zakka matuƙar inã da rai."
32"Kuma mai biyayya ga uwãta, kuma bai sanya ni mai kaushin zũciya ba marashin alhħri."
33"Kuma aminci ya tabbata a gare ni a rãnar da aka haife ni da rãnar da nake mutũwa da rãnar da ake tãyar da ni inã mai rai."
34Wancan ne Ĩsã ɗan Maryamu, maganar gaskiya wadda suke shakka a cikinta.
35Bã ya kasancħwa ga Allah Ya riƙi wani ɗã.(3) Tsarki ya tabbata a gare shi! Idan Yã hukunta wani al´amari sai kawai Ya ce masa, "Kasance." Sai ya dinga kasan cħwa.
36"Kuma lalle Allah ne Ubangijina(4) kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan shi ne tafarki madaidaici."
37Sai ƙungiyõyin(5) suka sãɓã wa jũna a tsakãninsu. To, bõne ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta daga halartar yini mai girma.
38Mħne ne ya yi jinsu,(6) kuma mħne ne ya yi ganinsu a rãnar da suke zo Mana! Amma azzãlumai sunã a cikin ɓata bayyananna.
39Kuma ka yi musu gargaɗi da rãnar nadãma a lõkacin da aka hukunta al´amari alhãli kuwa sunã a cikin ɓãta, kuma sũ bã su yin ĩmãni.
40Lalle ne Mũ, Mũ ne ke gãdon ƙasa da wanda yake a kanta, kuma zuwa gare Mu ake mayar da su.
41Kuma ambaci Ibrãhĩm(2) a cikin Littafi. Lalle shi ya kasance mai yawan gaskatãwa, Annabi.
42A lõkacin da ya ce wa ubansa, "Yã bãba! Don me kake bauta wa abin da bã ya ji, kuma bã ya ga ni, kuma ba ya wadãtar da kõme daga barinka?"
43"Yã bãba! Lalle ni, haƙĩƙa abin da bai je maka ba na ilmi ya zo mini, sabõda haka ka bĩ ni in shiryar da kai wani tafarki madaidaici."
44"Yã bãba! Kada ka bauta wa Shaiɗan. Lalle Shaiɗan ya kasance mai saɓãwa ga Mai rahama."
45"Yã bãba! Lalle ne ni inã tsõron wata azãba daga Mai rahama ta shãfe ka, har ka zama masõyi ga Shaiɗan."
46Ya ce: "Ashe, mai gudu ne kai daga gumãkãna? Yã Ibrãĩm! Lalle ne, idan ba ka hanu ba, haƙĩ ƙa, zan jħfe ka. Kuma ka ƙaurace mini tun kanã mai mutunci."
47Ya ce: "Aminci(3) ya tabbata a gare ka! zan nħmi Ubangijina Ya gãfarta maka. Lalle Shi Ya kasance Mai girmamãwa gare ni."
48"Kuma inã nĩsantar ku da abin da kuke kira, baicin Allah kuma inã kiran Ubangijina, tsammãnin kada in zama marashin arziki game da kiran Ubangijina."
49To, sa´ad da ya nĩsance su da abin da suke bautãwa baicin Allah, Muka bã shi Is´hãƙa da Ya´aƙuba alhãli kuwa kõwanensu Mun mayar da shi Annabi.
50Kuma Muka yi musu kyauta daga RahamarMu, kuma Muka sanya musu harshen gaskiya(4) maɗaukaki.
51Kuma ka ambaci Mũsã a cikin Littãfi. Lalle ne shi, yã kasance zãɓaɓɓe, kuma yã kasance Manzo, Annabi.
52Kuma Muka kira shi daga għfen dũtse na dãma kuma Muka kusanta shi yanã abõkin gãnãwa.
53Kuma Muka yi masa kyauta daga RahamarMu da ɗan´uwansa Hãrũna, ya zama Annabi.
54Kuma ka ambaci Ismã´ila a cikin Littãfi. Lalle shi, yã kasance mai gaskiyar alkawari, kuma yã kasance Manzo, Annabi.
55Kuma yã kasance yanã umurnin mutãnens(1) da salla da zakka. Kuma yã kasance yardajje a wurin Ubangijinsa.
56Kuma ka ambaci Idrĩsa a cikin Littãfi. Lalle shi, ya kasance mai yawan gaskatãwa, Annabi.
57Muka ɗaukaka shi a wuri maɗaukaki.
58Waɗancan sũ ne waɗanda Allah Ya yi wa ni´ima daga Annabãwa daga zurriyar Ãdamu, kuma daga waɗanda muka ɗauka tãre da Nũhu, kuma daga zurriyar Ibrãhĩm da Isrã´ila, kuma daga waɗanda Muka shiryar kuma Muka zãɓe su. Idan anã karãtun ãyõyin Mai rahama a kansu, sai su fãɗi sunã mãsu sujada kuma mãsu kũka.
59Sai waɗansu ´yan bãya(2) suka maye a bãyansu suka tõzarta salla, kuma suka bi sha´awõwinsu. To, da sannu zã su hau da wani sharri.
60Fãce wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aiki na ƙwarai. To, waɗannan sunã shiga Aljanna, kuma bã a zãluntar su da kõme.
61Gidãjen Aljannar zama wadda Mai rahama ya yi alkawarin bãyarwa ga bãyinSa (mãsu aikin ĩmãni) a fake. Lalle ne shĩ, alkawarin ya kasance abin riskuwa.
62Bã su jin yasassar magana a cikinta, fãce sallama. Kuma sunã da abinci, a cikinta, sãfe da maraice.
63Wancan Aljannar ce wadda Muke gãdar da wanda ya kasance mai aiki da taƙawa daga bãyiNa.
64(Sunã mãsu cħwa) "Kuma bã mu sauka(3) Fãce da umuruin Ubangijinka (Muhammad). Shĩ ne da mulkin abin da ke a gaba gare mu da abin da ke a bãyanmu da abin da ke a tsakãnin wannan." Kuma(4) (Ubangijinka bai kasance wanda ake mantãwa ba.
65Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautarsa. Shin kã san wani takwara a gare shi?
66Kuma mutum yana cħwa, "Shin idan na mutu lalle ne haƙĩ ƙa da sannu zã a fitar da ni inã mai rai?"
67Shin, kuma mutum bã zai tuna ba cħwa lalle ne Mun halitta shi a gabãni, alhãli kuwa bai kasance kõme ba?
68To, Munã rantsuwa da Ubangijinka, lalle ne, Muna tãyar da su da kuma shaianun sa´an nan, kuma lalle Muna halatar da su da kuma Shaiɗanun sa´an nan, kuma, lalle Muna halatar da su a għfen Jahannama sunã gurfãne.
69Sa´an nan kuma lalle Munã fizge wanda yake mafi tsananin girman kai ga Mai rahama daga kõwace ƙungiya.
70Sa´an nan kuma lalle Mũ ne Mafi sani ga waɗanda suke sũ ne mafiya cancantar ƙõnuwa da ita.
71Kuma bãbu kõwa daga gare ku sai mai tuzga mata.(1) Yã kasance wajibi ga Ubangijinka, hukuntacce.
72Sa´an nan kuma Mu tsħrar da waɗanda suka yi aiki da taƙawa, kuma Mu bar azzãlumai a cikinta gurfãne.
73Kuma idan anã karatun ãyõyinMu, bayyanannu a kansu, sai waɗanda suka kãfirta su ce wa waɗanda suka yi ĩmãni, "Wanne daga ƙungiyõyin biyu ya fi zama mafi alhħri ga matsayi, kuma mafi kyaun majalisa?"
74Kuma da yawa daga mutãnen ƙarni Muka halakar a gabãninsu sũ (waɗandaMuka halakar) in ne mafi kyaun kãyan ãki da magãnã.(2)
75Ka ce: "Wanda ya kasance a cikin ɓata sai Mai rahama Ya yalwata masa yalwatãwa, har idan sun ga abin da ake yi musu wa´adi, imma azãba kõ sã´a, to zã su sani, wane ne yake shĩ ne, mafi sharri ga wuri, kuma mafi rauni ga runduna!"
76Kuma Allah na ƙãra wa wa ɗanda suka nħmi shiryuwa da shiriya. Kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai ne mafi alhħri awurin Ubangijinka ga lãda, kuma mafi alhħri ga makõma.
77Shin, ka ga wanda ya kãfirta da ayõyinMu, kuma ya ce: "Lalle ne zã a bã ni dũkiya da ɗiya?"
78Shin, yã tsinkãyi gaibi ne, kõ kuwa yã ɗauki wani alkawari daga Mai rahama ne?
79ôaha! zã mu rubũta abin da yake faɗa, kuma Mu yalwata masa, daga azãba, yalwatãwa.
80Kuma Mu gãde shi ga abin da yake faɗa, kuma ya zo Mana yanã shi kɗai.
81Kuma suka riƙi gumãka,(1) baicin Allah, dõmin su kãsance mataimaka a gare su.
82ôaha! Zã su kãfirta da ibãdarsu, kuma su kasance maƙiya a kansu.
83Shin, ba ka gani ba cħwa Mun saki shaiɗanu(2) a kan kãfirai sunã shũshũta su ga zunubi shũshũtãwa?
84Sabõda haka kada ka yi gaggawa a kansu, Munã yi musu ƙidãyar ajali ne kawai, ƙidãyãwa.
85A rãnar da Muka tãra mãsu taƙawa zuwa ga Mai rahama sunã bãƙin girma.
86Kuma Munã kõra mãsu laifi zuwa Jahannama, gargaãwa.
87Ba su mal1akar cħto fãce wanda ya riƙi alkawari a wurin Mai rahama.
88Kuma suka ce: "Mai rahama Yã riƙi ã!"
89Lalle ne haƙĩƙa kun zo da wani abu mai girman mũni.
90Sammai sunã kusa su tsattsage sabõda shi, kuma ƙasa ke kħce kuma duwãtsu su faɗi sunã karyayyu.
91Dõmin sun yi da´awar ɗã ga Mai rahama.
92Alhãli bã ya kamata ga Mai rahama ya riƙi wani ɗã.
93Dukkan wanda yake a cikin sammai da ƙasa bai zama ba fãce mai jħ wa Mai rahama ne yanã bãwã.
94Lalle ne haƙĩƙa Yã lissafe su, kuma ya ƙidãye su, ƙidãya.
95Kuma dukan kõwanensu mai jħ Masa ne a Rãnar Ƙiyãma yanã shi kaɗai.
96Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Mai rahama zai sanya musu so.(1)
97Sa´an nan Ibin sani kawai Mun sauƙaƙar da shi (Alƙur´ãni) a harshenka, dõmin ka yi bushãra da shi ga mãsu aiki da taƙawa kuma ka yi gargaɗi da shi ga mutãne mãsu tsananin husũma.
98Kuma da yawa Muka halakar da mutãnen ƙarnõni a gabãninsu. Shin kanã jin mõtsin wani guda daga gare su, kõ kuwa kanã jin wata ɗuriya tãsu?
Chapter 20 (Sura 20)
1Ɗ. H.
2Ba Mu saukar da Alƙur´ãni a gare ka dõmin ka wahala ba.
3Fãce dõmin tunãtarwa ga wanda ke tsõron Allah.
4(An saukar da shi) saukarwa daga wanda Ya halitta ƙasa da sammai maɗaukaka.
5Mai rahama, Ya daidaita(2) a kan Al´arshi.
6Abin da yake a cikin sammai nãSa ne, da abin da yake a cikin ƙasa da abin da yake a tsakãninsu da abin da ke ƙarƙashin turɓãya.
7Kuma idan ka bayyana da magana, to, lalle Shi, Yanã sanin asĩri da mafi bõyuwa.
8Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau.
9Kuma shin, lãbarin Mũsã yãje maka?
10A lõkacin da ya ga wata wuta, sai ya ce wa iyãlinsa, "Ku dãkata. Lalle ne nĩ, na tsinkãyi wata wuta tsammãnĩna in zo mukuda makãmashi daga gare ta, kõ kuwa in sãmi wata shiriya a kan wutar."
11Sa´an nan a lõkacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Mũsã!"
12"Lalle ne, Nĩ ne Ubangijnka, sai ka ɗħbe takalmanka(3) Lalle ne kanã a rãfin nan abin tsarkakħwa, Ɗuwa."
13"Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi."
14"Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni."
15"Lalle ne Sa´a mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukan rai da abin da yake aikatãwa."
16"Sabõda haka, kada wanda bã ya yin ĩmãni da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka."
17"Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!"
18Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshħna kuma inã da waɗansu bukãtõci(1) na dabam a gare ta."
19Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!"
20Sai ya jħfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa.
21Ya ce: "Ka kãma ta kuma kada ka ji tsõro. Za Mu mayar da ita ga hãlinta na farko."
22"Kuma ka haɗa hannunka zuwa ga damtsenka, ya fita yanã fari, bãbu sõfane, wata ãyã ta dabam."
23"Dõmin Mu nũna maka daga ãyõyinMu manya."
24"Ka tafi zuwa ga Fĩr´auna. Lalle shĩ ya ƙħtare haddi (da girman kai)."
25Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka buɗa(2) mini, ƙirjĩna.
26"Kuma ka sauƙaƙe mini al´amarĩna."
27"Kuma Ka warware mini wani ƙulli daga harshħna."
28"Su fahimci maganãta."
29"Kuma Ka sanya mini wani mataimaki daga mutãnena."
30"Hãrũna ɗan´uwana."
31"Ka ƙarfafa halittata da shi."
32"Kuma Ka shigar da shi a cikin al´amarina."
33"Dõmin mu tsarkake Ka da yawa."
34"Kuma mu tuna Ka da yawa."
35"Lalle Kai, Ka kasance Mai gani gare mu."
36Ya ce: "Lalle ne, an bã ka rõƙonka, yã Mũsã!"
37"Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun yi wata baiwa gare ka a wani lõkacin na dabam."
38"A lõkacin da Muka yi wahayin abin da aka yi wahayi zuwa ga uwarka."
39"cħwa, Ki jħfa shi a cikin akwatin nan, sa´an nan ki jħfa shi a cikin kõgi, sa´an nan kogin ya jefa shi a gãɓa, wani maƙiyi Nãwa kuma maƙiyi nãsa ya ɗauke shi.´ Kuma Na jħfa wani so daga gare Ni a kanka. Kuma dõmin a riƙe ka da kyau a kan ganiNa."
40"A sa´ad da ´yar´uwrka ke tafiya har ta ce, shin, in shiryar da ku ga wanda ke rħnonsa?´ Sai Muka mayar da kai zuwa ga uwarka dõmin idonta ya yi sanyi(1) kuma bã zã ta yi baƙin ciki ba. Kuma kã kashe wani rai, sa´an nan Muka tsħrar da kai daga baƙin ciki, kuma Muka fitine ka da waɗansu fitinõni. Sa´an nan ka zauna shħkaru a cikin mutãnen Madyana. Sa´an nan kuma ka zo a kan wata ƙaddara, yã Mũsã!
41"Kuma Na zãɓe ka dõmin Kaina."
42"Ka tafi kai da ɗan´uwanka game da ãyõyiNa, kuma kada ku yi rauni ga ambatõNa."
43"Ku tafi kũ biyu zuwa ga Fir´auna. Lalle shĩ ya ƙħtare haddi (ga girman kai)."
44"Sai ku gaya masa magana mai laushi,(2) tsammãninsa yanã tunãwa kõ kuwa ya ji tsõro."
45Su biyu suka ce: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne munã tsõron ya yi gaggawa a kanmu, kõ ya ƙħtare haddi."
46Ya ce: "Kada ku ji tsõro. Lalle Nĩ, Inã tãre da ku, Inaji, kuma Inã gani."
47"Sai ku jħ masa sa´an nan ku ce, Lalle mũ, Manzanni biyune na Ubangijinka, sai ka saki Banĩ Isrã´ĩla tãre da mu. Kuma kada ka yi musu azãba. Haƙĩƙa mun zomaka da wata ãyã daga, Ubangijinka. Kuma aminci ya tabbata ga wanda ya bi shiriya."
48"Lalle mũ, haƙĩƙa, an yi wahayi zuwa gare mu, cħwaazãba tanã a kan wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya."
49Ya ce: "To, wãne ne Ubangijinku? Ya Mũsã!"
50Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kõme halittarsa, sa´an nan Ya shiryar."
51Ya ce: "To, mħne hãlin ƙarnõnin farko?"
52Ya ce: "Saninsu yanã a wurin Ubangijĩna, Ubangijĩna bã Ya ɓacħwa kuma bã Ya mantuwa."
53"Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma Ya shigar muku da hanyõyi a cikinta, kuma Ya saukar da ruwa daga sama." Sa´an nan game da shi(1) Muka fitar da nau´i-nau´i daga tsirũruwa dabam-dabam.
54Ku ci kuma ku yi kiwon dabbõbin ni´imarku. Lalle ne, a cikin wannan akwai ãyõyi ga masu hankali.
55Daga gare ta(2) Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke mayar da ku, kuma daga gare ta Muke fitar da ku a wani lõkaci na dabam.
56Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun nũna masa ãyõyinMu dukansu sai ya ƙaryata, kuma ya ƙiya!
57Ya ce: "Shin kã zo mana ne dõmin ka fitar da mu daga ƙasarmu game da sihirinka, yã Mũsã?"
58"To, lalle ne munã zo maka da wani sihiri irinsa. Sai ka sanya wani wa´adi a tsakãninmu da tsakãninka bã mu sãɓa masa mũ kai kuma, bã ka sãɓãwa, a wani wuri mai dãcħwa."
59Ya ce: "Wa´adinku shi ne rãnar ƙawa kuma a tãra mutãne da hantsi."
60Sai Fir´auna ya jũya, sa´an nan ya tãra mugunyar dabãrarsa, sa´an nan kuma ya zo.
61Mũsã ya ce musu, "Kaitõnku! Kada ku ƙirƙira ƙarya ga Allah har Ya tumɓuke ku da wata azãba. Kuma wanda ya ƙirƙira ƙarya, yã tãɓe."
62Sai suka yi jãyayya ga al´amarinsu a tsakãninsu kuma suka asirta gãnawa.
63Suka ce: "Lalle ne waɗannan biyun, haƙĩƙa masihirta ne sunã nufin su fitar da ku daga ƙasarku(3) game da sihirinsu kuma su tafi da tabĩ´arku mafĩficiya."
64"Sai ku haɗa dabãrarku sa´an nan kuma ku tafi a sahu guda, kuma haƙĩƙa, wanda ya rinjãya, a yau, ya rabbanta."
65Suka ce: "Ya Mũsã! Imma ka jefa, ko kuma mu kasance farkon mai jħfawa."
66Ya ce: "ôa, ku jħfa." Sai gã igiyoyinsu da sandunansu anã sũranta su a gare shi, daga sihirinsu, lalle sunã tafiya da sauri.
67Sai Mũsã ya ji tsõro a cikin ransa.
68Muka ce: "Kada ka ji tsõro. lalle kai ne mafi ɗaukaka."
69"Kuma ka jħfa abin da ke a cikin hannun dãmanka, ta cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata mãkircin masihirci ne kuma masihirci bã ya cin nasara a duk inda ya je."
70Sai aka jħfar da masihirtan sunã mãsu sujada, suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin Hãrũna da Mũsã."
71Ya ce: "Kun yi ĩmãni sabõda shi a gabãnin in yi muku izni? Lalle shĩ, haƙĩƙa, babbanku ne wanda ya sanar da ku sihirin! To, lalle ne zan kakkãtse hannayenku da ƙafãfunku a tarnaƙi kuma lalle zan tsĩre ku a cikin kututturan itãcen dabĩno, kuma lalle zã ku sani wanenmu ne mafi tsananin azãba kuma wãne ne mafi wanzuwar (azãba)."
72Suka ce: "Bã zã mu fĩfĩta ka ba faufau a kan abin da ya zo mana na hujjõji. Munã rantsuwa da wanda Ya ƙãga halittarmu sai ka hukunta abin da kake mai hukuntãwa, ai kanã ƙãre wannan rãyuwar dũniya kawai ne."
73"Lalle mũ, mun yi ĩmãni da Ubangijinmu dõmin Ya gãfarta mana laifuffukanmu da abin da ka tĩlasta mu a kansa na sihiri. Kuma Allah ne Mafi alhħri, kumaMafi wanzuwa."
74Lalle(1) shĩ wanda ya je wa Ubangijinsa yanã mai laifi, to lalle ne yanã da Jahannama, bã ya mutuwa a cikinta kuma bã ya rãyuwa.
75Kuma wanda ya je Masa yanã mai ĩmãni, alhãli kuwaya aikata aikin ƙwarai to waɗannan sunã da darajõji maɗaukaka.
76Gidãjen Aljannar zama kõguna na gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu. Kuma wannan ne sakamakon wanda ya tsarkaku.
77Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun yi wahayi zuwa ga Mũsã cħwa, "Ka yi tafiyar dare da bãyiNa. Sa´an nan ka dõka musu hanya a cikin tħku tana ƙħƙasasshiya, bã ka tsõron riskuwa, kuma bã ka fargabar nutsħwa."
78Sai Fir´auna ya bi su game da rundunarsa. Sai abin da ya rufe su daga tħku ya rufe su.
79Kuma Fir´auna ya ɓatar da mutãnensa, kuma bai shiryar(dasu) ba.
80Yã Banĩ Isrã´ĩla! Lalle Mun tsħrar da ku daga maƙiyinku, kuma mun yi muku wa´adi a għfen Dũtsen nan na dãma, kuma Mun sassaukar da darɓa da tattabaru dõminku.
81Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurtã ku kuma kada ku ƙħtare haddi a cikinsa har hushĩNa ya sauka a kanku. Kuma wanda hushĩNa ya sauka a kansa, to, lalle ne, ya fãɗi.
82Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa´an nan kuma ya nħmi shiryuwa.
83"Kuma mħne ne ya gaggautar(1) da kai ga barin mutãnenka? Yã Mũsã!"
84Ya ce: "Su ne waɗannan a kan sãwũna, kuma na yi gaggãwa zuwa gare Ka, yã Ubangiji! Dõmin Ka yarda."
85Ya ce: "To, lalle ne, haƙĩƙa, Mun fitini, mutãnenka daga bayãnka, kuma sãmiri ya ɓatar da su."
86Sai Mũsã ya kõma zuwa ga mutãnensa yanã mai hushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Yã mutãnħna! shin, Ubangijinku bai yi muku wa´adi ba, wa´adi mai kyau? Shin, lõkacin ya yi tsãwo a kanku ne, kõ kun yi nufi ne wani hushi ya sauka a kanku daga Ubangijinku, sabõda haka kuka sãɓã wa alkawarĩna?"
87Suka ce: "Ba mu sãɓa wa alkawarinka(2) ba da ĩkonmu kuma amma an ɗõra mana waɗansu kãya masu nauyi daga abin ƙawar mutãnen ne, sai muka jħfar da su. Sa´an nan kamar haka ne sãmiri ya jħfa."
88"Sai ya fitar musu da wani maraƙi, jikin mutãne, yanã rũri, sa´an nan suka ce: wannan ne gunkinku kuma gunkin Mũsã, sai ya manta."
89Shin, to, bã su ganin cħwabã ya mayar musu da magana, kuma bã ya mallakar wata cũta a gare su, kuma bã ya mallakar amfãni?
90Kuma, haƙĩƙa, Hãrũna yã ce musu daga gabãni, "Yã mutãnħna! Lalle an fitinħ ku da shi ne kawai. Kuma lalle Ubangijinku Mai rahama ne, sai ku bi ni, kuma ku yi ɗã´ã ga umurnĩna."
91Suka ce: "Ba zã mu gushe ba faufau a kansa munã mãsu lazimta,(1) sai Mũsã ya kõmo zuwa gare mu."
92(Mũsã) ya ce: "Yã Hãrũna! Mħ ya hane ka, sa´ad da kagan su sun ɓace."
93"Ba ka bĩ ni ba! Shin, to, ka sãɓã wa umurnina ne?"
94(Hãrũna) ya ce: "Yã ɗãn´uwãna! Kada ka yi kãmu ga għmũna kõ ga kaina. Lalle nĩ, nã ji tsõron ka ce: Ka rarraba a tsakãnin Banĩ Isrã´ĩla kuma ba ka tsare maganata ba."
95(Mũsã) ya ce: "Mħne ne babban al´amarinka? Ya Sãmiri!"
96(Sãmiri) ya ce: "Nã ga abin da ba su gan shi ba shi, sai na yi damƙa, damƙa guda daga kufan sãwun Manzon, sa´an nan na jħfa ta. Kuma haka dai raina ya ƙawãta mini."
97(Mũsã) ya ce: "To, ka tafi, sabõda haka lalle ne kanã da a cikin rãyuwarka, ka ce ´Bãbu shãfa´ kuma kanã da wani ma´alkawarta, bã zã a sãɓa maka gare ta ba. Kuma ka dũba zuwa ga gunkinka wanda ka yini a kansa kanã mai lazimta. Lalle ne muna ƙõne shi,(2) sa´an nan kuma munã shħƙe shi, a cikin tħku, shħƙħwa."
98Abin sani kawai abin bautãwarku Allah kawai ne wanda bãbu wani abin bautãwa, fãce Shi kuma Yã yalwaci(3) dukkan kõme da ilmi.
99Kamar wancan ne Muke lãbartãwa(1) a gare ka, daga lãbãran abin da ya gabãta, alhãli kuwa haƙĩƙa, Mun bã ka zikiri (Alƙur´ãni) daga gunMu.
100Wanda ya kau da kai daga gare shi, to, lalle shĩ, yanãɗaukar wani nauyi a Rãnar Ƙiyãma.
101Sunã madawwama a cikinsa, kuma yã mũnana ya zama abin ɗauka, a Rãnar Ƙiyãma.
102A Rãnar da ake hũrãwa a cikin ƙãho kuma Munã tãra mãsu laifi, a rãnar nan, sunã mãsu shũɗãyen idãnu.
103Suna ɓõye magana a tsakãninsu, (Sunã ce wa jũna) "Ba ku zauna ba (a cikin dũniya) fãce kwãna gõma."
104Mu ne mafi sani ga abin da suke faɗa a sa´ad da mafĩficinsu ga hanya ke cħwa, "Ba ku zauna ba fãce a yini guda."
105Kuma sunã tambayar ka daga duwãtsu(2) sai ka ce: "Ubangijina Yana shħƙe su shħƙħwa,
106Sa´an nan Yanã barin (wurinsu) faƙo mai santsi.
107"Bã ka ganin karkata a cikinsa, kuma bã ka ganin wani tudu."
108A rãnar nan sunã biyar mai kira, bãbu karkata a gare shi, kuma sautuka suka yi kawaici ga Mai rahama, bã ka sauraren kõme fãce sautin tafiya.
109A yinin nan cħto bã ya yin amfãni fãce wanda Mai rahama Ya yi masa izni kuma Ya yarda da shi, da magan(3)
110Yanã sanin(4) abin da ke a gaba gare su da abin da ke bãyansu, kuma bã su kħwayħwa da shi ga sani.
111Kuma fuskõki suka ƙanƙan da kai ga Rãyayye,Tsayayye, alhãli kuwa wanda ya ɗauko wani zãlunci ya tãɓe.
112Kuma wanda ya aikata wani abu daga ayyukan ƙwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bã ya tsõron wani zãlunci ko wata naƙasa.
113Kuma haka Muka saukar da shi, Alƙur´ãni, yanã abin karantãwa, da Larabci kuma Muka jujjuya misãlai, a cikinsa, na tsõratarwa, tsammãninsu, sunã yin taƙawa ko ya sabbaba musu wata wa´aztuwa.
114Sa´an nan Allah Mamallaki, Tabbatacce Yã ɗaukaka. Kuma kada ka yi gaggãwa(1) da Alƙur´ãni a gabãnin a ƙãre wahayinsa zuwa gare ka. Kuma ka ce: "Yã Ubangiji! Ka ƙãra mini ilmi."
115Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun yi alkawari zuwa ga Ãdamu a gabãnin wannan, sai ya manta, kuma ba Mu sãmi ƙarfin zũciya a gare shiba.
116Kuma sa´ad da Muka ce wa malã´iku, "Ku yi sujada ga Ãdamu." Sai suka yi sujada, fãce Iblĩsa, yã ƙiya.
117Sai Muka ce: "Ya Ãdamu! Lalle ne wannan maƙiyi(2) ne gare ka da kuma ga mãtarka, sabõda haka kada ya fitar da ku daga Aljanna har ku wahala."
118Lalle ne kã sãmu bã zã ka ji yunwa ba a cikinta, kuma bã zã ka yi tsiraici ba.
119"Lalle kai, bã zã ka ji ƙishirwa ba, kuma bã zã ka shiga hantsi ba."
120Sai shaiɗan ya sanya waswãsi zuwa gare shi, ya ce: "Yã Ãdamu! Shin, in shiryar da kai ga itãciyar dawwama da mulki wanda bã ya ƙãrħwa?"
121Sai suka ci daga gare ta, sabõda haka al´aurunsu suka bayyana, kuma suka shiga sunã lulluɓãwa a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ãdamu ya sãɓã wa Ubangijinsa, sabõda haka ya ɓace.
122Sa´an nan kuma Ubangjinsa Ya zãɓħ shi, Ya karɓi tũba gare shi, kuma Ya shiryar (da shi).
123Ya ce: "Ku sauka kũ biyu daga gare ta gabã ɗaya, sãshenku yanã maƙiyi ga sãshe. To, imma dai wata shitiya ta jħ muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiryarwãta, to, bã ya ɓacħwa, kuma bã ya wahala."
124"Kuma wanda ya bijire(3) daga ambatõNa (Alƙur´ãni) to, lalle ne rãyuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi, kuma Munã tãyar da shi a Rãnar Ƙiyãma yanã makãho."
125Ya ce: "Ya Ubangiji! Don me Ka tãyar da ni makãho alhãli kuwa nã kasance mai gani?"
126Ya ce: "Kamar wancan ne ãyõyinMu suka jħ maka sai ka mance su, kuma kamar hakar a yau ake mance ka."
127Kuma kamar haka Muke sãka wa wanda ya yawaita,(1) kuma bai yi ĩmãni da ãyõyin Ubangijinsa ba. Kuma lalle ne azãbar Lãhira ce mafi tsanani, kuma mafi wanzuwa
128Shin, to, bai shiryar da su ba cħwa da yawa Muka halakarda (kãfirai) daga ƙarnuka, a gabãninsu, sunã tafiya a cikin masaukansu? Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu hankula.
129Kuma bã dõmin wata kalma ba wadda ta gabãta daga Ubangijinka, da kuma ajali ambatacce haƙĩƙa, dã azãbarta kasance mai lazimta.
130Sai ka yi haƙuri(2) a kan abin da suke cħwa, kuma ka yi tasbĩhi da gõdħ wa Ubangijinka a gabãnin fitõwar rãnã da gabãnin ɓacħwarta, kuma daga sã´õ´in dare sai ka yi tasbĩhi da sãsannin yini, tsammãninka zã ka sãmi yarda.
131Kuma kada ka mĩƙar da idãnunka zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi da shi, nau´i-nau´i daga gare su, kamar huren rãyuwar dũniya yake, dõmin Mu fitine su a cikinsa, alhãli kuwa arzikin Ubangijinka, ne mafi alhħri kuma mafi wanzuwa.
132Kuma ka umurci iyãlanka da salla, kuma ka yi haƙuri a kanta. Bã Mu tambayar ka wani arziki Mu ne Muke azurta ka. Kuma ãƙiba mai kyau tanã ga taƙawa.
133Kuma suka ce: "Don me bã ya zo mana da wata ãyã daga Ubangijinsa?" Shin, kuwa hujjar abin da ke a cikin littattafan farko, ba ta jħ musu ba?
134Kuma dã dai Mun halaka sũ da wata azãba daga gabãninsa, lalle ne dã sun ce: "Yã Ubangijinmu! Dã Kã aiko da wani Manzo zuwa gare mu har mu bibiyi ãyõyinKa daga gabãnin mu ƙasƙanta, kuma mu wulãkantu!"
135Ka ce: "Kõwa mai tsumãye ne. Sai ku yi tsumãye. Sa´an nan zã ku san su wa ne ma´abũta tafarki madaidaici, kuma wane ne ya nħmi shiryuwa."
Chapter 21 (Sura 21)
1Hisãbin mutãne ya kusanta gare su, ahãli kuwa sunã a cikin gafala, sunã mãsu bijirħwa.
2Wani ambatõ daga Ubangijinsu sãbo, bã ya zuwa gare su fãce sun saurãre shi, alhãli kuwa sunã mãsu yin wãsa.
3Sanã mãsu shagaltacin zukãtansu, kuma su asirta gãnãwa: Waɗanda suka yi zãlunce (sunã cħwa) "Wannan bã Kõwa ba ne fãce mutum misãlinku. Shin, to, kunã jħ wa sihiri, ahãli kuwa kũ, kunã fahimta?"
4Ya ce: "Ubangijina Yanã sanin magana a cikin sama da ƙasa kuma Shi ne Mai ji, Masani."
5ôa, suka ce: "Yãye-yãyen mafarki ne. ôa, yã ƙirƙira shi ne. ôa, shi mawãƙi ne. Sai ya zo mana da wata ãyã kamar yadda aka aiko manzanni na farko."
6Wata alƙarya da Muka halaka ta a gabãninsu, ba ta yi ĩmãni ba. Shin, to, sũ, sunã yin ĩmãni?
7Kuma ba Mu aika ba a gabãninka fãce mazãje, Munã yin wahayi zuwa gare su. Ku tambayi ma´abũta ambato(1) idan kun kasance ba ku sani ba.
8Kuma ba Mu sanya su jiki, bã su cin abin ci ba, kuma ba su kasance madawwama ba.
9Sa´an nan kuma Muka gaskata musu alkawari; sai Muka tsħrar da su da wanda Muke so, kuma Muka halakar da mãsu yawaitãwa.(2)
10Lalle haƙĩƙa Mun saukar da wani littãfi zuwa gare ku,(3) a cikinsa akwai ambatonku. Shin, to, bã ku hankalta?
11Kuma da yawa Muka karya wata alƙarya tã kasance mai zãlunci, kuma Muka ƙãga halittar waɗansu mutãne na dabam a bãyanta.
12Sai a lõkacin da suka hangi azãbarMu, sai gã su sunã gudu daga gare ta.
13"Kada ku yi gudu. Ku kõmo zuwa ga abin da aka ni´imtar da ku a cikinsa da gidãjenku tsammãninku anã tambayar ku."
14Suka ce: "Kaitonmu! Lalle mũ ne muka kasance mãsu zãlunci."
15Sa´an nan waccan ba ta gushe ba, ita ce da´awarsu har Muka mayar da su girbabbu, bitattu.
16Kuma ba Mu halitta sama da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu Muna Mãsu wãsã ba.
17Da Mun yi nufin Mu riƙi wani abin wãsa dã Mun(1) riƙe shi daga gunMu, idan Mun kasance mãsu aikatãwa.
18ôa, Munã jĩfa da gaskiya a kan ƙarya, sai ta darkãke ta, sai ga tã halakakka. Kuma bone yã tabbata a gare ku sabõda abin da kuke siffantãwa.
19Kuma shĩ ne da mallakar wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma waɗanda suke wurinSa (watau malã´iku), bã su yin girman kai ga ibãdarSa. kuma bã su gajiya.
20Sunã tasbĩhi dare da rãnã, bã su yin rauni.
21Kõ (kãfirai) sun riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa ne ga ƙasã, su ne mãsu tãyarwa (gare su)?
22Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al´arshi daga abin da suke siffantãwa.
23Bã a tambayar Sa ga abin da Yake aikatãwa, alhãli kuwa sũanã tambayar su.
24Kõ sun riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa baicinSa? Ka ce: "Ku kãwo hujjarku, wannan shi ne ambaton wanda yake tãre da ni, kuma shi ne ambaton wanda yake a gabãnĩna. ôa, mafi yawansubã su sanin gaskiya, sabõda haka sũ mãsu bijirħwa ne."
25Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cħwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini."
26Kuma suka ce: "Mai rahama ya riƙi ɗã." Tsarkinsa, ya tabbata! ôa, (malã´iku) bãyi ne mãsu daraja.
27Bã su gabãtarSa da magana, kuma su da umurninSa suke aiki.
28Yanã sanin abin da yake gaba gare su da abin da yake a bãyansu, kuma bã su yin cħto fãce ga wanda Ya yarda, kuma sũmasu sauna ne sabõda tsõronSa.
29Kuma wanda ya ce daga gare su, "Lalle nĩ abin bautãwa ne baicinSa," to, wannan Munã sãkã masa da, Jahannama. Kamar haka Muke sãkã wa azzãlumai.
30Shin kuma waɗanda suka kãfirta ba, su gani da cħwa lalle sammai da ƙasa sun kasance ɗinke,(1) sai Muka bũɗe su, kuma Muka sanya dukan kome mai rai daga ruwa? Shin, bã zã su yi ĩmãni ba?
31Kuma Mun sanya tabbatattun duwãtsu a cikin ƙasa dõmin kada ta karkata da su kuma Mun sanya ranguna, hanyõyi, a cikinsu (duwãtsun), tsammãninsu sunã shiryuwa.
32Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhãli kuwa su daga ãyõyinta mãsu bijirħwa ne.
33Kuma shĩ ne wanda Ya halitta dare da yini da rãnã da watã dukansu(2) a cikin wani sarari suKe iyo.
34Kuma ba Mu sanya dawwama ga wani mutum ba, a gabãninka. Shin to idan ka mutu to sũ ne madawwama?
35Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma Munã jarraba ku da sharri da alhħri dõmin fitina. Kuma zuwa gare Mu ake mayar da ku.
36Kuma idan waɗanda suka kãfirta suka gan ka, bã su riƙon ka fãce da izgili (sunã cħwa), "Shin, wannan ne ke ambatar gumãkanku?" Alhãli kuwa sũ, ga ambatar Mai rahama, mãsu kãfirta(1) ne.
37An halitta mutum daga gaggãwa, zan nũna muku ãyõyiNa. Sabõda haka kada ku nħmiyin gaggãwa.
38Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi zai tabbata, idan kun kasance mãsu gaskiya?"
39Dã waɗanda suka kãfirta sunã sanin lõkacin da bã su kange wuta daga fuskõkinsu, kuma haka daga bãyayyakinsu, alhãli kuwa ba su zama ana taimakon su ba.
40ôa, tanã jħ musu bisa ga auke sai ta ɗimautar da su, sa´an nan bã su iya mayar da ita, kuma ba su zama anã yi musu jinkiri ba.
41Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili ga waɗansu Manzanni daga gabãninka, sai abin da suka kasance sunã izgili da shi ya auku ga waɗanda suka yi izgilin daga gare su.
42Ka ce: "Wãne ne yake tsare ku a dare da yini daga Mai rahama?" ôa, sũ mãsu bijirħwa ne daga ambaton Ubangijinsu.
43Ko kuwa sunã da waɗansu abũbuwan bautãwa waɗanda ke tsare su, daga gare Mu? Bã su iya taimakon kansu kuma ba su kasance anã abũtar su(2) ba daga gareMu.
44ôa, Mun yalwata wa waɗannan da ubanninsu ni´imarMu, har rãyuwa ta yi tsawo a kansu. Shin, to, bã su ganin cħwa lalle Mũ, Munã je wa ƙasarsu, Munã rage(3) ta daga sãsanninta? Shin, to, su ne marinjaya?
45Ka ce: "Abin sani, inã yi muku gargaɗi kawai da wahayi," kuma kurma ba ya jin kira a lõkacin da ake yi musu gargaɗi.
46Kuma haƙĩƙa idan wata iska daga azãbar Ubangiji ta shãfe su, haƙĩƙa sunã cħwa, "Yã kaitonmu! Lalle mũ ne muka kasance mãsu zãlunci."
47Kuma Munã aza ma´aunan ãdalci ga Rãnar Ƙiyãma, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme. Kuma kõ dã ya kasance nauyin ƙwãya daga kõmayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Mãsu hisãbi.
48Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun kãwo wa Mũsã da Hãrũna Rarrabewa da haske da ambato ga mãsu aiki da taƙawa.
49Waɗanda suke tsãron Ubangijinsu a fake, alhãli kuwa sũ, mãsu sauna ne daga Sa´a.
50Kuma wannan ambato ne mai albarka Mun saukar da shi. Shin, to, kũ mãsu musu ne gare shi?
51Kuma lalle haƙĩƙa Mun kãwo wa Ibrãhĩm shiryuwarsa daga gabãni, kuma Mun kasance Masana gare shi.
52Ya ce wa ubansa da mutanensa, "Mħne ne waɗannan mutummutumai waɗanda kuke mãsu lazimta a kansu?"
53Suka ce: "Mun sãmi Ubanninmu mãsu lazimta a kansu."
54Ya ce: "Lalle, haƙĩƙa, kun kasance kũ da Ubanninku a cikin ɓata bayyananna."
55Suka ce: "Shin kã zo mana da gaskiya ne, Kõ kuwa kai kanã daga mãSu wãsã ne?"
56Ya ce: "ôa, Ubangijinku Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa, wanda Ya ƙãga halittarsu. Kuma Ni inã daga mãsu shaida a kan haka."
57"Kuma inã rantsuwa da Allah, lalle zan yi wani shiri ga gumãkanku a bãyan kun jũya kunã mãsu bãyar da bãya."
58Sai ya sanya su guntu-guntu fãce wani babba gare su, tsammãninsũ sunã Kõmãwa zuwa gare shi.
59Suka ce: "Wane ne ya aikata wannan ga gumãkanmu? Lalle shĩ, haƙĩƙa, yanã daga azzãlumai."
60Suka ce: "Mun ji wani saurayi yanã ambatar su. Anã ce masa Ibrahĩm."
61Suka ce: "To, ku zo da shi a kan idanun mutãne, tsammãnin su zã su bãyar da shaida."
62Suka ce: "Shin kai ne ka aikata wannan ga gumãkanmu? Yã Ibrahĩm!"
63Ya ce: "ôa, babbansu, wannan, shĩ ya aikata, shi. Sai ku tambaye su idan sun kasance sunã yin magana."
64Sai suka kõma wa jũnansu suka ce: "Lalle ne kũ, kũ ne azzãlumai."
65Sa´an nan kuma aka sunkuyar da su a kan kãwunansu (sukace,) "Lalle, haƙĩƙa, kã sani waɗannan bã su yin magana."
66Ya ce: "Shin to, kunã bautã wa abin da, bã ya, amfãnin ku da Kõme kuma bã ya cũtar da ku baicin Allah?"
67"Tir da ku, kuma da abin da kuke bauta wa, baicin Allah! Shin to, bã ku hankalta?"
68Suka ce: "Ku ƙõne shi kuma ku taimaki gumãkanku, idan kun kasance mãsu aikatãwa."
69Muka ce: "Yã wuta! Ki kasance sanyi da aminci ga Ibrahĩm."
70Kuma suka yi nufin wani mũgun shiri da shi, sai Mukasanya su mafiya hasãra.
71Kuma Muka tsħrar da shi da Lũɗu zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta ga tãlikai.
72Kuma Muka ba shi Is´haka da Ya´aƙuba a kan daɗi alhãli kuwa dukansu Mun sanya su sãlihai.
73Kuma Muka sanya su shugabanni, sunã shiryarwa da umurninMu. Kuma Muka yi wahayi zuwa gare su da ayyukan alhħri da tsayar da salla da bãyar da zakka. Kuma sun kasance mãsu bauta gare Mu.
74Kuma Lũɗu Mun bã shi hukunci da ilmi. Kuma Mun tsĩrar da shi daga alƙaryar nan wadda ke aikata mũnãnan ayyuka. Lallesũ, sun kasance mutãnen mũgun aiki, fãsiƙai.
75Kuma Muka shigar da shi a cikin rahamarMu. Lalle ne shĩ, yanã daga sãlihai.
76Kuma Nũhu, a sa´ad da ya yi kira a gabãni, sai Muka karɓa masa, sa´an nan Muka tsirar da shi da mutãnensa daga baƙin ciki mai girma.
77Kuma Muka taimake shi daga mutãnen nan waɗanda suka ƙaryata da ãyõyinMu. Lalle ne sũ, sun kasance mutãnen mugun aiki. Sai Muka nutsar da su gabã ɗaya.
78Kuma Dãwũda da Sulaimãn sa´ad da suke yin hukunci a cikin sha´anin shũka a lõkacin da tumãkin mutãne suka yi kiĩwon dare a cikinsa. Kuma Mun kasance Mãsu halarta ga hukuncinsu.
79Sai Muka fahimtar da ita (mats´alar)(1) ga Sulaiman. Kuma dukansu Mun bã su hukunci da ilmi kuma Muka hõre duwatsu tãre da Dãwũda, sunã tasbĩhi, da tsuntsãye. Kuma Mun kasance Mãsu aikatãwa.
80Kuma Muka sanar da shi sana´ar(2) wata tufa sabõda ku dõmin ya tsare ku daga makãminku. To, shin, ku mãsu gõdħwa ne?
81Kuma (Muka hõre) wa Sulaimãn iska mai tsananin bugãwa, tanã gudãna da umuruinsa zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta. Kuma Mun kasance Masana ga dukkan Kõme.
82Kuma daga Shaiɗannu (Mun hõre) wanda ke nutso sabõda shi. Kuma sunã yin wani aiki baicin wancan. Kuma Mun kasance Mãsu tsaro a gare su.
83Kuma da Ayyũba a sã´ad da ya yi kiran Ubangijinsa, (ya ce:) "Lalle nĩ, cũta ta shãfe ni, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama."
84Sai Muka karɓa masa, sa´an nan Muka kuranye abin da ke a gare shi na cũta, kuma Muka kãwo masa mutãnesa da kwatank wacinsu tãre da su, sabõda rahama daga wurinMu da tunãtarwa(1) ga mãsu ibãda.
85Kuma da Ismãĩla da Idrĩsa da Zulkifli, dukansu sunã daga mãsu haƙuri.
86Kuma Muka shigar da su a cikin rahamarMu. Lalle ne, sunã daga sãlihai.
87Kuma mai kifi(2) a sã´ad da ya tafi yanã mai hushi, sai ya yi zaton cħwa ba zã Mu ƙuƙunta masa ba. Sai ya yi kira a cikin duffai cħwa, "Bãbu abĩn bautãwa fãce Kai. Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle ne nĩ, na kasance daga azzãlumai."
88Sai Muka karɓa masa kuma Muka tsĩrar da shi daga baƙin ciki. Kamar haka ne Muke tsĩrarda masu ĩmãni.
89Kuma da Zakariyya a sa´ad da ya kirãyi Ubangijinsa cħwa, "Ya Ubangiji! Kada Ka bar ni makaɗaici alhãli kuwa Kai ne Mafi alhħrin mãsu gãdo."
90Sai Muka karɓa masa kuma Muka kyautata(3) masa mãtarsa. Lalle ne sũ, sun kasance sunã gudun tsħre zuwa ga ayyukan alhħri. Kuma sunã kiran Mu a kan kwaɗayi da fargaba. Kuma sun kasance mãsu saunar (aikata sãɓo) gare Mu.
91Kuma da wadda ta tsare farJinta daga alfãsha. Sai Muka hũra a cikinta daga rũhinMu.(1) Kuma Muka sanya ta ita da ɗanta wata ãyã ga dũniya.
92Lalle ne wannan(2) ita ce al´ummarku ta zama al´umma guda, kuma Nĩ ne Ubangijinku. Sai ku bauta Mini.
93Kuma suka kakkãtse al´amarinsu a tsakaninsu. Dukan Kõwanensu mãsu Kõmõwa zuwa gare Ni
94Dõmin wanda ya aikata daga ayyukan kwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bãbu musu ga aikinsa, kuma Mu Mãsu rubũtãwa gare shi ne.
95Kuma hananne ne a kan wata alƙarya da Muka halakar cħwa lalle sũ, bã su kõmõwa.
96Har sa´ad da aka bũde Yãjũju da Mãjũju alhãli kuwa sunã gaggãwa daga kõwane tudun ƙasa.
97Kuma wa´adin nan tabbatacce ya kusanto, sai gã ta idãnun waɗanda suka kãfirta sunã bayyanannu, (sunã cħwa), "Yã kaitonmu! Haƙĩƙa mun kasance a cikin gafala daga wannan! ôa, mun kasance dai mãsu zãlunci!"
98(A ce musu) "Lalle ne, kũ da abin(3) da kuke bautãwa, baicin Allah makãmashin Jahannama ne. Kũ mãsu tusgãwa gare ta ne."
99Dã waɗannan (abũbuwanbautãwar) sun kasance abũbuwan bautãwar gaskiya ne, dã ba su tusga mata ba, alhãli kuwa dukansu madawwama a cikinta ne.
100Sunã da wata hargõwa a cikinta, alhãli kuwa sũ, a cikinta, bã su saurãren kõme.
101Lalle ne waɗanda kalmar yabo tã gabãta a garħ su daga garħ Mu, waɗannan waɗanda ake nĩsantarwa daga barinta ne.
102Bã su jin sautin mõtsinta alhãli kuwa sũ madawwamãne a cikin abin da rãyukansu suka yi marmarinsa.
103Firgitar nan mafi girma, bã zã ta baƙantã musu rai ba. Kuma malã´iku na yi musu marãba (sunã cħwa) "Wannan yininku nħ wanda kuka kasance anã yi muku wa´adi da shi."
104A rãnar da Muke naɗe sãma kamar neɗħwar takarda ga abũbuwan rubũtãwa kamar yadda Muka fãra a farKon(1) halitta Muke mãyar da ita. Wa´adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa.
105Kuma lalle haƙĩƙa Mun rubũta a cikin Littãfi baicin Ambato(2) (Lauhul Mahfũz) cħwa ƙasã, bayĩNa sãlihai, sunã gãdonta.
106Lalle ne a cikin wannan (Alƙur´ãni), haƙĩƙa, akwai iyarwa (ga maganar da ta gabãta(3) ga waɗansu mutãne mãsu ibãda.
107Kuma ba Mu aike ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai.
108Ka ce: "Abin sani kawai, anã yin wahayi zuwa gare ni ne, cħwa, lalle ne, Abin bautãwarku, Abin bautãwa ne Guda. To shin kũ mãsu mĩƙa wuya ne?"
109Sa´an nan idan suka jũya, to, ka ce: "Nã sanar da ku, a kan daidaita, kuma ban sani ba, shin, abin da ake yi muku wa´adi makusanci ne Kõ kuwa manĩsanci?"
110"Lalle ne Shĩ (Allah) Yanã sanin bayyane daga magana, kuma Yanã sanin abin da kuke ɓõyħwa.
111"Kuma ban sani ba, tsammãninsa ya zama fitina a gare ku, kõ kuma don jin dãɗi, zuwa ga wani ɗan lõkaci."
112Ya ce: "Yã Ubangiji! Ka yi hukunci da gaskiya. Kuma Ubangijinmu Mai rahama ne Wanda ake nħman taimakonSa a kan abinda kuke siffantãwa."
Chapter 22 (Sura 22)
1Yã ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar(1) ƙasa ta tsayuwar Sa´a wata aba ce mai girma.
2A rãnar da kuke ganin ta dukan mai shãyar da mãma tanã shagala daga abin da ta shãyar, kuma dukan mai ciki tanã haihuwar cikinta, kuma kanã ganin mutãne sunã mãsu mãyħ alhãli kuwa su bã mãsu mãye ba, amma azãbar Allah ce mai tsanani.
3Akwai daga mutãne(2) wanda yake yin musũ ga sha´anin Allah bã da wani ilmi ba, kuma yanã biyar kõwane Shaiɗan mai taurin kai.
4An wajabta masa cħwa wanda ya jiɓince shi, to, lalle ne sai ya ɓatar da shi, kuma ya shiryar da shi zuwa ga azãbar sa´ĩr.
5Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin Ƙiyãma, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa´an nan kuma daga gudãjin jini, sa´an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa´an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa´an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa´an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau´i mai ban sha´awa.
6Wancan ne dõmin lalle Allah Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne shi Yake rãyar da matattu, kuma lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kõme.
7Kuma lalle ne Sa´ar Tãshin Ƙiyãma mai zuwa ce, bãbu shakka a cikinta kuma lalle ne Allah Yanã tãyar da waɗanda suke a cikin ƙaburbura.
8Kuma daga mutãne akwai mai yin musu(1) ga Allah bã da wani ilmi ba kuma bã da wata shiriya ba, kuma bã da wani littãfi mai haskakãwa ba.
9Yanã mai karkatar da sãshensa dõmin ya ɓatar (da wasu) daga tafarkin Allah! Yanã da wani wulãkanci a dũniya, kuma Munã ɗanɗana masa azãbar gõbara a Rãnar Ƙiyãma.
10(A ce masa): "Wancan azaba sabõda abin da hannayenka biyu suka gabatar ne, kuma lalle ne Allah bai zama Mai zãlunci ga bãyinSa ba."
11Kuma daga mutãne akwai mai bauta(2) wa Allah a kan wani gefe. Sa´an nan idan wani alhħri ya sãme shi, sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta sãme shi, sai ya jũya bãya a kan fuskarsa. Yã yi hasãrar dũniya da Lãhira. Waccan ita ce hasãra bayyananna.
12Yanã kiran baicin Allah, abin da bã ya cũtarsa da abin da bã ya amfãninsa! waccan ita ce ɓata mai nĩsa.
13Yanã kiran wanda yake lalle cũtarwarsa ce mafi kusa daga amfãninsa! Lalle ne, tir da shi ya zama majiɓinci, kuma tir da ya zama abõkin zama!
14Lalle ne Allah Yanã shigar da waɗanda suka yi ĩmãni(3) kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake nufi.
15Wanda ya kasance yanã zaton cħwa Allah bã zai taimake shi(4) ba a cikin dũniya da Lãhira to sai ya mĩƙa wata igiya zuwa sama, sa´an nan kuma ya yanke ta, sa´an nan ya dũba. Shin, ko lalle kaidinsa zai gusar da abin da yake ji na takaici?
16Kuma kamar haka Muka saukar da shi (Alƙur´ãni) yanã ãyõyi bayyanannu. Kuma lalle ne Allah Yanã shiryar da wanda Yake nufi.
17Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni da waɗanda suka tũba(1) (Yahũdu) da waɗanda suka karkace (Saba´ãwa) da Nasãra da Majũsãwa da waɗanda suka yi shirka, lalle ne Allah Yanã yin hukunci a tsakãninsu a Ranãr Ƙiyãma.Lalle ne Allah Mahalarci ne a kan dukkan kõme.
18Ashe, ba ka gani ba, lalle Allah, wanda yake a cikin sammai da wanda yake a cikin ƙasa yanã yin sujada a gare shi, da kuma rãna da watã da taurãri da duwãtsu da itãce da dabbõbi, da kuma mãsu yawa daga mutãne? Kuma waɗansu mãsu yawa azãba tã tabbata a kansu. Kuma wanda Allah Ya wulãkantar, to, bã ya da wani mai girmamãwa. Kuma Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake so.
19waɗannan ƙungiyõyi biyu(2) ne mãsu husũma, sun yi husũma ga sha´anin Ubangijinsu. To, waɗanda suka kãfirta an yanka musu waɗansu tufafi daga wata irin wuta, anã zuba tafasasshen ruwa daga bisa kãwunansu.
20Da shĩ ake narkar da abin da yake a cikin cikunansu da fãtun jikinsu.
21Kuma sunã da waɗansu gwalmõmin dũka na baƙin ƙarfe.
22A kõyaushe suka yi nufin fita daga gare ta, daga baƙin ciki, sai a mayar da su a cikinta, (a ce musu) "Ku ɗanɗani azãbar gõbara."
23Lalle ne, Allah Yana shigar da waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, anã ƙawãta su, a cikinsu, da waɗansu mundãye na zĩnãri da lu´u-lu´u. Kuma tufãfinsu a cikinsu alharĩni ne.(3)
24Kuma an shiryar da su zuwa ga mai kyau na zance kuma an shiryar da su zuwa ga, hanyar wanda ake gode wa.
25Lalle ne waɗanda suka kãfirta kuma suka taushe (mutãne) daga hanyar Allah da masallaci mai alfarma wanda Muka sanya shi ga mutãne alhãli kuwa mazauni a ciki da baƙauye daidai suke kuma wanda ya yi nufin karkatar(1) da gaskiya a cikinsa da zãlunci zã Mu ɗanɗana masa daga wata azãba mai raɗadi.
26Kuma a lõkacin da Muka iyãkance(2) wa Ibrãhim wurin Ɗakin (Muka ce masa), "Kada ka haɗa kõme da Ni ga bauta, kuma ka tsarkake ƊãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu tsayuwa da mãsu ruku´u da mãsu sujada.
27"Kuma ka yi yħkuwa ga mutãne da wajabcin Hajji su je maka suna mãsu tafiya da ƙafãfu da kuma a kan kõwane maɗankwarin rãƙumi mãsu zuwa daga kõwane rango mai zurfi."
28"Dõmin su halarci abũbuwan amfãni a gare su, kuma su ambãci sunan Allah a cikin ´yan kwãnuka sanannu sabõda abin da Ya azurta su da shĩ daga dabbõbin jin dãɗi. Sai ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da matsattse matalauci."
29"Sa´an nan kuma sai su ƙãre ibãdarsu da gusar da ƙazanta, knma sai su cika alkawuransu kuma sai su yi ɗawãfi (sunã għwaya) ga Ɗãkin nin ´yantacce."
30Wancan ne. Kuma wanda ya girmama hukunce-hukuncen Allah to shĩ ne mafĩfĩci a gare shi, a wurin Ubangijinsa. Kuma an halatta muku dabbõbin ni´ima(3) fãce abin da ake karantãwa a kanku. Sabõda haka ku nĩsanci ƙazanta daga gumãka kuma ku nĩsanci ƙazanta daga shaidar zur.
31Kuna mãsu tsayuwa ga gaskiya dõmin Allah, ba masu yin shirka da Shi ba. Kuma wanda ya yi shirka da Allah, to, yanã kamar abin da ya fãɗo daga sama, sa´an nan tsuntsãye su cafe shi, ko iska ta fãɗa da shi a cikin wani wuri mai nisa.
32Wancan ne. Kuma wanda ya girmama ibãdõdin Allah, to, lalle ne ita (girmamãwar) tanã daga ayyukan zukãta na ibãda.
33Kuna da waɗansu abũbuwan amfãni(1) a cikinta (dabbar hadaya) har ya zuwa ga wani ajali ambatacce, sa´an nan kuma wurin halattãta zuwa ga Ɗãkin ´yantacce ne.
34Kuma ga kõwace al´umma Mun sanya ibãdar yanka, dõmin su ambaci sũnan Allah a kan abin da Ya azurta su da shi daga dabbõbin ni´ima. Sa´an nan kuma Abin bautawarku Abin bautawa ne Guda, sai ku sallama Masa. Kuma ka yi bushãra ga mãsu ƙanƙantar da kai.
35Waɗanda suke idan an ambaci Allah sai zukãtansu su firgita, da mãsu haƙuri a kan abin da ya sãme su, da mãsu tsayar da salla, kuma sunã ciyarwa daga abin da Muka azurta su.(2)
36Kuma rãƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibãdõjin Allah. Kunã da wani alhħri babba a cikinsu. Sai ku ambaci sũnan Allah a kansu sunã tsaye(3) a kan ƙafãfu uku. Sa´an nan idan sãsanninsu suka fãɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da mai wadar zũci da mai bara. Kamar haka Muka hõre muku su, tsammãninku kunã gõdħwa.
37Nãmõminsu bã za su sãmi Allah ba haka jinainansu amma taƙawa daga gare ku tanã, sãmun Sa. Kamar haka Ya hõre su sabõda ku dõmin ku girmama Allah sabõda shiriyar da Ya yi muku. Kuma ka yi bushãra ga mãsu kyautata yi.
38Lalle ne, Allah Yanã yin faɗa(4) sabõda waɗanda suka yi ĩmãni. Lalle ne Allah bã Ya son dukkan mayaudari, mai yawan kãfirci.
39An yi izni ga waɗanda ake yãƙar su da cħwa lalle an zãlunce su, kuma lalle ne Allah, haƙĩƙa,Mai ĩkon yi ne a kan taimakonsu.
40Waɗanda aka fitina daga gidajensu bã da wani hakki ba fãce sunã cħwa, Ubangijinmu Allah ne."Kuma ba dõmin tunkuɗħwar Allah ga mutãne ba, sãshensu da sãshe, haƙĩƙa, da an rũsa sauma´õ´in (Ruhbãnãwa) dã majãmi´õ´in Nasãra da gidãjen ibãdar Yahudu da masallatai waɗanda ake ambatar Allah a cikinsu da yawa. Kuma lalle, haƙĩƙa, Allah Yanã taimakon wanda yake taimakon Sa. Lalle Allah ne haƙĩƙa Mai ƙarfi Mabuwãyi.
41Waɗanda suke idan Muka bã su ĩko a cikin ƙasa sai su tsai da salla, kuma su baybr da zakka kuma su yi umurni da abin da aka sani,(1) kuma su hana daga abin da ba a sani ba. Kuma ãƙibar al´amura ga Allah take.
42Kuma idan sun ƙaryata ka, to lalle haƙĩƙa, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdawa, sun ƙaryata a gabaninsu.
43Da mutãnen Ibrahim da mutãnen Lũɗu.
44Da mãsu Madyana, kuma an ƙaryata Mũsã. Sai Na jinkirtawa kãfiran, sa´an nan kuma Na kãma su. To, yãya musũNa (gare su) ya kasance?
45Sa´an nan da yawa daga alƙarya, Muka halaka ta, alhãli kuwa tanã mai zalũnci sai ta zama fãɗaɗɗa a kan rassanta, da yawa daga rĩjiya wadda aka wõfintar, da kuma gidãjen sarauta maɗaukaka.
46Shin, to, ba su yi tafiya ba a cikin ƙasa dõmin zukãta waɗanda zã su yi hankali da su da kunnuwa da za su yi saurãre da su su kasance a gare su? Dõmin lalle ne idãnun ba su makanta, amma zukãta waɗanda ke a cikin ƙirãza sũ ke makanta.
47Kuma sunã nħman ka yi gaggãwa da azãba, alhãli kuwa Allah bã zai sãɓa wa´adinSa ba kuma lalle ne, yini(1) ɗaya a wurin Ubangijinka kamar shħkara dubu yake daga abin da kuke ƙidãyãwa.
48Kuma da yawa daga alƙarya, Na yi jinkirin azãba gare ta (da laifinta) sa´an nan Na kãma ta, kuma zuwa gare Ni makõma take.
49Ka ce: "Ya ku mutãne! Nĩ wani mai gargaɗi ne kawai zuwa gare ku, mai bayyanawa."
50To, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, sunã da gãfara da arziki na karimci.
51Kuma waɗanda suka yi aikin ɓãtãwa a cikin ayõyinMu, sunã mãsu gajiyarwa, waɗancan ´yan Jahĩm ne.
52Kuma ba Mu aika wani manzo ba a gabãninka, kuma ba Mu umurci wani Annabi ba fãce idan ya yi bũri,(2) sai Shaiɗan ya jħfa (wani abu) a cikin bũrinsa, sa´an nan Allah Ya shãfe abin da Shaiɗan ke jefãwa. Sa´an nan kuma Allah Ya kyautata ãyõyinSa. Kuma Allah Masani ne, Mai hikima.
53Dõmin Ya sanya abin da Shaiɗan ke jħfãwa ya zama fitina ga waɗanda a cikin zukãtansu akwai cũta, da mãsu ƙħƙasassun zukãtansu. Kuma lalle ne azzãlumai haƙĩƙa, sunã a cikin sãɓãnimai nĩsa.
54Kuma dõmin waɗanda aka bai wa ilmi su sani lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka dõmin su yi ĩmãni da shi sabõda zukãtansu su natsu gare shi. Kuma lalle ne Allah, haƙĩƙa, Mai shiryar da waɗanda suka yi ĩmãni ne zuwa ga hanya madaidaiciya.
55Kuma waɗanda suka kãfirta bã zã su gushe ba sunã a cikin shakka daga gare shi, har Sa´a ta jħ musu bisa ga abke, kõ kuwa azãbar wani yini bakarãre ta jħ musu.
56Mulki a rãnar nan ga Allah yake, Yanã hukunci a tsakãninsu. To, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã a cikin gidãjen Aljannar ni´ima.
57Kuma waɗandra suka kãfirta kuma suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, to, waɗannan sunã da azãba mai wulãkantarwa.
58Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin tafarkin Allah sa´an nan kuma aka kashe su, kõ suka mutu, lalle ne Allah Yanã azurta su da arziki mai kyau. Kuma lalle ne Allah, haƙĩƙa, Shĩ ne Mafi alhħrin mãsu azurtãwa.
59Lalle ne, Yanã shigar da su a wata mashiga wadda zã su yarda da ita. Kuma lalle ne Allah, haƙĩƙa Masani ne, Mai haƙuri.
60Wancan! Kuma wanda ya rãma azãba da misãlin abin da aka yi masa, sa´an nan kuma aka zãlunce shi, lalle ne Allah Yanã taimakon sa. Lalle ne Allah haƙĩƙa Mai yãfħwa ne, Mai gãfara.
61Wancan! sabõda Allah Yanã shigar da dare a cikin yini, kuma Yanã shigar da yini a cikin dare, kuma lalle, Allah Mai jĩ ne,Mai gani.
62Wancan! sabõda lalle ne Allah, shĩ ne Gaskiya, kuma lalle ne, abin da suke kira waninSa shi ne ƙarya. Kuma lalle ne Allah, Shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma.
63Ashe, ba ka gani ba, lalle ne, Allah Yã saukar da ruwa(1) daga sama, sai ƙasa ta wãyi gari kõriya? Lalle Allah Mai tausasawa ne, Mai ƙididdigewa.
64Abin da ke a cikin sammai, da abin da ke a cikin ƙasa, Nasa ne, kuma lalle ne Allah, haƙĩƙa,Shi ne wadatacce, Gõdadde.
65Shin ba ka gani ba, lalle ne Allah Ya hõre muku abin da yake a cikin ƙasa, kuma jirãge sunã gudãna a cikin tħku, da umurninSa kuma Yanã riƙe sama dõmin kada ta fãɗi a kan ƙasa fãce da izninsa? Lalle ne Allah ga mutãne haƙĩƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai.
66Kuma shĩ ne wanda Ya rãya ku, sa´an nan kuma Yanã matar da ku, sa´an nan kuma Yanã rãyar da ku. Lalle mutum, haƙĩƙa, mai kãfirci ne.
67Ga kõwace al´umma Mun sanya wurin yanka, su ne masu yin baiko gare Shi, sabõda haka, kada su yi maka jãyayya a cikin al´amarin (hadaya). Kuma ka yi kira zuwa ga Ubangijinka lalle kai kana a kan shiriya madaidaiciya.
68Kuma idan sun yi maka jidãli, sai ka ce: "Allah ne Mafi sani game da abin da kuke aikatãwa."
69"Allah ne zai yi hukunci a tsakãninku, a Rãnar Ƙiyãma a cikin abin da kuka kasance a cikinsa kunã sãɓawa jũna."
70Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yanã sanin abin da yake a cikin sama da ƙasa? Lalle ne wancan yanã cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne.
71Kuma sunã bautãwa baicin Allah, abin da (Allah) bai saukar da wani dalili ba game da shi, kuma abin da bã su da wani ilmi game da shi, kuma bãbu wani mai taimako ga azzãlumai.
72Kuma idan anã karanta ãyõyinMu bayyanannu a kansu kanã sanin abin ƙyãma a cikin fuskõkin waɗanda suka kãfirta sunã kusa su yi danƙa ga waɗanda ke karãtun ayõyinMu a kansu. Ka ce: "Shin to in gaya muku abin da yake mafi sharri daga wannan? (Ita ce) Wuta." Allah Yã yi alkawarinta ga waɗanda suka kãfirta. Kuma makõmarsu ta mũnana.
73"Ya ku mutãne! An buga wani misãli, sai ku saurãra zuwa gare shi. Lalle ne waɗanda kuke kira baicin Allah, bã zã su halitta ƙudã ba, kõ da sun tãru gare shi, kuma idan ƙudãn ya ƙwãce musu wani abu, bã zã su kuɓutar da shi ba daga gare shi. Mai nħma da wanda ake nħman gare shi sun raunana."
74Ba su ƙaddara wa Allah hakkin girmanSa ba. Lalle ne Allah, haƙĩƙa, Mai ƙarfi ne, Mabuwãyi.
75Allah nã zãɓen Manzanni daga malã´iku kuma daga mutãne.(1) Lalle Allah, Mai ji ne, Mai gani.
76Yanã sanin abin da ke gaba gare su da abin da ke bãyansu, kuma zuwa ga Allah ake mayar da al´amura.
77Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi rukũ´i, kuma ku yi sujada, kuma ku bauta wa Ubangijinku, kuma ku aikata alhħri, tsammãninku, ku sami babban rabo.
78Kuma ku yi jihãdi a cikin (al´amarin) Allah, hakkin JihãdinSa. shĩ ne Ya zãɓe ku alhãli kuwa bai sanya wani ƙunci(2) ba a kanku a cikin addĩni. Bisa ƙudurcħwar ubanku Ibrãhĩm, shĩ ne ya yi muku sũna Musulmi(3) daga gabãnin haka. Kuma a cikin wannan (Littãfi ya yi muku sũna Musulmi), dõmin Manzo ya kasance mai shaida a kanku, kũ kuma ku kasancemãsu shaida a kan mutãne. Sabõda haka ku tsayar da salla kuma ku bãyar da zakka kuma ku amince da Allah, Shi ne Majiɓincinku. Sãbõda haka mãdalla da Shi Ya zama Majiɓinci, mãdalla da Shi ya zama Mai taimako.
Chapter 23 (Sura 23)
1Lalle ne, Mũminai(1) sun sãmi babban rabõ.
2Waɗanda suke a cikin sallarsu mãsu tawãli´u ne.
3Kuma waɗanda suke, sũdaga barin yasassar magana, mãsu kau da kai ne.
4Kuma waɗanda suke ga zakka mãsu aikatãwa ne.
5Kuma waɗanda suke ga farjõjinsu mãsu tsarħwa ne.
6Fãce a kan mãtan aurensu, kõ kuwa abin da hannayen dãmansu suka mallaka to lalle sũ bã waɗanda ake zargi, ba, ne.
7Sabõda haka wanda ya nħmi abin da ke bãyan wancan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙħtarħwar haddi.
8Kuma waɗanda suke, sũga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarħwa ne.
9Kuma da waɗanda suke, sũ a kan sallõlinsu sunã tsarħwa.
10Waɗannan, sũ ne magãda.
11Waɗanda suke gãdõn (Aljannar) Firdausi,(2) su a cikinta madawwama ne.
12Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka.
13Sa´an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya.
14Sa´an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa´an nan Muka halitta gudan jinin tsõka, sa´an nan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sa´an nan Muka tufãtar da ƙasũsuwan da wani nãma sa´an nan kuma Muka ƙãga shi wata halitta dabam. Sabõda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun mãsu halittawa.
15Sa´an nan kuma ku, bãyan wannan, lalle ne masu mutuwa ne.
16Sa´an nan kuma lalle ne kũ a Rãnar Ƙiyãma, za a iãyar da ku,
17Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halitta, a samanku, hanyõyi bakwai, kuma ba Mu kasance, daga barin halittar, Mãsu shagala ba.
18Muka saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado, sa´an nan Muka zaunar da shi a cikin ƙasa alhãli, lalle ne Mũ, a kan tafiyar da shi, Mãsu iyãwa ne.
19Sai Muka ƙãga muku, game da shi (ruwan), gõnaki daga daĩnai da inabõbi, kunã da, a cikinsu, ´ya´yan itãcen marmari mãsu yawa, kuma daga gare su kuke ci.
20Da wata itãciya,(1) tanã fita daga dũtsin Sainã´a, tanã tsira da man shãfãwa, da man miya dõmin masu cĩ.
21Kuma lalle ne kunã da abin lũra a cikin dabbõbin ni´imõmi Munã shãyar da ku daga abin da yake a cikinsu, kuma kunã da a cikinsu abũbuwan amfãni(2) mãsu yawa, kuma daga gare su kuke cĩ
22Kuma a kansu da a kan jirgin ruwa ake ɗaukar ku.
23Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnensa, sai ya ce: "Yã mutãnħna! Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa waninsa. Shin, to, bã za ku yi taƙawa ba?"
24Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa, suka ce: "Wannan ba kõwa ba ne, fãce mutum misãlinku, yanã nufin ya ɗaukaka a kanku. Dã Allah Yã so, lalle ne dã Yã saukar da Malã´iku, Ba muji (kõme)ba, game da wannan, a cikin ubanninmu na farko."
25"Shi bai zamo kõwa ba fãce wani namiji ne, a gare shi akwai hauka, sai ku yi jinkiri da shi har wani lõkaci."
26Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimakeni sabõda sun ƙaryatani."
27Sai Muka yi wahayi zuwa gare shi. "Ka sana´anta jirgin bisa ga idonMu, da wahayinMu. To, idan umuminMu ya jħ, kuma tandã ta ɓuɓɓuga da ruwa, to, ka shigar a cikinta daga kõme, ma´aura biyu, da iyãlanka, sai wanda Magana ta gabãta a kansa, daga gare su, kuma kada ka rõƙħ Ni (sabõda wani) a cikin waɗanda suka yi zãlunci, lalle ne sũ waɗanda ake nutsarwa ne.
28"Sa´an nan idan ka daidaitu kai da waɗanda ke tãre da kai a kan jirgin, sai ka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya tsĩrar damu daga mutãne azzãlumai."
29"Kuma ka ce: ´Ya Ubangijĩna! Ka saukar da ni, saukarwa mai albarka. Kuma Kai ne Mafi alhħrin mãsu saukarwa.´"
30Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi, ko da yake Mun kasance, haƙħƙa´ Mãsu jarrabãwa.
31Sa´an nan kuma Muka ƙãga wani ƙarni na waɗansu dabam daga bãyansu.
32Sai Muka aika a cikinsu Manzo daga gare su. "Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa, sai Shi. Shin to, bã zã ku yi taƙawa ba?"
33Mashãwarta daga mutãnensa, waɗanda suka kãfirta kuma suka ƙaryata game da haɗuwa da Lãhira, kuma Muka ni´imtar da su a cikin rãyuwar dũniya, suka ce: "Wannan bã kõwa ba fãce wani mutum ne kamarku, yanã cĩ daga abin da kuke cĩ daga gare shi, kuma yanã shã daga abin da kuke shã."
34"Kuma lalle ne idan kun yi ɗã´ a ga mutum misãlinku, lalle ne, a lõkacin nan, haƙĩƙa, kũ mãsu hasãra ne."
35"Shin, yanã yi muku wa´adin (cħwa) lalle kũ, idan kun mutu kuma kuka kasance turɓãya da ɓasũsuwa lalle ne kũ waɗanda ake fitarwa ne?"
36"Faufau faufau ga abin da ake yi muku wa´adi da shi."
37"Rãyuwa ba ta zama ba fãce rãyuwarmu ta dũniya, munã mutuwa kuma munã rãyuwa,(1) kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
38"Bai zama kõwa ba fãce namiji, ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma ba mu zama, sabõda shi, mãsu ĩmãni ba."
39Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimake ni sabõda sun ƙaryatã ni."
40Ya ce: "Daga abu kaɗan, lalle ne zã su wãyi gari sunã mãsu nadãma."
41Sai tsãwa ta kãma su da gaskiya, sai Muka sanya su tunkuɓa. Sabõda haka nĩsa ya tabbataga mutãne azzãlumai!
42Sa´an kuma Muka ƙãga halittar wasu ƙarnõni dabam daga bayãnsu.
43Wata al´umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
44Sa´an nan kuma Muka aika da ManzanninMu jħre a kõda yaushe Manzon wata al´umma ya jħ mata, sai su ƙaryata shi, sabõda haka Muka biyar da sãshensu ga sãshe, kuma Muka sanya su lãbãrun hĩra. To, nĩsa ya tabbata ga mutãne (waɗanda) bã su yin ĩmãni!
45Sa´an nan kuma Muka aika Mũsã da ɗan´uwansa Hãrũna, game da ãyõyinMu da, dalĩli bayyananne.
46Zuwa ga Fir´auna da majalisarsa, sai suka kangara, alhãli sun kasance mutãne ne marinjãya.
47Sai suka ce: "Shin, zã Mu yi ĩmãni sabõda wasu mutãne biyu misãlinmu, alhãli kuwa mutãnensu a gare mu, mãsu bauta ne."
48Sai suka ƙaryata su sabõda haka suka kasance halakakku.
49Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã littãfi tsammaninsu(1) zã su shiryu.
50Kuma Mun sanya Ɗan Maryama, shi da uwarsa wata ãyã(2) Kuma Muka tattara su zuwa ga wani tsauni ma´abũcin natsuwa da marħmari.
51Yã ku Manzanni! Ku ci daga abũbuwa mãsu dãɗi(3) kuma ku aikata aikin ƙwarai. Lalle Nĩga abin da kuke aikatãwa, Masani ne.
52Kuma lalle ne, wannan al´ummarku ce, al´umma guda, kuma Nĩ, Ubangijinku ne, sai ku bĩ Ni da taƙawa.(4)
53Sai (al´ummar) suka yanyanke al´amarinsu a tsakãninsu guntu-guntu,(5) kõwace ƙungiya sunã mãsu farin ciki da abin da yake a gare su.
54To, ka bar su a cikin ɓatarsu har a wani lõkaci.
55Shin, sunã zaton cħwa abin da Muke taimakon su da shi daga dũkiya da ɗiya,
56Munã yi musu gaggãwa ne a cikin alhħrõri?
57Lalle ne waɗanda suke mãsu sauna sabo da tsõron Ubangijinsu,
58Da waɗanda suke, game da ãyõyin Ubangijinsu sunã ĩmãni,
59Da waɗanda suke game da Ubangijinsu bã su yin shirki,
60Da waɗanda ke bãyar da abin da suka bãyar, alhãli kuwa zukãtansu sunã tsõrace dõmin sunã kõmãwa zuwa ga Ubangijinsu,
61Waɗancan sunã gaggãwar tsħre a cikin ayyukan alhħri, alhãli kuwa sunã mãsu tsħrħwa zuwa gare su (ayyukan alhħri).
62Kuma bã Mu kallafa wa rai fãce abin iyawarsa, kuma a wurinMu akwai wani Littãfi wanda yake magana da gakiya, kuma sũ bã a zãluntar su.
63ôa, zukãtansu sunã cikin jãhilci daga wannan (magana), kuma sunã da waɗansu ayyuka, baicin wancan, sũ a gare su,mãsu aikatãwa ne.
64Har idan Mun kãma mani´imtansu da azãba, sai gã su sunã hargõwa.
65Kada ku yi hargowa a yau, lalle ne kũ, daga gare Mu bã a taimakon ku.
66Lalle ne, ãyõyĩNa sun kasance anã karãtun su a kanku, sai kuka kasance, a kan dugãduganku, kunã kõmãwa bãya.
67Kunã mãsu girman kai gare shi (Annabi), da hĩrã kunã alfãsha.
68Shin fa, ba su yi ta´ammalin maganar (Alƙur´ãni) ba, kõ abin da bai jħ wa ubanninsu na farko ba ne ya jħ musu?
69Kõ ba su san Manzonsu ba ne dõmin haka suke mãsu musu a gare shi?
70Kõ sunã cħwa, "Akwai hauka gare shi?" ôa, yã zo musu da gaskiya, alhãli kuwa mafi yawansu, ga gaskiya, mãsu ƙi ne.
71Kuma dã gaskiya (Alƙur´ãni) yã bi son zuciyoyinsu, haƙĩƙa dã sammai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sun ɓãci. ôa, Mun tafo musu da ambaton(1) (darajar) su, sa´an nan sũ daga barin ambaton su mãsu bijirħwa ne, bijirħwa.
72Kõ kanã tambayar su wani harãji ne (a kan iyar da Manzanci a gare su)? To, harãjin Ubangijinka ne mafi alhħri kuma Shĩ ne Mafi alhħrin mãsu ciyarwa.
73Kuma lalle ne kai haƙĩƙa kanã kiran su zuwa ga hanya madaidaiciya.
74Kuma lalle waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba mãsu karkacħwa daga hanya ne.
75Kuma dã Mun ji tausayinsu, kuma Muka kuranye musu abin da yake tãre da su na cũta, lalle ne dã sun yi zurfi a cikin ɓatarsu, sunã ɗimuwa.
76Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã kãma su da azãba(1) sai dai ba su saukar da kai ba, ga Ubangijinsu, kama bã su yin tawãli´u.
77Har idan Mun bũɗe, akansu, wata ƙõfa mai azãba mai tsanani sai gã su a cikinta sunã mãsu mugi.(2)
78Kuma Shi ne Wanda Ya ƙãga halittar ji da gani da zukãta dominku. Kaɗan ƙwarai kuke gõdħwa.
79Kuma Shĩ ne Ya halitta ku a cikin ƙasa, kuma zuwa gare Shi ake tãyar da ku.
80Kuma Shĩ ne Wanda Yake rãyarwa, kuma Yanã matarwa, kuma a gare Shi ne sãɓawar dare da yini take. Shin, to, bã zã ku hankalta ba?
81ôa, sun faɗi misãlin abin da na farko suka faɗa.
82Suka ce: "Shin idan mun mutu kuma muka kasance turɓaya da ƙasũsuwa shin lal1e ne mu haƙĩƙa waɗanda ake tãyarwa ne?
83"Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa´adi, mũ da ubanninmu ga wannan a gabãni, wannan abu bai zama kõme ba, fãce tãtsũniyõyin na farko."
84Ka ce: "Wane ne da mulkin ƙasa da wanda ke a cikinta, idan kun kasance kunã sani?"
85Zã su ce: "Ta Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku yi tunãni ba?"
86Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al´arshi mai girma?"
87Zã su ce: "Na Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku bĩ Shi da taƙawa ba?"
88Ka ce: "Wãne ne ga hannunsa mallakar kõwane abu take alhãli kuwa shi yanã tsarħwar wani, kuma ba a tsare kõwa daga gare shi, idan kun kasance kunã sani?"
89Zã su ce: "Ga Allah yake." Ka ce: "To, yãya ake sihirce ku?"
90ôa, Mun zo musu da gaskiya, kuma lalle ne sũ, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
91Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa.
92Masanin ɓõye da bayyane. sa´an nan Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka.
93Ka ce: "Yã Ubangijina! Ko dai Ka nũna mini abin da ake yi musu wa´adi da shi."
94"Yã Ubangijina, to, kada Ka sanya ni a cikin mutãne azzãlumai."
95Kuma lalle ne Mũ haƙĩƙa Mãsu iyawa ne a kan Mu nũna maka abin da Muke yi musu wa´adi da shi.
96Ka tunkuɗe cũta da wadda take ita ce mafi kyau. Mũ neMafi sani game da abin da suke siffantãwa.
97Ka ce: "Yã Ubangijĩna, inã nħman tsari da Kai daga fizge-fizgen Shaiɗãnu."
98"Kuma inã nħman tsari da Kai, ya Ubangijĩna! Dõmin kada su halarto ni,(1) "
99Har idan mutuwa ta jħ wa ɗayansu, sai ya ce: "Yã Ubangijina, Ku mayar da ni (dũniya)."
100"Tsammãnina in aikata aiki na ƙwarai cikin abin da na bari." Kayya! Lalle ne ita kalma ce, shĩ ne mafaɗinta, alhãli kuwa a bãya gare su akwai wani shãmaki har rãnar da zã a tãyar da su.
101Sa´an nan idan an yi bũsa a cikin ƙaho, to, bãbu dangantakõki a tsakãninsu a rãnar nan kuma bã zã su tambayi jũnansu ba.
102To, wadanda sikħlinsu ya yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
103Kuma waɗanda sikħlinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu sunã madawwama a cikin Jahannama.
104Fuskokinsu sunã balbalar wuta, kuma su a cikinta mãsu yãgaggun leɓɓa daga haƙõra ne.
105"Shin, ayõyĩNa ba su kasance anã karanta su a kanku ba sai kuka kasance game da su kunã ƙaryatãwa?"
106Suka ce: "Yã Ubangijinmu, shaƙãwamiu ce ta rinjãya a kanmu, kuma mun kasance mutãne ɓatattu."
107"Yã Ubangjinmu! Ka fitar da mu daga gare ta, sa´an nan idan mun kõma, to, lalle ne, mũ ne mãsu zãlunci."
108Ya ce: "Ku tafi (da wulãkanci) a cikinta. Kada ku yi Mini magana."
109Lalle ne waɗansu ƙungiyoyi daga bãyiNa sun kasance sunã cħwa, "Yã Ubangijinmu! Mun yi ĩmãni, sai Ka gãfarta mana, kuma Ka yi mana rahama, kuma Kai ne Mafi alhħrin mãsu tausayi."
110Sai kuka riƙe su lħburõri har suka mantar da ku ambatõNa kuma kun kasance, daga gare su kuke yin dãriya.
111Lalle ne Nĩ Inã sãka musu a yau, sabõda abin da suka yi wa haƙuri. Dõmin lalle ne sũ sũ ne mãsu sãmun babban rabo.
112Ya ce: "Nawa kuka zauna a cikin ƙasa na ƙidãyar shħkaru?"
113Suka ce: "Mun zauna a yini ɗaya ko rabin yini, sai ka tambayi mãsu ƙidãyãwa."
114Ya ce: "Ba ku zauna ba fãce kaɗan, dã dai kun kasance kunã sani."
115"Shin, to, kun yi zaton cħwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba?"
116Allah Mamallaki gaskiya, Yã ɗaukaka. Bãbu abin bautãwa, fãce Shi. Shĩ ne Ubangijin Al´arshi, mai daraja.
117Kuma wanda ya kira, tãre da Allah, waɗansu abũbuwan bautãwa na dabam, bã yanã da wani dalĩli game da shĩ (kiran) ba, to hisãbinsa yanã wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kãfirai bã su cin nasara.
118Kuma ka ce: "Yã Ubangijina! Ka yi gãfara, Ka yi rahama, kuma Kai ne Mafi alhħrin mãsu rahama."
Chapter 24 (Sura 24)
1(Wannan) sũra ce. Mun saukar da ita, kuma Mun wajabta ta, kuma Mun saukar da ãyõyi bayyanannu a cikinta, dõmin ku riƙa tunãwa.
2Mazinãciya da mazinãci,(1) to, ku yi bũlãla ga kõwane ɗaya daga gare su, bũlãla ɗari. Kuma kada tausayi ya kãma ku game da su a cikin addinin Allah idan kun kasance kunã yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Kuma wani yankin jama, a daga mũminai, su halarci azãbarsu.
3Mazinãci bã ya aure(2) fãce da mazinãciya kõ mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai aurenta fãce mazinãci kõ mushiriki. Kuma an haramta wannan a kan mũminai.
4Kuma waɗanda ke jĩfar(3) mãtã masu kãmun kai, sa´an nan kuma ba su jħ da shaidu huɗu ba to, ku yi musu bũlãla, bũlãla tamãnin, kuma kada ku karɓi wata shaida tãsu, har abada. Waɗancan su ne fãsiƙai.
5Fãce waɗanda suka tũbadaga bãyan wannan, kuma suka gyãru, to lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
6Kuma waɗanda ke jĩfar mãtan(4) aurensu kuma waɗansu shaidu ba su kasance a gare su ba, fãce dai kansu, to, shaidar ɗayansu, shaida huɗu ce da Allah, ´Lalle shĩ, haƙĩƙa, yanã daga magasganta.´
7Kuma ta biyar cħwa ´La´anar Allah ta tabbata a kansa, idan ya kasance daga maƙaryata.´
8Kuma yanã tunkuɗe mata azãba ta yi shaida, shaida huɗu da Allah, ´Lalle shĩ haƙĩƙa, yanã daga maƙaryata.´
9Kuma tã biyar cħwa ´Hushin Allah ya tabbata a kanta idan ya kasance daga magasganta.´
10Kuma bã dõmin falalar Allah ba a kanku, da rahamarSa, kuma cħwa Allah Mai karɓar tũba ne, Mai hikima!
11Lalle ne waɗanda(1) suka zo da ƙiren ƙarya waɗansu jama´a ne daga gare ku, kada ku yi zatonsa sharri ne a gare ku. ôa, alhħri ne gare ku. Kõwane mutum daga gare su na da sakamakon abin da ya sanã´anta na zunubi, kuma wanda ya jiɓinci girmansa, daga gare su, yanã da azãba mai girma.
12Don me a lõkacin da kuka ji shi mũminai maza da mũminai mãta ba su yi zaton alhħri game da kansu ba kuma su ce: "Wannan ƙiren ƙarya ne bayyananne?"
13Don me ba su zo da shaidu huɗu a kansa ba? To idan ba su kãwo shaidun nan ba to, waɗannan, a wurin Allah, sũ ne maƙaryata.
14Kuma bã dõmin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa a cikin dũniya da Lãhira. Lalle ne,dã azãba mai girma ta shãfe ku a cikin abin da kuka kũtsa da magana a cikinsa.
15A lõkacin da kuke marãbarsa da harsunanku kuma kunã cħwa da bakunanku abin da bã ku da wani ilmi game da shi, kuma kunã zaton sa mai sauƙi alhãli kuwa, shi a wurin Allah, babba ne.
16Kuma don me a lõkacin da kuka ji shi, ba ku ce ba, "Bã ya yiwuwa a gare mu, mu yi magana a game da wannan. Tsarki ya tabbata a gare Ka, wannan ƙiren ƙarya ne mai girma"?
17Allah Yanã yi muku wa´azi, kada ku kõma ga irinsa, har abada, idan kun kasance mũminai.
18Kuma Allah Yanã bayyana muku ãyõyinSa, kuma Allah Masani ne, Mai hikima.
19Lalle ne waɗanda ke son alfãsha ta wãtsu ga waɗanda suka yi ĩmãni sunã da azãba mai raɗaɗi a cikin dũniya da Lãhira. KumaAllah, Shi ne Ya sani, alhãli kuwa, kũ ba ku sani ba.
20Kuma bã dõmin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa. Kuma lalle ne Allah Mai tausayi ne, Mai jin ƙai!
21Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni, kada ku bi hanyõyin Shaiɗan. Kuma wanda ke bin hanyõyin Shaiɗan, to, lalle ne shi, yanã umurni da yin alfãsha da abin da ba a sani ba, kuma bã dõmin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa, bãbu wani mutum daga gare ku da zai tsarkaka har abada, kuma amma Allah Yanã tsarkake wanda Yake so kuma Allah Mai ji ne, Masani.
22Kuma kada(1) ma´abũta falala daga gare ku da mawadãta su rantse ga rashin su bãyar da alhħri ga ma´abũta zumunta da miskĩnai da muhãjirai, a cikin hanyar Allah. Kuma su yãfe, kuma su kau da kai. shin, bã ku son Allah Ya gãfarta muku, alhãli Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?
23Lalle ne waɗannan da suke jĩfar mãtã mãsu kãmun kai gãfilai(2) mũminai, an la´ane su, a cikin dũniya da Lãhira, kuma sunãda azãba mai girma.
24A rãnar da harsunansu da hannãyensu, da ƙafãfunsu suke bãyar da shaida a kansu, game da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
25a rãnar dl Allah Yake cika musu sakamakonsu tabbatacce kuma sunã sanin (cħwa) lalle Allah, Shi ne Gaskiya bayyananna.
26Miyãgun mãtã dõmin miyagun(3) maza suke, kuma miyãgun maza dõmin miyãgun mãtã suke kuma tsarkãkan mãtã dõmin tsarkãkan maza suke kuma tsarkãkan maza dõmin tsarkãkan mãtã suke. waɗancan sũ ne waɗanda ake barrantãwa daga abin da (mãsu ƙazafi) suke faɗa kuma sunã da gãfara da arziki na karimci.
27Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku shiga gidãje waɗanda bã gidãjenku ba sai kun sãmi izni, kuma kun yi sallama(4) a kan ma´abũtansu. Wannan ne mafi alhħri gare ku, tsammaninku, zã ku tuna.
28To, idan ba ku sãmi kõwa a cikinsu ba, to, kada ku shige su, sai an yi muku izni. Kuma idan an ce muku, "Ku kõma." Sai ku kõma, shi ne mafi tsarkaka a gare ku. Kuma Allah game da abin da kuke aikatãwa, Masani ne.
29Bãbu laifi a kanku, ga ku shiga gidãje waɗanda bã zaunannu ba, a cikinsu akwai waɗansu kãya nãku. Kuma Allah Yanã sanin abin da kuke nũnãwa, da abin dakuke ɓãyħwa.
30Ka ce wa mũminai maza su runtse daga ganinsu, kuma su tsare farjõjinsu.(1) wannan shĩ ne mafi tsarki a gare su. Lalle ne, Allah, Mai ƙididdigewa ne ga abin da suke sanã´antãwa.
31Kuma ka ce wa mũminai mãta su runtse daga gannansu, kuma su tsare farjõjinsu kuma kada su bayyana ƙawarsu fãce abin da ya bayyana daga gare ta, kuma su dõka da mayãfansu a kan wuyan rigunansu, kuma kada su nũna ƙawarsu fãce ga mazansu ko ubanninsu ko ubannin mazansu, ko ɗiyansu, ko ɗiyan mazansu, ko ´yan´uwansu, ko ɗiyan ´yan´uwansu mãtã, kõ mãtan(2) ƙungiyarsu, ko abin da hannãyensu na dãma suka mallaka, ko mabiya wasun mãsu bukãtar mãta daga maza, kõ jãrirai waɗanda. bã su tsinkãya a kan al´aurar mãtã. Kuma kada su yi dũka da ƙafãfunsu dõmin a san abin da suke ɓõyħwa daga ƙawarsu.Kuma ku tũba zuwa ga Allah gabã ɗaya, yã ku mũminai! Tsammãninku, ku sãmi babban rabo.
32Kuma ku aurar da gwaurãye daga gare ku, da sãlihai daga bãyinku, da kuyanginku. Idan sun kasance matalauta Allah zai wadãtar da su daga falalarSa. Kuma Allah Mawadãci ne, Masani.
33Kuma waɗannan da ba su sãmi aure ba su kãme kansu har Allah Ya wadãtar da su daga, falalarsa. Kuma waɗanda ke nħman fansa daga abin da hannuwanku na dãma suka mallaka, to, ku ɗaura musu fansã idan kun san akwai wani alhħri a cikinsu kuma ku bã su wani abu daga dũkiyar Allah wannan da Ya bã ku. Kuma kada ku tĩlasta kuyanginku a kan yin zina, idan sun yi nufin tsaron kansu,(1) dõmin ku nħmi rãyuwar dũniya, kuma wanda ya tĩlasta su to, lalle Allah, a bãyan tĩlasta su, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
34Kuma lalle ne Mun saukar zuwa gare ku, ãyõyi mãsu bayyanãwa, da misãli daga waɗanda suka shige daga gabãninku, da wa´azi ga mãsu taƙawa.
35Allah ne Hasken sammai da ƙasa, misãlin HaskenSa, kamar tãgã, a cikinta akwai fitila, fitilar a cikin ƙarau, ƙarau ɗin kamar shi taurãro ne mai tsananin haske, anã kunna shi daga wata itãciya mai albarka, ta zaitũni, bã bagabashiya ba kuma bã bayammaciya ba, manta na kusa ya yi haske, kuma kõ wuta ba ta shãfe shi ba, haske a kan haske, Allah na shiryar da wanda Yake so zuwa ga HaskenSa. Kuma Allah na buga misãlai ga mutãne, kuma Allah game da dukan kõme, Masani ne.
36A cikin waɗansu gidãje waɗanda Allah Yã yi umurnin a ɗaukaka kuma a ambaci sũnansa a cikinsu, sunã yin tasbĩhi a gare Shi a cikinsu, sãfe da maraice.
37Waɗansu maza, waɗanda wani fatauci bã ya shagaltar da su, kuma sayarwa bã ta shagaltar da su daga ambaton Allah, da tsai da salla da bãyar da zakka, sunã tsõron wani yini wanda zukãta sunã bibbirkita a cikinsa, da gannai.
38Dõmin Allah Ya sãka musu da mafi kyaun abin da suka aikata, kuma Ya ƙãra musu daga falalarsa. Kuma Allah Yanã azurta wanda Yake so, bã da lissafi ba.
39Kuma waɗanda suka ƙãfirta ayyukansu sunã kamar ƙawalwalniyã ga faƙo, mai ƙishirwa yanã zaton sa ruwa, har idan ya jħ masa bai iske shi kõme ba, kuma ya sãmi(1) Allah a wurinsa, sai Ya cika masa hisãbinsa. Kuma Allah Mai gaggãwar sakamako ne.
40Kõ kuwa kamar(2) duffai a cikin tħku mai zurfi, tãguwar ruwa tanã rufe da shi, daga bisansa akwai wata tãguwa, daga bisansa akwai wani girgije, duffai sãshensu a bisa sãshe, idan ya fitar da tãfinsa ba ya kusa ya gan shi. Kuma wanda Allah bai sanya masa haske ba, to, bã ya da wani haske.
41Shin, ba ka gani ba (cħwa) lalle ne Allah, Wanda yake a cikin sammai da ƙasa sunã yi Masa tasbĩhi, kuma tsuntsaye sunã mãsu sanwa, kõwane lalle ya san sallarsa da tasbĩhinsa kuma Allah Masani ne ga abin da suke aikatãwa?
42Mulkin sammai da ƙasa ga Allah kawai yake, kuma zuwa ga Allah makõma take.
43Ashe, ba ka ganĩ ba, lalle ne Allah Yanã kõra girgije, sa´an nan kuma Ya haɗa a tsakãninsa sa´an nan kuma Ya sanya shi mai hauhawar jũna? Sai ka ga ruwa yanã fita daga tsattsakinsa, kuma Ya saukar daga waɗansu duwãtsu a cikinsa na ƙanƙarã daga sama, sai ya sãmu wanda Yake so da shi, kuma Ya karkatar da shi daga barin wanda Yake so. Hasken walƙiyarsa Yanã kusa ya tafi da gannai.
44Allah Yanã jũyar da dare da yini. Lalle ne a cikin wannan akwai abin kula ga ma´abũta gannai.
45Kuma Allah ne Ya halitta kõwace dabba daga ruwa. To, daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan cikinsu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan ƙafãfu biyu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya akan huɗu. Allah Yãna halitta abin da Yake so, lalle Allah, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi ne.
46Lalle ne haƙĩƙa Mun saukar da ãyõyi, mãsu bayyanãwa. Kuma Allah Yanã shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya.
47Kuma sunã cħwa, "Mun yi ĩmãni da Allah da kuma Manzo, kuma mun yi ɗã´ã." Sa´an nan kuma wata ƙungiya daga gare su,su jũya daga bãyan wancan. Kuma waɗancan ba mũminai ba ne.
48Kuma idan aka kirã su zuwa ga Allah da ManzonSa, dõmin Ya yi hukunci(1) a tsakãninsu, sai gã wata ƙnngiya daga gare su sunã mãsu bijirewa.
49Kuma idan hakki ya kasance a gare su, zã su jħ zuwa gare shi, snnã mãsu mĩƙa wuya.
50Shin, a cikin zukãtansu akwai cũta ne, ko kuwa sunã tsõron Allah Ya yi zãlunci a kansu da ManzonSa? ôa, waɗancan sũ ne azzãlumai.
51Maganar mũminai, idan aka kira su zuwa ga Allah da ManzonSa dõmin Ya yi hukunci a tsakãninsu takan kasance kawai su ce "Mun ji, kuma mun yi ɗã´ã, Kuma waɗannan sũ ne mãsu cin nasara."
52Kuma wanda ya yi ɗã´ã ga Allah da ManzonSa, kuma ya ji tsõron Allah, ya kuma bĩ Shi da taƙawa to waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
53Kuma suka rantse da Allah iyãkar rantsuwarsu, ´Lalle ne idan ka umurce su haƙĩƙa sunã fita.´ Ka ce, "Kada ku rantse, ɗã´ã sananna ce! Lalle ne, Allah Mai ƙididdigewã ne ga abin da kuke aikatãwã."
54Ka ce: "Ku yi ɗã´ã ga Allah kuma ku yi ɗã´ã ga Manzo. To, idan kun jũya, to, a kansa akwai abin da aka aza masa kawai, kuma a kanku akwai abin da aka aza muku kawai, Kuma idan kun yi masa ɗã´ã za ku shiryu. Kuma bãbu abin da yake a kan Manzo fãce iyarwa bayyananna."
55Allah Ya yi wa´adi ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare. Ku, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle zai shugabantar da su a cikin ƙasa kamar yadda Ya shugabantar da waɗanda suke daga gabãninsu, kuma lalle ne zai tabbatar musu da addininsu wanda Ya yardar musu, kuma lalle ne Yanã musanya musu daga bãyan tsõronsu da aminci, sunã bauta Mini bã su haɗa kõme da Nĩ. Kuma wanda ya kãfirta a bãyan wannan, to, waɗancan, su ne fãsiƙai.
56Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka, kuma ku yi ɗã´ã ga Manzo, tsammãninku a yi muku rahama.
57Kada lalle ka yi zaton waɗanda suka kãfirta zã su buwãya a cikin ƙasa, kuma makõmarsu wuta ce, kuma lalle ne makomar tã mũnana.
58Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Waɗannan da hannuwanku na dãma suka mallaka da waɗanda ba su isa mafarki ba daga cikinku, su nħmi izni(1) sau uku; daga gabãnin sallar alfijir da lõkacin da kuke ajiye tufãfinku sabõda zãfin rãnã, kuma daga bãyan sallar ishã´i. Sũ ne al´aurõri uku a gare ku. Bãbu laifi a kanku kuma bãbu a kansu a bãyansu. Sũ mãsu kħwaya ne a kanku sãshenku a kan sãshe. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana ãyõyinSa a gare ku. Kuma Allah Masani ne, Mai hikima.
59Kuma idan yãra daga cikinku suka isa mafarki to su nħmi izni, kamar yadda waɗanda suke a gabãninsu suka nħmi iznin. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana ãyõyinSa a gare ku, kuma Allah Masani ne, Mai hikima.
60Kuma tsõfaffi daga mãtã, waɗanda bã su fatan wani aure to, bãbu laifi a kansu su ajiye tufãfinsu, bã sunã mãsu fitar da ƙawa ba, kuma su tsare mutuncinsu shĩ ne mafi alhħri a gare su. Kuma Allah Mai jĩ ne, Masani.
61Bãbu laifi a kan makãho, kuma bãbu laifi a kan gurgu, kuma bãbu laifi a kan majiyyaci, kuma bãbu laifi a kan kõwanenku, ga ku ci (abinci) daga gidãjenku, kõ daga gidãjen ubanninku, kõ daga gidãjen uwãyenku, kõ daga gidãjen ´yan´uwanku mazã, kõ daga gidãjen ´yan´uwanku mãtã, kõ daga gidãjen baffanninku, kõ daga gidãjen gwaggwanninku, kõ daga gidãjen kãwunnanku, kõ daga gidãjen innõninku kõ abin da kuka mallaki mabũɗansa kõ abõkinku bãbu laifi a gare ku ku ci gabã ɗaya, kõ dabam- dabam. To, idan kun shiga wasu gidãje, ku yi sallama a kan kãwunanku,(1) gaisuwã ta daga wurin Allah mai albarka, mai dãɗi. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ãyõyinSa, tsammãninku ku yi hankali.
62Waɗanda ke mũminai sõsai, su ne waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da ManzonSa, kuma idan sun kasance tãre da shi, a kan wani al´amari na aikin gayya, bã su tafiya sai sun nħme shi izni. Lalle ne, waɗanda suke biɗar ka izni waɗancan sũ ne suke yin ĩmãni da Allah da ManzonSa. To, idan sun nħme ka izni sabõda wani sha´aninsu, to, ka yi izni ga wanda ka so daga gare su, kuma ka nħmã musu gãfara daga Allah. Lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai(1) .
63Kada ku sanya kiran Manzo(2) a tsakãninku kamar kiran sãshenku ga sãshe. Lalle ne Allah Yanã sanin waɗanda ke sancħwa daga cikinku da saɗãɗe. To, waɗanda suke sãɓãwa daga umurninSa, su yi saunar wata fitina ta sãme su, kõ kuwa wata azãba mai raɗãɗi ta sãme su.
64To! Lalle Allah ne Yake da mulkin abin da ke a cikin sammai da ƙasa, haƙĩƙa, Yanã sanin abin da kuke a kansa kuma a rãnar da ake mayar da su zuwa gare shi, sai Yanã bã su lãbãri game da abin da suka aikata. Kuma Allah, ga dukkan kõme, Masani ne.
Chapter 25 (Sura 25)
1Albarka ta tabbata ga wanda Ya saukar da (Littãfi) mai rarrabħwa a kan bãwanSa, dõmin ya kasance mai gargaɗi ga halitta.
2wanda Yake da mulkin sammai da ƙasa kuma bai riƙi abin haihuwa ba, kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa kuma Ya halitta dukan kowane abu, sa´an nan Ya ƙaddara shi ƙaddarãwa.
3Kuma suka riƙi abũbuwan bautawa, baicin Shi, bã su yin halittar kõme alhãli sũ ne ake halittãwa kuma bã su mallakar wa kansu wata cũta ko wani amfãni, kuma bã su mallakar mutuwa kuma bã su mallakar rãyarwa, kuma bã su mallakar tãyarwa.
4Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Wannan bã kõme ba ne fãce ƙiron ƙarya da (Muhammadu) ya ƙirƙira shi, kuma waɗansu mutãne na dabam suka taimake shi a kansa." To, lalle ne sun jħ wa zãlunci da karkacħwar magana.
5Kuma suka ce: "Tatsũniyõyi ne na farko ya rurrbũta, sai sũ ake shibtarsu a gare shi sãfe da yamma."
6Ka ce: "wanda Yake sanin asĩri a cikin, sammai da ƙasane Ya saukar da shi. Lalle ne shĩ Ya kasance Mai gãfara, Mai, jin ƙai."
7Kuma suka ce: "Mħne ne ga wannan Manzo, yanã cin abinci, kuma yanã tafiya a cikin kãsuwanni! Don me ba a saukar da malã´ika zuwa gare shi ba, dõmin ya kasance mai gargaɗi tãre da shi?
8"Kõ kuwa a jħfo wata taska zuwa gare shi, kõ kuwa wata gõna ta kasance a gare shi, yanã ci daga gare ta?" Kuma azzãlumai suka ce: "Bã ku bin kõwa, fãce mutum sihirtacce:"
9Ka dũba yadda suka buga maka misãlai sai suka ɓace, dõmin haka bã su iya bin tafarki.
10Albarka ta tabbata ga wanda idan Ya so, Yã sanya maka mafi alhħri daga wannan (abu): gõnaki, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu, kuma Ya sanya maka manyan gidãje.
11ôa, sun ƙaryata game da Sã´a, alhãli kuwa Mun yi tattalin wuta mai tsanani ga wanda ya ƙaryata (manzanni) game da Sa´a.
12Idan ta gan su daga wani wuri mai nĩsa, sai su ji sautin fushi da wani rũri nãta.
13Kuma idan an jħfa su a wani wuri mai ƙunci daga gare ta, sunã waɗanda aka ɗaure ciki daidai, sai su kirãyi halaka a can.
14Kada ku kirãyi halaka guda, kuma ku kirãyi halaka mai yawa.
15Ka ce: "Shin, wancan ne mafi alhħri, kõ kuwa Aljannar dawwama wadda aka yi wa´adi ga mãsu taƙawa? Tã zama, a gare su, sakamako da makõma."
16"Sunã da abin da suke so, a cikinta sunã madawwama. Wannan ya kasance wa´adi abin tambaya a kan Ubangijinka."
17Kuma rãnar da Yake tãra su da abin da suke bauta wa, baicin Allah sai Ya ce: "Shin kũ nekuka ɓatar, da bãyiNa, waɗannan, ko kuwa su ne suka ɓata daga hanya?"
18suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka, bã ya kasancħwa agare mu, mu riƙi waɗansu majiɓinta, baicin Kai, kuma amma Kã jiyar da su dãɗi sũ da ubanninsu har suka manta da Tunãtarwa, kuma sun kasance mutãne ne halakakku."
19To, lalle ne, sun ƙaryata game da abin da kuke cħwa,sabõda haka bã ku iya karkatarwa ga (maganarsu), kuma ba ku iya taimako (ga hana azãba), kuma wanda ya yi zãlunci a cikinku zã Mu ɗanɗana masa azãba mai girma.
20Kuma ba Mu aika ba, a gabãninka daga Manzanni, fãce lalle sũ haƙĩƙa sunã cin abinci kuma sunã tafiya a cikin kasuwõyi. Kuma Mun sanya sãshen mutãne fitina ga sãshe. Shin kunã yin haƙuri? Kuma Ubangijia Ya kasance Mai gani.
21Kuma waɗanda bã su fatan haɗuwa da Mu suka ce: "Don me ba a saukar da malã´ĩku ba a kanmu, kõ kuwa mu ga Ubangijinmu?" Lalle ne sun kangara a cikin rãyukansu, kuma suka yi tsaurin kai, tsaurin kai mai girma.
22A rãnar da suke ganin malã´iku bãbu bushãra a yinin nan ga mãsu laifi kuma sunã cħwa,"Allah Ya kiyãshe(1) mu!"
23Kuma Muka gabãta zuwa ga abin da suka aikata daga aiki, sai Muka sanya shi ƙũra wãtsattsiya.
24Ma´abũta Aljanna a rãnar nan sũ ne mafi alhħri ga matabbata kuma mafi kyaun wurin ƙailũla.
25Kuma a rãnar da sama take tsattsãgewa tãre da gizãgizai, kuma a saukar da malã´iku, saukarwa.
26Mulki a rãnar nan, na gaskiya, yanã ga Mai rahama, kuma ya zama yini, a kan kãfirai, mai tsanani.
27Kuma rãnar da azzãlumi yake cĩzo a kan hannayensa, yanã cħwa "Ya kaitõna! (A ce dai) na riƙi hanya tãre da Manzo!
28"Ya kaitõna! (A ce dai) ban riƙi wãne masõyi ba!
29"Lalle ne, haƙĩƙa ya ɓatar da ni daga Tunãwa a bãyan (Tunãwar) ta je mini."Kuma Shaiɗan ya zama mai zumɓulħwa ga mutum.
30Kuma Manzo ya ce: "Ya Ubangijĩna! Lalle mutãnena sun riƙi wannan Alƙur´ãni abin ƙauracħwa!"
31Kuma kamar haka ne, Muka sanya maƙiyi daga mãsu laifi ga kõwane Annabi. Kuma Ubangijinka Ya isa ga zama Mai Shiryarwa, kuma Mai taimako.
32Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Don me ba a saukar da Alƙur´ãni a kansa ba, jimla guda?" kamar wancan! Dõmin Mu ƙarfafa zũciyarka game da shi, kuma Mun jħranta karanta shi da hankali jħrantawa.
33Kuma bã zã su zo maka da wani misãli ba, fãce Mun je maka da gaskiya da mafi kyau ga fassara.
34Waɗanda ake tãyarwa a kan fuskõkinsu, zuwa ga Jahannama, waɗancan sũ ne mafi sharri ga wuri, kuma mafi ɓacħwa ga hanya.
35Kuma lalle ne, Mun bai wa Mũsã Littãfi, kuma Mun sanya ɗan´uwansa, Hãrũna, mataimaki tãre da shi.
36Sai Muka ce: "Ku tafi, kũ biyu, zuwa ga mutãnen nan waɗanda suka ƙaryata game da ãyõ yinMu." sai Muka darkãke su, darkãkewa.
37Kuma mutãnen Nũhu, a lõkacin da suka ƙaryata Manzanni, Muka nutsar da su, kuma Muka sanya su wata ãya ga mutãne, kuma Muka yi tattalin azãba mai raɗaɗi ga azzãlumai.
38Da Ãdãwa da Samũdãwa, da mutanen Rassi, da waɗansu al´ummomi, a tsakãnin wannan, mãsu yawa.
39Kuma kõwannensu Mun buga masa misãlai, kuma kõwanne Mun halakar da (shi), halakarwa.
40Kuma lalle ne, haƙĩƙa, (Ƙuraishi) sun jħ a kan alƙaryar nan wadda aka yi wa ruwa, ruwan azãba. Shin, ba su kasance sun gan ta ba? ôa, sun kasance bã su ƙaunar tãyarwa (a Ƙiyãma).
41Kuma idan sun gan ka, bã su rikon ka fãce da izgili, (sunã cħwa) "Shin, wannan ne wanda Allah Ya aiko, Manzo?
42"Lalle ne, yã yi kusa ya ɓatar da mu daga Ubangijinmu, in bã dõmin da muka yi haƙuri a kansu ba."Kuma zã su sani a lõkacin da suke ganin azãba, wãne ne mafi ɓacħwa ga hanya!
43Shin, kã ga wanda ya riƙi UbangiJinsa son zuciyarsa? shin, to, kai ne ke kasancħwa mai tsaro a kansa?
44Ko kanã zaton cħwa mafi yawansu sunã ji, kõ kuwa sunã hankali? sũ ba su zama ba fãce dabbõbin gida(1) suke. ôa, sũ ne mafi ɓacħwa ga hanya.
45Ashe, ba ka dũba ba zuwa ga Ubangijinka, yadda Ya miƙe inuwa? Kuma dã Yã so dã Yã bar ta tsaye cif, sa´an nan Muka sanya rãnã mai nũni a kanta.
46Sa´an nan Muka karɓe ta (inuwa) zuwa gare Mu, karɓa mai sauƙi.
47Kuma shĩ ne wanda Ya sanya muku dare ya zama tũfa da barci ya zama hũtãwa, dã yini ya zama lokacin tãshi (kamar Tashin Ƙiyãma).
48Kuma Shi ne Ya aika iskõkin bushãra gaba ga rahamarSa, kuma Muka saukar da ruwa mai tsarkakħwa daga sama.
49Dõmin Mu rãyar, game da shi, gari matacce, kuma Mu shayar da shi dabbõbi da mutãne mãsu yawa daga abin da Muka halitta.
50Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun sarrafa(2) shi (Alƙur´ãni) a tsakãninsu, dõmin su yi tunãni, sai dai mafi yawan mutãnen sun ƙi fãce kãfirci.
51Kuma da Mun so, haƙĩƙa dã Mun aika da mai gargaɗi(3) a ciƙin kõwace alƙarya.
52Sabõda haka kada ka yi ɗã´ã ga kãfirai, ka yãke su, da shi, yãƙi mai girma.
53Kuma shĩ ne Ya garwaya tħkuna biyu, wannan mai dãdi, mai sauƙin haɗiya, kuma wannan gishiri gurɓatacce, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãninsu da kãriya mai shãmakacħwa.
54Kuma Shi ne Ya halitta mutum daga ruwa, sai Ya sanya shi nasaba da surukuta, kuma Ubangijinka Ya kasance Mai ĩkon yi.
55Kuma sunã bauta wa, baicin Allah, abin da bã ya amfãnin su, kuma bã ya cũtar su, kuma kãfiri ya kasance mai taimakon (Shaiɗan) a kan Ubangijinsa
56Ba Mu aika ka ba sai kana mai bãyar da bushãra, kuma mai gargaɗi.
57Ka ce: "Bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa fãce wanda ya so ya riƙi wata hanya(1) zuwa ga Ubangijinsa."
58Kuma ka dõgara a kan Rãyayye wanda bã Ya mutuwa, kuma ka yi tasbĩhi game da gõde Masa. Kuma Yã isa zama Mai ƙididdigewa ga laifuffukan bãyinSa.
59Wanda Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, a cikin kwãnuka shida sa´an nan Yã daidaitu a kan Al´arshi Mai rahama, sai ka tambayi mai bãyar da lãbãri game da(2) Shi.
60Idan aka ce musu, "Ku yi sujada ga Mai rahama." Sai su ce: "Mene ne Mai rahama? Ashe zã mu yi sujada ga abin da kuke umurnin mu?"Kuma wannan (magana(3) ta ƙãra musu gudu.
61Albarka ta tabbata ga Wanda Ya sanya masaukai(4) (na tafiyar wata) a cikin sama kuma Ya sanya fitila da watã mai haskakewa a cikinta.
62Kuma Shĩ ne wanda Ya sanya dare da yini a kan mayħwa,ga wanda yake son ya yi tunãni, kõ kuwa ya yi nufin ya gõde.
63Kuma bãyin Mai rahama(5) su ne waɗanda ke yin tafiya a kan ƙasa da sauƙi, kuma idan jãhilai sun yi musu magana, sai su ce: "Salãma" (a zama lafiya).
64Kuma waɗanda suke kwãna sunã mãsu sujada da tsayi a wurin Ubangijinsu.
65Kuma waɗanda suke cħwa "Ya Ubangijinmu! Ka karkatar da azãbar Jahannama daga gare mu. Lalle ne, azãbarta tã zama tãra(6)
66"Lalle ne ita ta mũnana ta zama wurin tabbata da mazauni."
67Kuma waɗanda suke idan sun ciyar, bã su yin ɓarna, kuma bã su yin ƙwauro, kuma (ciyarwarsu) sai ta kasance a tsakãnin wancan da tsakaitãwa.
68Kuma waɗanda bã su kiran wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da hakki kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka,
69A riɓanya masa azãba a Rãnar Ƙiyãma. Kuma ya tabbata a cikinta yanã wulakantacce.
70Sai wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aiki na ƙwarai to, waɗancan Allah Yanã musanya miyãgun ayyukansu da mãsu kyau. Allah Ya kasance Mai gãfara Mai jin ƙai.
71Kuma wanda ya tũba,(1) kuma ya aikata aiki mai kyau, to, lalle ne sai ya tũba zuwa gaAllah.
72Kuma waɗanda suke bã su yin shaidar zur, kuma idan sun shũɗe ga yasassar magana sai su shũɗe suna mãsu mutumci.
73Kuma waɗanda suke idan an tunãtar da su da ãyõyin Allah,bã su saukar da kai, sunã kurame(2) da makãfi.
74Kuma waɗanda suke cħwa "Yã Ubangijinmu! Ka bã mu sanyin idãnu daga mãtanmu da zũriyarmu, kuma Ka sanya(3) mu shũgabanni ga mãsu taƙawa."
75Waɗannan anã sãka musu da bħne, sabõda haƙurin da suka yi, kuma a haɗa su, a cikinsa, da gaisuwa da aminci.
76Suna madawwama a cikinsa. Ya yi kyau ga zama matabbaci da mazauni.
77Ka ce: "Ubangijĩna ba Ya kula da ku in bã dõmin addu´arku(4) ba. To, lalle ne, kun ƙaryata, sabõda haka al´amarin zã ya zama malizimci."
Chapter 26 (Sura 26)
1Ɗ. S̃. M̃.
2Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
3Tsammãninka kai mai halakar(1) da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
4Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
5Kuma wata tunãtarwa ba ta jħ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirħwa.
6To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
7Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau´i mai kyau?
8Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
9Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
10Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
11"Mutãnen Fir´auna bã zã su yi taƙawa ba?"
12Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
13"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci(2) kuma harshħna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
14"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
15Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
16"Sai ku je wa Fir´auna, sa´an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
17"Ka saki Banĩ Isrã´ila tãre da mu."
18Ya ce: "Shin, ba mu yi rħnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shħkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
19"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
20Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
21"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
22"Kuma waccan ni´ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã´ĩla."
23Fir´auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
24Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
25Ya ce wa waɗanda suke a għfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
26Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
27Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
28Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
29Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
30Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
31Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
32Sai ya jħfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
33Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
34(Fir´auna) ya ce ga mashãwarta a għfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
35"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mħne ne kuke shãwartãwa?"
36Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan´uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
37"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
38Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
39Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
40"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
41To, a lõkacin da masihirta suka jħ suka ce wa Fir´auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
42Ya ce: "Na´am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
43Mũsã ya ce musu, "Ku jħfa abin da kuke mãsu jħfãwa."
44Sai suka jħfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir´auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
45Sai Mũsa ya jħfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
46Sai aka jħfar da masihirta sunã mãsu sujada.
47Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
48"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
49Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa,zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrħ ku gabã ɗaya."
50Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
51"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
52Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cħwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã(1) ne.
53Sai Fir´auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
54"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
55"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
56"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
57Sai Muka fitar da su daga gonaki da marħmari.
58Da taskõki da mazauni mai kyau.
59Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
60Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
61Sa´an nan a lõkacin da jama´a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
62Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
63Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cħwa "Ka dõki tħku da sandarka." Sai tħku ta tsãge,(1) kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
64Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
65Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
66Sa´an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
67Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
68Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
69Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
70A sã´ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mħne ne kuke bauta wa?"
71Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
72Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
73"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
74Suka ce: "ôa mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
75Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
76"Kũ da ubanninku mafi daɗħwa?"
77"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
78"Wanda Ya halitta ni, sa´an nan Yanã shiryar da ni."
79"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
80"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
81"Kuma wanda Yake matar da ni, sa´an nan Ya rãyar da ni."
82"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
83"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
84"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya(1) a cikin mutãnen ƙarshe."
85"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni´ima."
86"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
87"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
88"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
89"Fãce wanda ya jħ wa Allah da zũciya mai tsarki."
90Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
91Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
92Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
93"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
94Sai aka kikkife su(2) a cikinta, su da halakakkun.
95Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
96Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
97"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
98"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
99"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
100"Sabõda haka bã mu da waɗansu macħta."
101"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
102"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
103Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
104Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
105Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
106A lõkacin da ɗan´uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
107"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
108"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
109"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
110"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
111Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
112Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
113"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancħwa."
114"Ban zama mai kõre mũminai ba."
115"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
116Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancħwa daga waɗanda ake jħfewa"
117Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
118"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
119Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
120Sa´an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
121Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
122Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
123Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
124A lõkacin da ɗan´uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
125"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
126"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
127"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
128"Shin, kunã yin ginin sitadiyo(1) a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
129"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"(2)
130"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
131"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
132"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
133"Ya taimake ku da dabbõbin ni´ima da ɗiya."
134"Da gõnaki da marħmari."
135"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
136Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa´azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa´azi ba."
137"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen(1) mutãnen farko."
138"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
139Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ.Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
140Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
141Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
142A lõkacin da ɗan´uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
143"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
144"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã.
145"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
146"Shin, anã barin ku(2) a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
147"A cikin gõnaki da marħmari."
148"Da shuke-shuke da dabĩ nai, ´ya´yan itãcensu hirtsi(3) mãsu narkħwa a ciki?"
149"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
150"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
151"Kada ku yi ɗã´ã ga umurnin maɓarnata."
152"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
153Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
154"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
155Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan(4) yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
156"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
157Sai suka sõke ta sa´an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
158Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
159Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
160Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
161A lõkacin da ɗan´uwansu, (1) Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
162"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
163"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã."
164"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
165"Shin kunã jħ wa maza daga cikin talikai?"
166"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? ôa, ku mutãne ne mãsu ƙħtarħwa!"
167Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancħwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
168Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
169"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
170Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
171Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
172Sa´an nan kuma Muka darkãke wasu.
173Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
174Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
175Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
176Ma´abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
177A lõkacin da Shu´aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
178"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
179"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã´ã."
180"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
181"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
182"Kuma ku yi awo da sikħli daidaitacce."
183"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
184"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama´ar farko."
185Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
186"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
187"To ka jħfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
188Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
189Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije(1) ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
190Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
191Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
192Kuma lalle shi (Alƙur´ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
193Rũhi(2) amintacce ne ya sauka da shi.
194A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
195Da harshe na Larabci mai bayãni.
196Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
197Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã´ĩla sun san shi?
198Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
199Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
200Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
201Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
202Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
203Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
204Ashe, to, da azãbarMu suke nħman gaggãwa?
205Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shħkaru,
206Sa´an nan abin da suka kasance anã yi musu wa´adi (da shi) ya jħ musu,
207Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare(1) su.
208Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
209Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
210Kuma (Alƙur´ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
211Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
212Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
213Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
214Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
215Kuma ka sassauta fikãfikanka(2) ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
216Sa´an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
217Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
218Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
219Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
220Lalle Shi,(3) Shi ne Mai ji,Masani.
221Shin, (kunã so) in gaya(4) muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
222Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
223Sunã jħfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
224Kuma mawãƙa(5) halakakku ne ke bin su.
225Shin, ba ku cħwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙħtare haddi) ba?
226Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
227Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
Chapter 27 (Sura 27)
1Ɗ.S̃. Waɗancan ãyõyinAlƙur´ãni ne da Littãfi mai bayyanawa.
2Shiriya ce da bushãra ga mũminai.
3Waɗanda suke tsayar da salla kuma su bãyar da zakka, alhãli kuwa sũ, game da Lãhira, to, sũ,sunã yin yaƙĩni.
4Lalle ne waɗanda suke bã su yin ĩmãni da Lãhira, Mun ƙawãta musu ayyukansu, sabõda haka sunã ɗimuwa.
5Waɗannan ne waɗanda suke sunã da mugunyar azãba (a dũniya), kuma sũ, a Lãhira, sũ ne mafiya hasãra.
6Kuma lalle ne haƙĩƙa, anã haɗa(1) ka da Alƙur´ãni daga gun Mai hikima, Masani.
7A lõkacin da Mũsã ya ce wa iyãlinsa "Lalle ni, na tsinkãyi wata wuta, ni mai zo muku daga gare ta ne, da wani lãbari, ko kuwa mai zo muku ne da Yũla, makãmashi, tsammãninku, ku ji ɗimi."
8To, a lõkacin da ya jħ mata, sai aka kira shi cħwa, "An tsarkake wanda yake cikin (wurin) wutar da yanda yake a għfenta kuma tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin halittu."
9"Yã Mũsã lalle ne shi, Nĩ ne Allah, Mabuwãyi, Mai hikima."
10"Kuma ka jħfa sandarka." To, a lõkacin da ya gan ta tanã girgiza kamar dai ita ƙaramin macĩji ne, sai ya jũya yanã mai bãyar da bãya, kuma bai kõma ba, "Yã Musã! Kada ka ji tsõro lalle Ni, Manzanni bã sujin tsõro a wuriNa."
11"Sai wanda ya yi zãlunci, sa´an nan ya musanya kyau a bãyan cũta, to, lalle Nĩ, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai."
12"Kuma ka shigar da hannunka a cikin wuyan rĩgarka, ya fita fari, bãbu wata cũta, a cikinwasu ãyõyi tara zuwa ga Fir´auna da mutãnensa. Lalle ne sũ, sun kasance mutãne ne fãsiƙai."
13To, a lõkacin da ãyõyinMu suka jħ musu, sunã mãsu wãyar da kai suka ce wannan sihiri ne bayyananne.
14Kuma suka yi musunsu, alhãli zukãtansu sun natsu da su dõmin zãlunci da girman kai. To, ka dũbi yadda ãƙibar maɓarnata ta kasance.
15Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Dãwũda da Sulaimãn ilmi kuma suka ce: "Gõdiya(1) ta tabbata ga Allah, Wanda Ya fĩfĩta mu a kan mãsu yawa daga bãyinSa mũminai."
16Kuma sulaimãn ya gãji Dãwũda ya ce: "Yã ku mutãne! An sanar da mu maganar tsuntsãye, kuma an bã mu daga kõwane abu. Lalle ne wannan haƙĩƙa shi ne falalar (Allah) bayyananna."
17Kuma aka tattara, dõmin Sulaimãn, rundunõninsa, daga aljannu da mutãne da tsuntsãye, to, sũ anã kange su (ga tafiya).
18Har a lõkacin da suka je a kan rãfin turũruwa wata turũruwa ta ce, "Yã kũ jama´ar turũruwa! Ku shiga gidãjenku, kada Sulaimãn da rundunõninsa su kakkarya ku, alhãli kuwa sũ, ba su sani ba."
19Sai ya yi murmushi yanã mai dãriya daga maganarta, kuma ya ce, "Yã Ubangijĩna! Ka cũsa mini in gõde wa ni´imarKa wadda Ka ni´imta ta a gare ni da kuma ga mahaifãna biyu, kuma in aikata aiki na ƙwarai, wanda Kake yarda da shi, kuma Ka shigar da ni, sabõda rahamarKa, a cikin bãyinKa sãlihai."
20Kuma ya binciki(2) tsuntsãye, sai ya ce: "Me ya kãre ni bã ni ganin hudhudu, kõ ya kasance daga mãsu fakuwa ne?"
21"Lalle ne zã ni azabta shi azãba mai tsanani kõ kuwa lalle in yanka shi, kõ kuwa lalle ya zo mini da dalĩli bayyananne."
22Sai ya zauna bã nħsa ba, sa´an nan ya ce: "Nã san abin da ba ka sani ba, kuma na zo maka daga Saba da wani lãbari tabbatacce."
23"Lalle ni nã sãmi wata mace wadda tanã mulkinsu kuma an bã ta daga dukkan kõme, kuma tanã da gadon sarauta mai girma.
24"Na sãme ta ita da mutãnenta, sunã yin sujada ga rãnã, baicin Allah, kuma Shaiɗan ya ƙawãce musu ayyukansu, sabõda haka ya karkatar da su daga hanya, sa´an nan sũ, ba su shiryuwa."
25"Ga(1) su yi sujada ga Allah Wanda Yake fitar da abin da yake a ɓõye, a cikin sammai da ƙasa, kuma Yã san abin da kuke ɓõyħwada abin da kuke bayyanãwa."
26"Allah bãbu abin bautãwa fãce shĩ Ubangijin(2) Al´arshi, mai girma."
27Ya ce: "Za mu dũba shin kã yi gaskiya ne, kõ kuwa kã kasance daga maƙaryata?"
28"Ka tafi da takardata wannan, sa´an nan ka jħfa ta zuwa gare su, sa´an nan kuma ka jũya daga barinsu, sa´an nan ka ga mħne ne suke mayarwa."
29Ta ce: "Yã kũ mashawarta! Lalle ne, an jħfo, zuwa gareni, wata takarda mai girma."
30"Lalle ita daga Sulaiman take, kuma lalle ita da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai ne."
31"Kada ku yi girman kai a gare ni, kuma ku zo mini kunã mãsu sallamãwa."
32Ta ce: "Yã ku mashawarta(3) ! Ku yi Mini fatawa ga al´amarĩna, ban kasance mai yanke wani al´amari ba, sai kun halarta."
33Suka ce: "Mũ ma´abũta ƙarfi ne, kuma ma´abbũta yãƙi mai tsanani ne, kuma al´amari yã kõma zuwa gare ki, sabõda haka ki dũbamħne ne zã ki yi umurui (da shi)?"
34Ta ce: "Lalle sarakuna idan sun shiga wata alƙarya, sai su ɓãta ta, kuma su sanya mãsu darajar mutãnenta ƙasƙantattu. Kuma kamar wancan ne suke likatãwa."
35"Kuma lalle nĩ mai aikãwa ce zuwa gare su da kyauta, sa´an nan mai dũbawa ce: Da me manzannin zã su kõmo."
36To, a lõkacin da ya jħ wa Sulaiman ya ce: "Shin, za ku ƙãra ni da dũkiya ne? To, abin daAllah Ya bã ni, shi ne mafi alhħridaga abin da Ya bã ku. A´a, kũ nekuke yin farin ciki da kyautarku."
37"Ka kõma zuwa gare su. Sa´an nan lalle munã je musu da rundunõni, bãbu wata tãɓukawa gare su game da su, kuma lalle munã fitar da su daga gare ta, sunã mafi wulãkantuwa, kuma sunã ƙasƙantattu."
38Ya ce: "Yã ku mashãwarta! Wannenku zai zo mini da gadonta a gabãnin su zo, sunã mãsu sallamãwa?"
39Wani mai ƙarfi daga aljannu ya ce: "Nĩ inã zo maka da shi a gabãnin ka tãshi daga matsayinka. Kuma llale nĩ a gare shi, haƙĩƙa, mai ƙarfi ne amintacce."
40Wanda yake a wurinsa akwai(1) wani ilmi daga Littafin ya ce: "Ni inã zo maka da shi a gabãnin ƙyaftãwar ganinka ta kõma gare ka." To, a lõkacin da ya gan shi matabbaci a wurinsa, ya ce: "Wannan daga falalar Ubangijĩna yake, dõmin Ya jarraba ni: Shin, zan gõde ne, kõ kuwa zan butulce! Kuma wanda ya gõde, to, yanã gõdħwa ne dõmin kansa, kuma wanda ya kãfirta, to, lalle Ubangijina Wadãtacce ne, Karĩmi."
41Ya ce: "Ku canza kamar gadonta gare ta, mu gani, shin zã ta shiryu, kõ kuwa tanã kasancħwa daga waɗanda bã su shiryuwa."
42To a lõkacin da ta jħ aka ce "Shin, kamar wannan gadon sarautarki yake?" Ta ce: "Kamar dai shĩne. Kuma an bã mu ilmi daga gabãninta kuma mun kasance mãsu sallamãwar (al´amari ga Allah)."
43Kuma abin da ta kasance tanã bautãwa, baicin Allah, ya kange ta. Lalle ita, tã kasance daga mutãne kãfirai.
44Aka ce mata, "Ki shiga a gidan sarauta." To, a lõkacin da ta gan shi, ta yi zatona wai gurbi ne, kuma ta kuranye(2) daga ƙwaurinta. Ya ce: "Lalle ne shi, gidan sarauta ne mai santsi daga madũbai." Ta ce: "Yã Ubangijĩna! Bã a rõƙon Allah sai da sunãyensa mãsu kyau, tis´in da taran nan, sai dai a dunƙule kamar a ce, "Inã rõƙon Allah da sunãyenSa da na sani da waɗanda ban sani ba." Lalle nĩ, na zãlunci kaina, kuma nã sallama al´amari tãre da Sulaiman ga Allah, Ubangijin halittu."
45Kuma lalle ne, haƙĩƙa, mun aika zuwa Samũdãwa da ɗan´uwansu, Salihu (ya ce), "Ku bauta wa Allah." Sai gã su ƙungiyõyi biyu sunã ta husũma.
46Ya ce: "Yã mutãnħna! Don me kuke nħman gaggãwa game da mũnanãwa, a gabãnin kyautatãwa. Don me bã ku nħman Allah gãfara, tsammãninku, zã a yi muku rahama?"
47Suka ce: "Munã shu´umci da kai, kuma da wanda ke tãre da kai." Ya ce: "Shu´umcinku a wurin Allah yake. ôa, kũ mutãne ne, anã fitinar ku."
48Kuma waɗansu jama´a tara(1) sun kasance a cikin birnin, sunã yin ɓarna, kuma bã su kyautatãwa.
49Suka ce: "Ku yi rantsuwa da Allah, lalle zã mu kwãnan masa,(2) shi da mutãnensa sa´an nan mu ce wa waliyyinsa. ´Ba mu halarci halakar mutãnensa ba kuma mũ, haƙĩ ƙa, mãsu gaskiya ne´."
50Kuma suka ƙulla mãkirci, kuma Muka ƙulla sakamakon mãkirci, alhãli sũ ba su sani ba.
51Ka dũba yadda ãƙibar mãkircinsu ta kasance lalle Mũ Mun darkãke su da mutãnensu, gabã ɗaya.
52Waɗancan, gidãjensu ne, wõfintattu sabõda zãluncin da suka yi, lalle ne a wancan akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke sani.
53Muka tsĩrar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma sun kasance sunã taƙawa.
54Da Lũdu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Shin kunã jħ wa alfasha(3) ne, alhãli, kuwa kunã gani?"
55"Shin lalle kũ haƙĩƙa kunã je wa maza da sha´awa baicin mãtã? ôa, kũ wasu irin mutãne ne kuna aikin jãhilci."
56Bãbu abin da ya kasance jawãbin mutãnensa fãce suka ce "Ku fitar da mutãnen Lũɗu daga alƙaryarku, lalle sũ, wasu irin mutãne ne mãsu da´awar sunã da tsarki."
57Sai Muka tsĩrar da shi, shi da mutãnensa,(1) fãce mãtarsa, Mun ƙaddara ta a cikin mãsu wanzuwa.
58Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa. To, ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
59Ka ce: "Godiya ta tabbata ga A1lah, kuma aminci ya tabbata bisa ga bãyinSa, waɗanda Ya zãɓa." Shin Allah ne Mafi alhħri koabin da suke yin shirki da Shi?(2)
60Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha´awa, ba ya kasancħwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? ôa, sũ mutãne ne suna daidaitãwa (Allah da wani).
61Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta kuma Ya sanya mata manyan duwãtsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãnin tħkuna biyu? Shin akwai wani abin bautãwa tãre da Allah. ôa, mafi yawansu ba su sanĩ ba.
62Kõ wãne ne yake karɓã , kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni.
63Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da tħku,kuma wãne ne Yake aikõwar iskõki dõmin bãyar da bushãra a gaba ga rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi.
64Kõ wãne ne yake fã ra halitta sa´an nan kuma ya mayar da ita,kuma Wãne ne Ya azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka ce: "Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya."
65Ka ce: "Bãbu wanda ya san gaibi a cikin sammai da ƙasa fãce Allah. Kuma bã su sansancħwar a yaushe ne zã a tãyar da su."
66ôa, saninsu ya kai a cikin Lãhira ôa, sunã cikin shakka daga gare ta. ôa, sũ da gare ta makãfin zũci ne.
67Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Shin idan mun kasance turɓaya, mu da ubanninmu, shin, haƙĩƙa, waɗanda ake fitarwa ne?"
68"Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa´adi ga wannan, mũ da ubanninmu, daga gabãnin haka. Wannan bã kõme ba ne fãce tãtsũniyõyin farko."
69Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa´an nan ku dũba, yãya ãƙibar mãsu laifi take?"
70Kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke ƙullãwa na mãkirci.
71Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi (zai auku), idan kun kasance mãsu gaskiya?"
72Ka ce: "Akwai fatan sãshen abin da kuke, nħman gaggãwarsa, ya kasance yã kuturta(1) a gare ku."
73Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa Mai falala ne a kanmutãne kuma amma mafi yawansu, bã su gõdħwa.
74Kuma lalle Ubangijinka, haƙĩƙa Yanã sanin abin da ƙirãzansu suke, ɓõyħwa, da abin da suke hayyanãwa.
75Kuma bãbu wata (mas´ala) mai bõyuwa, a cikin sama da ƙasa fãce tanã a cikin littafi bayyananne.
76Lalle ne wannan Alƙur´ãni(2) yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki.
77Kuma lalle shi haƙĩƙa shiriya ce da rahama ga mũminai.
78"Lalle Ubangijinka Yanã yin hukunci a tsakãninsu da hukuncinsa, kuma Shi ne Mabuwãyi, Masani."
79Sabõda haka, ka dõgara ga Allah, lalle ne, kai ne a kan gaskiya bayyananniya.
80Lalle ne kai, bã ka jiyar da matattu, kuma bã ka sa kurãme su ji kiranka, idan sun jũya sunã mãsu bãyar da bãya.
81Kuma kai ba ka zama mai shiryar da ɗimammu daga ɓata ba. Bã ka jiyarwa fãce wanda yake yin ĩmãni da ãyõyinMu. To, sũ ne mãsu sallamãwa (al´amari zuwa ga Allah).
82Kuma idan magana ta auku a kansu, Munã fitar musu da wata dabba(1) daga ƙasa, tanã yi musu magana, cħwa "Lalle mutãne sun kasance game da ayoyinMu, ba su yin ĩmãnin yaƙĩni."
83Kuma a rãnar da Muke tãrãwa daga kõwace al´umma, wata ƙungiya daga waɗanda suke ƙaryata ãyõyinMu, sai ga su anã kangesu. (ga kõra)
84Har idan sun zo, (Allah) zai ce, "Ashe kun ƙaryata ãyõyinNa, kuma ba ku kħwaye su da sani ba? To, mħne ne kuka kasance kunã aikatãwa?"
85Kuma magana ta auku a kansu, sabõda zãluncin da suka yi. To, sũ bã su da ta cħwa.
86Shin, ba su gani ba, cħwa, lalle Mũ, Mun sanya dare dõmin su natsu a cikinsa, kuma da yini mai sanya gani? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi! Dõmin mutãne waɗanda suka yi ĩmãni.
87Kuma da rãnar(2) da ake hũsa a cikin ƙaho, sai wandayake a cikin sammai da waɗanda suke a cikin ƙasa su firgita, fãce wanda Allah Ya so, kuma dukansu, su je Masa sunã ƙasƙantattu.
88Kuma kanã ganin duwãtsu, kanã zaton su sandararru, alhãli kuwa sũ sunã shũɗħwa shũɗewar girgije, bisa sanã´ar Allah wanda Ya kyautata kõwane abu. Lalle Shi, Mai lãbartãwa ne game da abin da kuke aikatãwa.
89Wanda ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yanã da mafi alhħri daga gare shi. Kuma sũ daga wata firgita,(1) a yinin nan, amintattu ne.
90Kuma wanda ya zo da mugun aiki, to, an kife fuskõkinsu a cikin wuta. Ko zã a sãka muku fãce da abin da kuka kasance kũnã aikatãwa?
91(Ka ce): "An umurce ni, in bauta wa Ubangijin wannan Gari,(2) Wanda Ya mayar da shi Hurumi, kuma Yanã da dukan kõme. Kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu sallamãwa."
92"Kuma inã karanta Alƙur´ãni." To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai. Kuma wanda ya ɓãce, to, ka ce: "Ni daga mãsu gargaɗi kawai nake."
93Kuma ka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah. Zai nũna muku ãyõyinSa, har ku sansu." Kuma Ubangijinka bai zama Mai shagala daga barin abin da kuke aikatãwa ba.
Chapter 28 (Sura 28)
1Ɗ. S̃. M̃.
2Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
3Munã karantãwa a kanka daga lãbarin Mũsã da Fir´auna da gaskiya dõmin mutãne waɗanda suke yin ĩmãni.
4Lalle ne Fir´auna ya ɗaukaka a cikin ƙasa, kuma ya sanya mutãnenta ƙungiya-ƙungiya, yanã raunanar da wata jama´a daga gare su; yanã yanyanka ɗiyansu maza kuma yanã rãyar da mãtan. Lalle shĩ ya kasance daga mãsu ɓarna.
5Kuma Munã nufin Mu yi falala ga waɗanda aka raunanar a cikin ƙasar, kuma Mu sanya su shugabanni, kuma Mu sanya su magãda.
6Kuma Mu tabbatar da su a cikin ƙasar, kuma Mu nũna wa Fir´auna da Hãmãna da rundunõninsu abin da suka kasance sunã sauna daga gare su.
7Kuma Muka yi wahayi zuwa ga uwar Mũsa, cħwa ki shãyar da shi, sai idan kin ji tsõro game da shi, to, ki jħfa shi a cikin kõgi,kuma kada ki ji tsõro, kuma kada ki yi baƙin ciki. Lalle ne Mũ, Mãsu mayar da shi ne zuwa gare ki, kuma Mãsu sanya shi ne a cikin Manzanni
8Sai mutãnen Fir´auna suka tsince shi, dõmin ya kasance maƙiyi da baƙin ciki a gare su. Lalle ne Fir´auna da Hãmãna da rundunõninsu, sun kasance mãsu aikin ganganci.
9Kuma matar(1) Fir´auna ta ce ("Ka bar shi yanã) sanyin ido a gare ni da gare ka! Kada ka kashe shi, akwai fatan ya amfane mu, kõ mu riƙe Shi ɗã," alhãli kuwa sũ ba su sansance ba.
10Kuma zuciyar uwar Mũsã ta wãyi gari yõfintatta.(2) Lalle ne, haƙĩƙa, ta yi kusa ta bayyanar da shi, bã dõmin Mun ɗaure zũciyarta ba, dõmin ta kasance daga mũminai.
11Kuma ta ce wa ´yar´uwarsa,(3) "Ki bĩ shi." Sabõda haka sai ta lħƙe shi daga għfe, alhãli sũ ba Su sani ba.
12Kuma Muka hana masa mãsu shãyai da mãma, a gabãnin haka sai ta ce: "Kõ in nũnamuku mutãnen wani gida, su yi muku renonsa alhãli kuwa su mãsu nasĩha ne a, gare shi?"
13Sai Muka mayar da shi zuwa ga uwarsa dõmin idanunta su yi sanyi, kuma bã zã ta yi baƙin ciki ba, kuma dõmin ta san cħwa lalle wa´adin Allah gaskiya ne, amma kuma mafi yawansu ba su sani ba.
14Kuma a lõkacin da ya kai ƙarfinsa, kuma ya daidaita, Mun bã shi hukunci(1) da ilmi kuma kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
15Kuma sai ya shiga garin a lõkacin da mutãnen garin suka shagala, sai ya sãmu, a cikin garin, waɗansu maza biyu sunã faɗa, wannan daga ƙungiyarsa, kuma ɗayan daga maƙiyansa, sai wannann da yake daga ƙungiyarsa ya nħmi ãgajinsa, sai Mũsã ya yi masa ƙulli, ya kashe shi. Ya ce: "Wannan aikin Shaiɗan ne, dõmin shi maƙiyi ne mai ɓatarwa, bayyananne!"
16Ya ce: "Ya Uhangijĩna! Lalle na zãlunci kaina, sai Ka yi mini gãfara." Sai Ya gãfarta masa, dõmin Shĩ ne Mai yawan gãfara, Mai jin ƙai.
17Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Dõmin abin da Ka ni´imta shi a kaina, sahõda haka bã zan kasance mai taimako ga mãsu laifi ba."
18Sai ya wãyi gari a cikin birnin yanã mai tsõro, yanã sauna. Sai ga wanda ya nħmi taimako daga gare shi a jiya, yanã nħman ãgajinsa. Mũsã ya ce masa, "Lalle kai ɓatacce ne, bayyananne."
19To, a lõkacin da Mũsã ya yi nufin ya damƙi wanda yake maƙiyi ne a gare su, (mai nħman ãgajin) ya ce,(2) "Ya Mũsã! Shin kanãnufin ka kashe ni ne kamar yadda ka kashe wani rai jiya? Ba ka son kõme fãce ka kasance mai tanƙwasawa(3) a cikin ƙasa kuma bã ka nufin ka kasance daga mãsu kyautatãwa."
20Kuma wani mutum ya zo daga mafi nĩsan birnin yanã taliya da gaggãwa, ya ce: "Ya Mũsã! Lalle mashãwarta sunã shãwara game da kai dõmin su kashe ka sabõda haka ka fita. Lalle nĩ, mai nasĩha ne a gare ka."
21Sai ya fita daga gare ta,(4) yanã mai jin tsõro yanã sauna. Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Kã tsħrar da ni daga mutãne azzãlumai."
22Kuma a lõkacin da ya fuskanci wajen Madyana, ya ce: "Inã fatan Ubangijĩna Ya shiryar da ni a kan madaidaiciyar hanya."
23Kuma a lõkacin da ya isa mashãyar Madyana, ya sãmi wata jam´ar mutãne sunã shãyarwa, kuma a bãyansu ya sãmi waɗansu mãtã biyu sunã kõrar (tumãkinsu). Ya ce: "Mħne ne shã´aninku?" Suka ce, "Bã zã mu iya shãyãrwa ba sai makiyãya sun fita, kuma ubanmu tsõho ne(1) mai daraja."
24Sai ya shãyar musu, sa´an nan kuma ya jũya zuwa ga inuwa, sa´an nan ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne, ga abin da Ka saukar zuwa gare ni na alhħri ni mai bukãta ne."
25Sai ɗayansu ta je masa, tanã tafiya a kan jin kunya, ta ce, "Ubãna yanã kiran ka, dõmin ya sãka maka ijãrar abin da ka shãyar sabõda mu." To, a lõkacin da ya je masa,ya gaya masa lãbãrinsa, ya ce: "Kada ka ji tsõro, kã tsĩra daga mutãne azzãlumai."
26Ɗayarsu ta ce, "Yã Bãba! Ka bã shi aikin ijãra, lalle ne mafi alhħrin wanda ka bai wa aikin ijãra shi ne mai ƙarfi(2) amintacce."
27Ya ce: "Lalle ne inã nufin in aurar da kai ɗayan ´yã´yãna biyu, waɗannan, a kan ka yi mini aikin ijãra shħkara takwas to, idan ka cika gõma, to, daga, gare ka yake. Ba ni so in tsanantã maka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga sãlihai."
28Ya ce: "Wannan yanã a tsakanina da tsakãninka kõwane ɗayan adadin biyun na ƙãre, to, bãbu wani zãlunci a kaina. Kuma Allah ne Wakili ga abin da muke faɗa."
29To, a lokacin da Mũsã ya ƙãre adadin kuma yanã tafiya da iyãlinsa, sai ya tsinkãyi wata Wutã daga għfen dũtse (Ɗũr). Ya cewa iyãlinsa, "Ku dãkata, lalle ne nĩ, na tsinkãyi wata wutã, tsammãnĩna ni, mai zo muku ne daga gare ta da wani lãbãrĩ, kõ kuwa da guntun makãmashi daga Wutar don kõ ku ji ɗimi."
30To, a lõkacin da ya jħ wurinta (Wutar) aka kirã shi, daga għfen rãfin na dãma, a cikin wurin nan mai albarka, daga itãciyar (cħwa) "Ya Mũsã! Lalle Nĩ ne Allah Ubangijin halittu."
31"Kuma ka jħfa sandarka." To, a lõkacin da ya gan ta, tanã girgiza kamar ƙaramar macijiya, ya jũya yanã mai bãyar da bãya,bai kõma ba. "Ya Mũsã! Ka fuskanto, kuma kada ka ji tsõro lalle ne kanã daga waɗanda ke amintattu."
32"Ka shigar da hannunka a cikin wuyan rĩgarka, ya fita fari, ba da wata cũta ba, kuma ka haɗa hannuwanka ga kãfaɗunka, dõmin tsõro (ya gushe daga gare ka). To, waɗannan abũbuwa dalĩlai biyu ne daga Ubangijinka zuwa ga Fir´auna da ´yan Majalisarsa. Lalle sun kasance mutãne ne fãsiƙai."
33Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle nã kashe wani rai daga gare su, dõmin haka inã tsõron kada su kashe ni."
34"Kuma ɗan´uwana Hãrũna shĩ ne mafi fasãha daga gareni, ga harshe, sabõda haka Ka aika shi tãre da ni, yanã mai taimako, yanã gaskata ni, lalle ne inã tsõron su ƙaryata ni."
35Ya ce: "Zã Mu ƙarfafa damtsenka game da ɗan´uwanka kuma Mu sanya muku wani dalĩli, sabõda haka bã zã su sãdu zuwa gareku ba, tãre da ãyõyinMu, kũ da waɗanda suka bĩ ku ne marinjãya."
36To, a lõkacin da Mũsã ya jħ musu da ãyõyinMu bayyanannu, suka ce: "Wannan ba kõme ba sai sihiri, wanda aka ƙãga, kuma ba mu ji wannan ba daga wajen ubanninmu na farko."
37Kuma Mũsã ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sanin wanda ya zo da shiriya daga gare Shi, da wanda ãƙibar gida take kasancħwa agare shi. Lalle ne mãsu zãlunci bã su cin nasara."
38Kuma Fir´auna ya ce: "Yã ku mashãwarta! Ban san kunã da wani abin bautãwa baicina ba, sabõda haka ka hũra mini wuta, ya Hãmãnu! a kan lãka(1) (dõmin a yi tũbali), sa´an nan ka sanya mini bħne tsammãnĩna zan ninƙãya zuwa ga Ubangijin Mũsã kuma lalle ne ni, haƙĩƙa, inã zaton sa daga maƙaryata."
39Kuma ya kangare, shi da rundunõninsa a cikin ƙasa, bã da haƙƙi ba kuma suka zaci cħwa sũ, bã zã a mayar da su zuwa gare Mu ba.
40Sai Muka kãma shi, shĩ da rundunõninsa sai Muka jħfa su a cikin kõgi. Sai ka dũbi yaddaãƙibar azzãlumai ta kasance.
41Kuma Muka sanya su shũgabanni, sunã kira zuwa ga wuta,kuma a Rãnar Ƙiyãma bã zã a taimake su ba.
42Kuma Muka biyar musu da la´ana a cikin wannan dũniyakuma a Rãnar Ƙiyãma sunã daga waɗanda aka mũnana halittarsu.
43Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã Littãfi daga bãyan Mun halakar da ƙarnõnin farko, dõmin su zama abũbuwan kula ga mutãne, da shiriya da rahama, tsammãninsu sunã tunãwa.
44Kuma ba ka kasance ba ga għfen rãfi na yamma a lõkacin da Muka hukunta al´amaru zuwa ga Mũsã, kuma ba ka kasance daga halartattu ba.
45Kuma amma Mũ, Mun ƙãga halittawar wasu ƙarnõni har lõkatan rãyuwa suka yi tsawo a kansu. Kuma ba ka kasance mazauni ba a cikin mutãnen Madyana, kanã karanta musu ãyõyinMu, amma Mũ Mun kasãnce mãsu aikãwa (da kai game(1) da waɗancan lãbarai).
46Kuma ba ka kasance ga għfen dũtse ba a lõkacin da Muka yi kira, kuma amma dõmin rahama daga Ubangijinka, dõmin ka yi gargaɗi ga mutãne waɗanda suke wani mai gargaɗi a gabãninka bai je musu ba, tsammãninsu sunã tunãwa.
47Kuma bã dõmin wata masĩfa ta sãme su ba sabõda abin da hannayensu suka gabãtar, su ce: "Yã Ubangijinmu! Don me ba Ka aiko wani Manzo zuwa gare mu ba, har mu dinga bĩn ãyõyinKa,kuma mu kasance daga mũminai?"
48Sa´an nan a lõkacin da gaskiya ta jħ musu daga wurinMu, suka ce: "Don me ba a bã shi kamar abin da aka bai wa Mũsã ba?" Shin kuma ba su kãfirta ba da abin da aka bai wa Mũsã a gabãnin (wannan)? suka ce: "Sihirõri biyu ne suka taimaki jũna," kuma suka ce: "Lalle ne mũ, mãsu kãfirta ne ga dukansu?"
49Ka ce: "To ku zo da wani littãfi daga, wurin Allah, wanda yake shi ne mafi shiryarwa daga gare su, in bĩ shi, idan kunkasance mãsu gaskiya."
50To, idan ba su karɓa maka ba to sai ka sani sunã bin son zuciyarsu ne kawai, kuma wãne ne mafi ɓata daga wanda ya bi son zuciyarsa, bã tãre da wata shiriya daga Allah ba? Lalle ne, Allah bã ya shiryar da mutãne azzãlumai.
51Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun sãdar(1) da magana sabõda su, tsammãninsu, suna tunãni.
52Waɗanda Muka bã su littãfi daga gabãninsa (Alƙur´ãni), su mãsu ĩmãni ne da shi.(2)
53Kuma idan anã karanta shi a kansu, sai su ce: "Mun yi ĩmãni da shi, lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinmu. Lalle mũ, mun kasance a gabãninsa masu sallamãwa."
54Waɗancan anã ba su lãdarsu sau biyu, sabõda haƙurin da suka yi, kuma da kyautatãwa suna tunkuɗewar mũnanãwa kuma daga abin da Muka azũrtã susunã ciyarwa.
55Kuma idan sun ji yãsassar magana sukan kau da kai daga barinta, kuma sukan ce, "Ayyukanmu sunã a gare mu, kuma ayyukanku sunã a gare ku, aminci ya tabbata a kanmu bã mu nħman jãhilai (da husũma)."(3)
56Lalle ne kai bã ka shiryar(4) da wanda ka so, amma kuma Allah Yanã shiryar da wanda Yake so, kuma Shi ne Mafi sani daga mãsu shiryuwa.
57Kuma suka ce: "Idan mun bi shiriya tãre da kai anã fizge mu(5) daga ƙasamiu." Shin, ba Mu tabbatar musu da mallakar Hurumi ba, ya zama amintacce, anã jãwõwa zuwa gare shi, ´ya´yan itãcen kõwane iri, bisa ga azurtãwa daga gare Mu? Amma kuma mafi yawansu ba su sani ba.
58Kuma da yawa Muka halakar da wata alƙarya wadda ta yi butulci ga rãyuwarta. To, waɗancan gidãjensu ne, ba a zaune su ba, a bãyansu, fãce kaɗan. Kuma mun kasance Mũ ne Magãda.
59Kuma Ubangijinka bai kasance Mai halaka alƙaryu ba, sai Ya aika a cikin hedkwatarsu da wani Manzo yanã karanta ãyõyinMu a kansu. Kuma ba Mu kasance Mãsu halaka alƙaryu ba, fãce mutanensu sun kasance mãsu zãlunci.
60Kuma abin da aka bã su daga kõme, to, jin dãɗin rayuwar dũniya ne da ƙawarta. Kuma abin da ke wurin Allah, shĩ ne mafi alhħri, knma mafi wanzuwa. Shin bã ku hankalta?
61Shin fa, wanda Muka yi wa wa´adi, wa´adi mai kyau, sa´an nan shĩ mai haɗuwa da shi ne, yanã zama kamar wanda Muka jiyar da shi ɗan dãɗi, dãɗin rãyuwar dũniya, sa´an nan shi a Rãnar Ƙiyãma yanã daga mãsu shiga wuta?
62Kuma rãnar da (Allah) Yake kiran su sa´an nan Ya ce: "Inã abõkan tãrayyaTa, waɗanda kuka kasance kunã riyãwa?"
63Waɗanda magana ta wajaba a kansu, su ce: "Yã Ubangijinmu! Waɗannan sũ ne waɗanda muka halakar mun halakar da su kamar yadda muka halaka. Mun barranta zuwa gare Ka, ba su kasance mũ suke bautã wa ba."
64Kuma a ce ku kirãwo abõkan tãrayyar ɗinku, sai su kira su, sai ba su amsa ba, kuma su ga azãbar. Dã dai lalle su sun kasance snnã shiryuwa(1) !
65Kuma rãnar da Yake kiran su, sa´an nan Ya ce: "Mħne nekuka karɓa wa Mananni?"
66Sai lãbãru su ɓace musu a rãnar nan sa´an nan bã zã su tambayi jũnaosu ba.
67To, amma wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni´ ya aikata aiki na ƙwarai, to, akwai fãtan su kasance daga mãsu cin nasara.
68Kuma Ubangijinka Yanã halitta abin da Yake so kuma Yake zãɓi. Zãɓi bai kasance a gare su ba.Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma (Allah) Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka.
69Kuma Ubangijinka Yanã sanin abin da zukãtansu ke ɓõyħwa, da abin da suke bayyanãwa.
70Kuma Shĩ ne Allah, bãbu abin bautãwa fãce Shi. Kuma Shi ne abin gõdiya a cikin ta farko (dũniya), da ta ƙarshe (Lãhira). Kuma Shi ne da hukunci, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku.
71Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya sanya dare tutur a kanku har zuwa Rãnar Ƙiyãma, wane abin bautãwa wanin Allah zai zo muku da haske? Shin, bã ku ji?"
72Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya sanya yini a kanku tutur zuwa Rãnar Ƙiyãma, wane abin bautãwa, wanin Allah, zai zo muku da dare wanda kunã natsuwa a cikinsa? Shin fa, bã ku gani?"
73"Kuma daga rahamarSa Ya sanya muku dare da yini dõmin ku natsu a cikinsa, kuma dõmin ku nħma daga falalarSa, kuma tsammãninku zã ku gõde."
74Kuma a rãnar da Yake kiran su ya ce: "Inã abõkan tarayya Ta, waɗanda kuka kasance kunã riyãwa"(1)
75Kuma Muka zãre mai shaida daga kõwace al´umma, sa´an nan Muka ce: "Ku kãwo dalilinku." Sai suka san cħwa lalle gaskiya ga Allah take. Kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa na ƙarya ya ɓace daga barinsu.
76Lalle ne Ƙãrũna ya kasance daga mutãnen Mũsã, sai ya fita(2) daga tsãrinsu alhãli Mun bã shi taskõkin abin da yake mabũɗansa sunã nauyi ga jama´a(3) ma´abũta ƙarfi a lõkacin da mutãnensa suka ce masa, "Kada ka yi annashuwa, lalle ne Allah bã Ya son mãsu annashuwa."
77"Kuma ka biɗã a cikin abin da Allah Ya bã ka, gidan Lãhira, kuma kada ka manta da rabonka daga dũniya. Kuma ka kyautata, kamar yadda Allah Ya kyautata zuwa gare ka, kuma kada ka nħmi ɓarna a cikin ƙasa,(4) lalle ne Allah bã Ya son mãsu barna."
78Ya ce: "An bã ni shi a kan wani ilmi wanda yake gare ni ne kawai." Shin, kuma bai sani ba cħwa lalle Allah haƙiƙa Ya halakar a gabaninsa, daga ƙarnõni, wanda yake Shi ne mafi tsananin ƙarfi daga gare shi, kuma mafi yawan tãrawar dũkiya, kuma bã zã a tambayi mãsu laifi daga zunubansu ba?(1)
79Sai (Ƙãrũna) ya fita a kan mutãnensa a cikin adonsa. Waɗanda suke nufin rãyuwar dũniya suka ce: "Inã dai munã da kwatancin abin da aka bai wa Ƙãrũna! Lalle shĩ haƙĩƙa ma´abũcin rabo babba ne."
80Kuma waɗanda aka bai wa ilmi suka ce: "Kaitonku! sakamakon Allah ne mafi alhħri a wanda ya yi tunãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai,(2) kuma bãbu wanda ake haɗãwa da ita fãce mai ha ƙuri."
81Sai Muka shãfe ƙasa(3) da shi da kuma gidansa. To, waɗansu jama´a ba su kasance gare shi ba, waɗanda suke taimakon sa, baicin Allah, kuma shi bai kasance daga mãsu taimakon kansu ba.
82Kuma waɗanda suka yi bũrin matsayinsa a jiya suka wãyi gari sunã cħwa, "Wai! Allah Yanã shimfiɗa arziki, ga wanda Yake so daga bãyinsa, kuma Yanã ƙuntatãwa. Bã dõmin Allah Ya yi mana falala ba dã Yã shãfe ƙasa da mu. Wai! lalle ne shi, kãfirai bã su cin nasara."
83Wancan gidan Lãhira Munã sanya shi ga waɗanda suke bã su nufin ɗaukaka a cikin rãyuwar dũniya kuma bã su son ɓarna. Kuma ãkiba ga mãsu taƙawa take.
84Wanda ya zo da abu mai kyau, to, yana da mafi alhħri daga gare shi, kuma wanda ya zo da mũgun abu, to, bã zã a sãkawa waɗanda suka aikata miyãgun ayyuka ba, fãce da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
85Lalle ne wanda Ya faralta Alƙur´ãni a kanka, haƙĩƙa, Mai Mayar da kai ne zuwa ga makõma. ka ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga wanda ya zo da shiriya, da kuma wanda yake a cikin ɓata bayyananna."
86Kuma ba ka kasance kanã fãtan a jħfa Littafin nan zuwa gare ka ba, fãce dai dõmin rahama daga Ubangijinka. Sabõda haka kada ka zama mai taimako(1) ga kãfirai.
87Kuma kada lalle su karkatar da kai daga barin ãyõyin Allah, a bãyãn har an saukar da su uwa gare ka. Ka yi kira zuwa ga Ubangijinka, kuma kada lalle ka kasance daga mãsu shirka.
88Kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. Kõwane abu mai halaka ne fãce fuskarSa. Shi ne da hukunci kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku.(2)
Chapter 29 (Sura 29)
1A. L̃. M̃.
2Ashe, mutãne sun yi zaton a bar su su ce: "Mun yi ĩmãni," alhãli kuwa bã zã a fitine su ba?"
3Kuma lalle Mun fitini waɗanda ke a gabãninsu, dõmin lalle Allah Ya san waɗanda suka yi gaskiya, kuma lalle Ya san maƙaryata.
4Kõ waɗanda ke aikata miyãgun ayyuka sun yi zaton su tsħre Mana? Abin da suke hukuntãwa ya mũnana.
5Wanda ya kasance yanã fãtan gamuwa da Al1ah to lalle ajalin Allah mai zuwa ne, kuma (Allah) Shĩ ne Mai ji, Masani.
6Kuma wanda ya yi jihãdi, to, yanã yin jihãdin ne dõmin kansa. lalle Allah haƙĩƙa waɗatacce ne daga barin tãlikai.
7Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle Munã kankare musu miyãgun ayyukansu, kuma lalle Munã sãka musu da mafi kyaun abin da suka kasance sunã aikatãwa.
8Kuma Mun yi wa mutum wasiyyar kyautatãwa ga uwayensa, kuma idan sun tsananta maka dõmin ka yi shirki da Ni game da abin da bã ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗã´ã. Zuwa gare Ni makõmarku take sa´an nan In bã ku lãbari ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
9Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle Munã shigar da su a cikin mutãnen kirki.
10Kuma daga cikin mutãne akwai mai cħwa, ´Mun yi ĩmãni da Allah" sa´an nan idan aka cũce shi wajen aikin Allah, sai ya sanya fitinar mutãne kamar azãbar Allah kuma lalle idan taimakon Ubangijinka ya zo, haƙĩƙa, ya kan ce: "Lalle mũ mun kasance tãre da ku." shin, Allah bai zama Mafi sani ba ga abin da ke a cikin ƙirãzan halittunSa?
11Kuma lalle Allah na sanin waɗanda suka yi ĩmãni kuma lalle Yanã sanin munfukai.
12Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce wa waɗanda suka yi ĩmãni, "Ku bi hanyarmu, kuma Mu ɗauki laifuffukanku," alhãli kõwa ba su zamo mãsu ɗauka da a kõme ba daga laifuffukansu. Lalle sũ maƙaryata ne.
13Kuma lalle sunã ɗaukar kãyan nauyinsu da waɗansu nauyãyan kãya tãre da kãyan nauyinsu, kuma lalle zã a tambaye su a Rãnar Ƙiyama game da abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa na ƙarya.
14Kuma lalle Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnensa, sai ya zauna a cikinsu shħkara dubu fãce shħkara hamsin, sa´an nan cikowar (Ɗũfãna) ta kãmã su, alhãli kuwa sũ ne mãsu zãlunci.
15Sa´an nan Muka tsĩrar da shi da mutãnen jirgin, kuma Muka sanya jirgin ya zama wata ãyã ga tãlikai.
16Da Ibrãhĩm a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Ku bautã wa Allah ku bĩ Shi da taƙawa. Wannan Shĩ ne alhħri a gare ku idan kun kasance kunã sani.
17"Abin da dai kuke bautãwa, baiein Allah, gumaka ne, kuma kun ƙirƙira ƙarya. Lalle waɗannan da kuke bauta wa baicin Allah, bã su mallakã muku arziki. Sabõda haka ku nħmi arziki a wurin Allah kawai, kuma ku bauta Masa, kuma ku yi gõdiya zuwa gare Shi. Zuwa gare Shi ake mayar da ku.
18"Kuma idan kun ƙaryata, to, lalle waɗansu al´ummõmi a gabãninku sun ƙaryata, kuma bãbu abin da ke kan Manzo, fãce iyar da manzanci, iyarwa bayyananna."
19Shin, ba su(1) ga yadda Allah ke fãra yin halitta ba, sa´an nan kuma Ya mayar da ita? Lalle wannan abu ne mai sauƙi ga Allah.
20Ka ce: "Ku yi tafiya cikin ƙasa, sa´an nan ku dũba yadda (Allah) Ya fãra yin halitta, sa´an nan kuma Allah Yanã ƙãga wata halittar mayarwa. Lalle Allah Mai ikon yi ne a kan kõme.
21"Yanã azabta wanda Ya so, kuma Yanã jin ƙan wanda Ya so. Kuma zuwa gare shi ake jũyaku."
22"Kuma ba ku zamo mãsu buwãya ba a cikin ƙasã, kuma haka a cikin sama kuma bã ku da wani majiɓinci wanda ba Allah ba, kuma ha ku da wani mataimaki."
23Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah da gamuwa da shi, waɗannan sun yanke ƙauna daga rahamaTa kuma waɗannan sunã da wata azãba mai raɗaɗi.
24Sa´an nan bãbu abin da ya kasance jawãbin mutãnensa (Ibrãhĩm) fãce dai suka ce: "Ku kashe shi kõ, ku ƙõnã shi," Sai Allah Ya tsĩrar da shi daga wutã. Lallea cikin wannan akwai ayõyi ga mutãnen da ke yin ĩmãni.
25Kuma Ibrahĩm ya ce "Bãbu abin da kuka yi sai dai kub bar Allah kun riƙi gumãka sabõda sõyayyar tsakãninku a cikin rãyuwar dũniya, a´an nan a Rãnar Ƙiyãma sãshinku zai kãfirce wa sãshi, kuma makõmarku ita ce wutã kuma bã ku da waɗansu mataimaka."
26Sai Lũɗu ya yi ĩmãni da shi. Kuma Ibrãhĩm ya ce: "Lallenĩ mai ƙaura ne zuwa ga Ubangijina. Lalle Shĩ Shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima."
27Kuma Muka bã shi Ishãƙa da Ya´aƙũba, kuma Muka sanya Annabci da littãfi a cikin zuriyarsa. Kuma Mun bã shi sakamakonsa a dũniya, kuma lalle shĩ a Lãhira, tabbas, yanã a cikin sãlihai.
28Da Lũɗu, a lõkacin daya ce wa mutãnensa, "Lalle kũ, haƙĩƙa kunã jħ wa alfãsha wadda wani mahalũƙi daga cikin dũniya bai riga ku gare ta ba.
29"Ashe, lalle kũ kunã je wa maza, kuma ku yi fashin hanya kuma ku je, a cikin majalisarku da abin da bã shi da kyau? To, jawãbin mutãnensa bai kasance ba fãce dai sun ce: ´Ka zo mana da azãbar Allah, idan ka kasance daga mãsu gaskiya.´"
30Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimake ni a kan mutãnen nan maɓarnata."
31Kuma a lõkacin da ManzanninMu suka jħ wa Ibrãhĩm da bushãra suka ce: "Lalle mu mãsu halaka mutãnen, wannan alƙarya ne. Lalle mutãnenta sun kasance mãsu zãlunci."
32Ya ce: "Lalle akwai Lũɗu a cikinta!" Suka ce: "Mũ ne mafiya sani ga waɗanda suke a cikinta, lalle munã tsĩrar da shi da mutãnensa, fãce fa mãtarsa ta kasance a cikin mãsu wanzuwa."
33Kuma a lõkacin da ManzanninMu suka je wa Lũɗu ya ɓãta rai sabõda su, kuma yã ƙuntata ga kirji sabõda su. Kuma suka ce: "Kada ka ji tsõro kuma kada ka yi baƙin ciki lalle mũ mãsu tsĩrar da kai ne da iyãlanka, fãce dai matarka ta kasance daga mãsu wanzuwa.
34"Lalle mũ, mãsu saukar da azãba ne daga sama a kan mutãnen wannan alƙarya sabõda abin da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci."
35Kuma lalle Mun bar wata ãyã bayyananna daga gare ta ga mutãne mãsu hankalta.
36Kuma zuwa ga Madyana, Mun aika ɗan´uwansu shu´aibu, sai ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah kuma ku yi fatan (rahamar) Rãnar Lãhira, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasã, alhãli kuwa kunã mãsu lãlãtarwa."
37Sai suka ƙaryata shi, sabõda haka tsãwa ta kãmã su, dõmin haka suka wãyi gari sunã guggurfãne.
38Da Ãdawa da Samũdãwa alhãli kuwa lalle alãmun azãba sun bayyana a gare su daga gidãjensu kuma Shaiɗan ya ƙawãta musu ayyukansu, sabõda haka ya kange su daga hanyar Allah, kuma sun kasance mãsu basĩra!
39Kuma Ƙãrũna da Fir´auna da Hãmãna, kuma lalle Mũsaya je musu da hujjõji, sai suka yi girman kai a cikin ƙasã kuma ba su kasance mãsu tsħrħwa ba.
40Sabõda haka kõwanensu Mun kama shi da laifinsa. Watau daga cikinsu akwai wanda Muka aika iskar tsakuwa a kansa kuma daga cikinsu akwai wanda tsãwa ta kãmã, kuma daga cikinsu akwai wanda Muka birkice ƙasã da shi kuma daga cikinsu akwai wanda Muka nutsar. Bã ya yiwuwa ga Allah Ya zãlunce su, amma sun kasance kansu suke zãlunta.
41Misãlin waɗanda suka riƙi waɗansu masõya waɗanda bã Allah ba, kamar misãlin gizõgizo ne wanda ya riƙi wani ɗan gida, alhãli kuwa lalle mafi raunin gidãje, shĩ ne gidan gizogizo, dã sun kasance sunã sane.
42Lalle Allah Yanã sane da abin da suke kira wanda bã Shi ba na wani abu duka kuma shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima.
43Kuma waɗancan misãlan Munã bayyana su ga mutãne kuma bãbu mai hankalta da su sai mãsu ilmi.
44Allah Ya halitta sammai da ƙasa da gaskiya. Lalle cikin wancan akwai ãyã ga mũminai.
45Ka karanta abin da ake yin wahayi zuwa gare ka daga Littãfi, kuma ka tsayar da salla. Lalle salla tanã hanãwa daga alfãsha da abni ƙyãma, kuma lalle ambaton Allah ya fi girma, kuma Allah Yanã sane da abin da kuke aikatãwa.
46Kada ku yi jayayya da mazowa Littãfi sai fa da magana wadda ta fi kyau, sai fa waɗanda suka yi zãlunci daga gare su, kuma ku ce, "Mun yi ĩmãni da abin da aka saukar a gare mu kuma aka saukar a gare ku, kuma Abin bautãwarmu da Abin bautãwarku Guda ne, kama mũ mãsu sallamãwa ne a gare shi."
47Kuma kamar haka Muka saukar da Littafi a gare ka, to, waɗannan da Muka bai wa Littãfi sanã ĩmãni da shi, daga cikin wãɗannan akwai mai ĩmãni da shi, kuma bãbu mai musun ãyõyinMu, fãce kãfirai.
48Kuma ba ka kasance kana karãtun wani littãfi ba a gabãninsa, kuma bã ka rubũtunsa da dãmanka dã haka yã auku, dã mãsu ɓarnã sun yi shakka.
49ôa, shĩ ãyõyi ne bayyanannu a cikin ƙirãzan waɗanda aka bai wa ilmi. Kuma bãbu mai musun ãyõyinMu fãce azzãlumai.
50Kuma suka ce: "Don me ba a saukar masa da ãyõi ba daga Ubangijinsa? "Ka ce: "Su ãyõyi a wurin Allah kawai suke, kuma lalle ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyanãwa."
51Shin bai ishe su ba cħwa lalle Mũ, Mun saukar da Littãfin akanka, anã karanta shi a kansu? Lalle a cikin wancan haƙĩƙa akwai rahama da tunãtawa ga mutanen da ke yin ĩmãni.
52Ka ce: "Allah Yã isa shaida a tsakãnĩna da tsakãnĩnku Yanã sane da abin da ke a cikin sammai da ƙasã, kuma waɗanda suka yi ĩmãni da ɗarya kuma suka kãfirta da Allah, waɗannan sũ nemãsu hasãra."
53Kuma suna nħman ka da gaggauta azãba, to, bã dõmin ajali ƙayyadadde ba, dã azãba ta jħ musu kuma lalle dã tanã iske su bisa ia abke, alhãli kuwa sũ ba su sani ba.
54Sunã nħman ka da gaggauta azãba, kuma lalle Jahannama, tabbas, mai kħwayewa ce gakãfirai.
55Rãnar da azãba ke rufe su daga samansu da kuma ƙasan ƙafafunsu kuma Ya(1) ce: "Ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
56Yã bãyiNa, waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle fa ƙasãTa mai yalwã(2) ce, sabãda haka ku bauta Mini.
57Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne, sa´an nan zuwa gare Mu ake mayar da ku.
58Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle zã Mu zaunar da su daga cikin Aljanna a gidãjen bħne, ƙoramu nã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu. To, madalla da sakamakon mãsu aikin ƙwarai.
59Waɗanda suka yi haƙuri, kuma sunã dõgara ga Ubangijinsu kawai.
60Kuma da yawa(3) dabba wadda bã ta ɗaukar abincinta Allah Yanã ciyar da ita tãre da ku, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai ilmi.
61Lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halitta sammai da ƙasã kuma ya hõre rãnã da watã?" Lalle sunã cħwa Allah ne. TO, yãya ake karkatar da su(4) ?
62A1lah ne ke shimfiɗa arziki ga wanda Yake so daga cikin bãyinsa kuma Yanã ƙuntãtãwa ga (wanda, Yake so). Lalle Allah, Masani ne ga dukan kõme.
63Kuma lalle idan ka tambaye su. "Wãne ne ya saukar da ruwa daga sama, har ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta?" Lalle sunã cħwa, "Allah ne." Ka ce: "Gõdiya tã tabbata ga Allah." ôa, mafi yawansu bã su hankalta.
64Kuma wannan rãyuwa ta dũniya ba ta zamo ba, fãce abar shagala da wãsã kuma lalle Lãhira tabbas, ita ce rãyuwa, dã sun kasance sunã sani.
65To, a lõkacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirãyi Allah sunã mãsu tsarkake addini a gare shi, to, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudun ƙasã, sai gã su sunã shirki.
66Dõmin su kãfirce wa abin da Muka bã su kuma dõmin su ji dãɗi sa´an nan kuma zã su sani.
67Shin, ba su ga cħwa, lalle Mun sanya Hurumi amintacce ba alhãli kuwa anã fisge mutãne a għfensu? Shin, da ɓãtaccen abu suke ĩmãni kuma da ni´imarAllah suka kãfirta?
68Kuma wãne ne ya fi zãlunci bisa ga wanda ya ƙirƙira ƙarya ya jingina ta ga Allah, kõ kuma ya ƙaryata gaskiya a lõkacin da ta je masa? Ashe a cikin Jahannama bãbu mazauna ga kãfirai?
69Kuma wadannan da suka yi ƙõƙari ga nħman yardarMu, lalle Munã shiryar da su ga hanyõyinMu, kuma lalle Allah, tabbas, Yanã tãre da mãsu kyautatãwa (ga addĩninsu).
Chapter 30 (Sura 30)
1A. L̃. M̃.
2An rinjãyi Rũmawa.(1)
3A cikin mafi kusantar ƙasarsu, kuma sũ, a bãyan rinjãyarsu, zã sn rinjãya.
4A cikin´yan shħkaru. Al´amari na Allah ne a gabãnin kõme da bãyansa, kuma a rãnar nan mũminai zã su yi farin ciki.
5Da taimakon Allah Yanã taimakon wanda Yake so. Kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
6Wa´adin Allah, Allah bã ya sãɓãwa ga wa´adinsa, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
7Sunã sanin bayyanannar rãyuwar dũniya, alhãli kuwa sũ shagalallu ne daga rãyuwar Lãhira.(1)
8Shin, ba su yi tunãni ba a cikin zukãtansu cħwa Allah bai halitta sammai da ƙasa ba da abin da ke tsakãninsu, fãce da gaskiya(2) da ajali ambatacce? Kuma lalle mãsu yawa daga mutãne kãfirai ne ga gamuwa da Ubangijinsu?
9Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã dõmin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabãninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nõmi ƙasa suka rãya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zãlunce su, amma kansu suka kasance sunã zãlunta.
10Sa´an nan ãƙibar waɗannan da suka aikata mũgun aiki ta kasance mafi muni, wãtau sun ƙaryata game da ãyõyin Allah, kuma suka kasance sunã izgili da su.
11Allah ne ke fãra yin halitta, sa´an nan Ya sãke ta sa´an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku.
12Kuma a rãnar da sa´a ke tsayuwa, mãsu laifi zã su kãsa magana.
13Kuma bã su da mãsu cħto daga abũbuwan shirkinsu, kuma snn kasance mãsu kãfircħwadaga abũbuwan shirkinsu.
14Kuma a rãnar da Sa´a ke tsayuwa, a rãnar nan mutãne ke farraba.
15To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai to sũ anã faranta musu rãyuka, a cikin wani lambu.
16Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryata, game da ãyõyinMu da kuma haɗuwa da Rãnar Lãhira, to, waɗancan anã halartar da su a cikin azãba.
17Sabõda haka tsarkakħwa ta tabbata ga Allah a lõkacin da kuke shiga maraice, da lõkacin da kuke shiga sãfiya.(1)
18Kuma Shĩ ne da gõdiya, a cikin sammai da ƙasã kuma da lõkacin yamma da lõkacin zawãli.
19Yanã fitar da mai rai daga matacce kuma Yanã fitar da matacce daga mai rai, kuma Yanã rãyar da ƙasa a bãyan mutuwarta. Kuma haka ake fitar da ku.
20Kuma akwai daga ãyõyinSa, Ya halitta ku daga turɓãya, sai gã ku kun zama mutum, kunã wãtsuwa.
21Kuma akwai daga ãyõyinsa, Ya halitta muku mãtan aure daga kanku, dõmin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya sõyayya da rahama a tsakãninku.(2) Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu yin tunãni.
22Kuma akwai daga ãyõyinSa halittar sammai da ƙasã da sãɓã, war harsunanku, da launukanku. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mãsu ilmi.
23Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, barcinku a cikin dare da rãna, da nħmanku ga falalarsa. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu saurãrãwa.
24Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, Ya nũna muku walƙiya a kan tsõro da ɗammãni kuma Ya dinga saukar da ruwa daga sama Sa´an nan Ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu hankaltawa.
25Kuma akwai daga ãyõyinsa, tsayuwar sama da asƙã bisa umurninsa, sa´an nan idan Ya kira ku, kira ɗaya, daga ƙasã, sai gã ku kunã fita.
26Kuma wanda ke cikin sammai da ƙasã Nãsa ne shi kaɗai. Dukansu mãsu tawãli´u ne a gare Shi.
27Kuma Shĩ ne Wanda Ya fãra halitta, sa´an nan Ya sãke ta kuma sakħwarta tã fi sauƙi a gare shi. Kuma Yanã da misãli wanda ya fi ɗaukaka a cikin sammai da ƙasã kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
28Ya bũga muku wani misãli daga kanku. Kõ kunã da abõkan tarħwa, daga cikin bãyin da hannãyenku na dãma suka mallaka, a cikin arzikinku, watau ku zama daidai a ciki kunã tsõron su kamar tSõronku ga kanku? Haka dai Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãne mãsu hankaltawa.
29ôaha! waɗanda suka yi zã1unci sun bi son zũciyõyinsu, bã tãre da wani ilmi ba. To wãne ne zai shiryar da wanda Allah Ya ɓatar, kuma bã su da waɗansu mataimaka?
30Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini,(1) kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
31Kunã mãsu mai da al´amari gare Shi, kuma ku bĩ Shi dataƙawa, kuma ku tsayar da salla, kuma kada ku kasance daga mushirikai.(2)
32Wãtau waɗanda suka rarrabe addininsu kuma suka kasance ƙungiya-ƙungiya, kõwace ƙungiya tanã mai farin ciki da abin da ke a gare ta kawai.
33Kuma idan cũta ta shãfi mutãne, sai su kirãyi Ubangijinsu, sunã mãsu mai da al´amari gare Shi, sa´an nan idan Ya ɗanɗana musu wata rahama daga gare Shi, sai gã wani ɓangare daga gare su sunã shirki da Ubangijinsu.
34Dõmin su kãfirta dl abin da Muka bã su. To ku ji dãɗi kaɗan Sa´an nan zã ku, sani.
35Kõ Mun saukar da wani dalĩ li a gare su? Shi kuwa yanã magana da abin da suka kasance sunã shirkin da shi?
36Kuma idan Muka ɗanɗana wa mutãne wata rahama, sai su yi farin ciki da ita kuma idan cũta ta sãme su, sabõda abin da hannayensu suka gabãtar, sai gã su sunã yanke ƙauna,
37Shin, kuma ba su gani ba cħwa Allah na shimfida arziki ga wanda Yake so kuma Yanã ƙuntatãwa? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu yin ĩmãni.
38Sabõda haka ka bai wa zumu hakkinsa da miskĩnai da ɗan hanya, wannan shĩ ne alhħri ga waɗanda ke nufin yardar Allah kuma waɗancan sũ ne mãsu sãmun babban rabo.
39Kuma abin da kuka bãyar na riba dõmin ya ƙãru a cikin dũkiyar mutãne to, bã zai ƙãru ba, a wurin Allah. Kuma abin da kuka bãyar na zakka, kanã nufin yardar Allah to (mãsu yin haka) waɗancan sũ ne mãsu ninkãwa (ga dũkiyarsu).
40Allah ne Wanda Ya halitta ku, sa´an nan Ya azurta ku, sa´an nan Ya matar da ku, sa´an nan Ya rãyar da ku. Ashe, daga cikin abũbuwan shirkinku akwai wanda ke aikata wani abu daga waɗannan ahũbuwa? Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma Ya ɗaukaka bisa ga abin da suke yi na shirki.
41Ɓarnã tã bayyana a cikin ƙasa da tħku, sabõda abin da hannãyen mutãne suka aikata. Dõmin Allah Ya ɗanɗana musu sãshin abin da suka aikata, ɗammãninsu zã su kõmo.
42Ka ce: "Ku tafi a cikin ƙasã sa´an nan ku dũbi yadda ãƙibar waɗanda suka kasance a gabãninku ta kasance. Mafi yawansu sun kasance mãsu yin shirki."
43Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini madaidaici a gabãnin wani yini ya zo, bãbu makawa gare Shi daga Allah, a rãnar nan mutãne sunã tsãgħwa (su rabu biyu).
44Wanda ya kãfirta,to,kãfircinsa na kansa, kuma wanda ya aikata aikin ƙwarai, to, sabõda kansu suke yin shimfiɗa.
45Dõmin Ya sãkã wa waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga falalarSa. Lalle Allah bã Ya son kafirai.
46Kuma akwai daga ãyõyinSa, ya aika iskõki mãsu bãyar da bushãra kuma dõmin Ya ɗanɗana muku daga rahamarSa, kuma dõmin jirãgen ruwa su gudãna da umurninSa, kuma dõmin ku nħma daga falalarSa, fãtanku zã ku gode.
47Kuma lalle Mun aiki waɗansu Manzanni a gabãninka, zuwa ga mutãnensu sai suka je musu da hujjõji, bayyanannu, sa´an nan Muka azabtar da waɗanda suka yi laifi, kuma ya kasance tabbatacce taimakon mũminai wajibi ne a kan mu.
48Allah ne Wanda ke aika iskõki, sai su mõtsar da girgije, sa´an nan Ya shimfiɗa shi a cikin sama yadda Yake so, kuma Ya sanya shi wani ɓaɓɓake, sa´an nan ka ga ruwa na fita daga tsakãninsa. Sa´an nan idan Allah Ya sãmi waɗanda Ya so daga bãyinsa, Sai gã su suna bushãra da shi.
49Kuma kõ da sun kasance a gabãnin a saukar da shi a kansu, kusa-kusa, sunã baƙin ciki hai bã su iya magana.
50Sai ka dũbi alãmõmin rahamar Allah yadda Yake rãyar da ƙasã a bãyan mutuwarta. Lalle wannan (Mai wannan aiki), tabbas, Mai rãyar da halitta ne, kuma Shi Mai ikon yi ne a kan kõme.
51Kuma lalle idan Mun aika wata iska, suka ganta fatsifatsi, lalle zã su yini a bãyansa sunã kãfirta.
52Sabõda haka, kai, bã ka jiyar da matattu kira, kuma bã ka jiyar da kurãme kira idan sun jũya bãya sunã gudu.
53Kuma ba ka zamo mai shiryar da makãfi ba daga ɓatarsu, bã ka jiyarwa fãce wanda ke yin ĩmãni da ãyõyinMu, watau sũ ne mãsu mĩƙa wuya, su sallama.
54Allah ne Ya halitta ku daga rauni,(1) sa´an nan Ya sanya wani ƙarfi a bayan wani rauni, sa´an nan Ya sanya wani rauni da furfura a bãyan wani ƙarfi, Allah na halitta abin da Ya so, kuma Shĩ ne Mai ilmi, Mai ĩkon yi,
55Kuma a rãnar da Sa´a(2) ke tsayuwa, mãsu laifi na rantsuwã: Ba su zauna a cikin kabari ba fãce sã´a guda. Kamar haka suka kasance anã karkatar da su.
56Kuma waɗanda aka bai wa ilmi da ĩmãni suka ce: "Lalle, haƙĩƙa kun zauna a cikin Littãfin Allah, har zuwa rãnar tãyarwa, to, kuma wannan ita ce rãnar tãyarwar, kuma amma kũ, kun kasance(3) ba ku sani ba."
57To, a rãnar da uzurin waɗanda suka yi zãlunci bã ya amfaninsu, kuma bã a neman yardarsu.
58Kuma lalle tabbas Mun buga kõwane irin misãli ga mutãne a cikin wannan Alƙur´ãni, kuma lalle idan kã je musu da kõwace ãyã, lalle, waɗanda suka kãfirta zã su ce "Kũ, bã kõme kuke ba fãce mãsu barua."
59Kamar haka Allah Yake shãfe haske a kan zukãtan waɗanda ba su sani ba.
60Sabõda haka ka yi haƙuri lalle wa´adin Allah gaskiya ne, kuma kada waɗanda bã su da yaƙĩni su sassabce maka hankali.
Chapter 31 (Sura 31)
1A. L̃. M̃.
2Waɗancan ãyõyin Littãfin ne mai hikima.
3Shiriya da rahama ne ga mãsu kyautatawa.
4Waɗanda ke tsai da salla kuma sunã ɓãyar da zakka kuma sũ, sunã yin ĩmãnin yaƙĩni, ga lãhira.
5Waɗannan sunã a kan shiriya ta daga Ubangijinsu kuma waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
6Kuma akwai daga cikin mutãne wanda ke sayen tãtsuniyõyi(1) dõmin ya ɓatar da mutãne daga hanyar Allah, bã da wani ilmi ba, kuma ya riƙe ta abin izgili! Waɗancan sunã da wata azãba mai wulãkantãwa.
7Kuma idan an karanta ãyõyinMu a gare shi, sai ya jũya bãya, yanã mai girman kai, kamar dai bai saurãre su ba kamar dai akwai wanĩ danni a kan kunnuwansa! To, ka yi masa bushãra da azãba mai raɗaɗi.
8Lalle, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljannar ni´ima.
9Sunã dawwama a cikinsu Allah Yã yi alkawarin, Ya tabbatar da shi. Kuma shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima.
10(Allah) Ya halitta sammai, bã da ginshiƙi wanda kuke gani ba, kuma Yã jħfa duwatsu mãsu kafuwa a cikin ƙasã, dõmin kada ta karkata da ku kuma Ya wãtsa daga kowanc irin dabba a cikinta, kuma Mun saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Muka tsirar a cikinta, daga kõwane nau´i biyu (nami; i da mace) mai ban sha´awa.
11Wannan shĩ ne halittar Allah. To ku nũna mini, "Mħne ne waɗanan da ba Shi ba suka halitta? ôa, azzalumai sunã a cikin ɓata bayyananna."
12Kuma lalle haƙĩƙa Mun bai wa Luƙmãn hikima. (Muka ce masa) Ka gõde wa Allah, kuma wanda ya gõde, to yanã gõdħwa ne dõmin kansa kawai kuma wanda ya kãfirta, to, lalle, Allah Mawadãci ne, Gõdadde.
13Kuma a lõkacin da Luƙmãn ya ce wa ɗansa, alhãli kuwa yanã yi masa wa´azi, "Yã ƙaramin ɗãna! Kada ka yi shirki game da Allah. Lalle shirki wani zãlunci ne mai girma."
14Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu; uwarsa tã ɗauke shi a cikin rauni a kan wani rauni, kuma yãyensa a cikin shekaru biyu (Muka ce masa) "Ka gõde Mini da kuma mahaifanka biyu. Makõma zuwa gare Ni kawai take."
15"Kuma idan mahaifanka suka tsananta(1) maka ga ka yi shirki game da Ni, ga abin da bã ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗã´a. Kuma ka abũce su a cikin dũniya gwargwadon sharĩ´a, kuma ka bi hanyar wanda ya mayar da al´amari zuwa gare Ni, sa´an nan zuwa gare Ni makõmarku take sa´an nan In bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
16"Yã ƙaramin ɗãna! Lalle ita idan gwargwadon ƙwãyar kõmayya ce ta kasance, to, ta kasance a cikin wani falalen dũtse, kõ a cikin sammai, kõ a cikin ƙasã, Allah zai kãwo ta Lalle Allah Mai tausasãwa ne, Masani."
17"Yã ƙaramin ɗãna! Ka tsai da salla, kuma ka yi umurni da abin da aka sani, kuma ka yi hani daga abin da ba a sani ba, kuma ka yi haƙuri a kan abin da ya sãme ka. Lalle, wancan yanã daga muhimman al´amura."
18"Kada ka karkatar da kundukukinka(2) ga mutãne, kada ka yi tafiya a cikin ƙasã kanã mai nũna fãɗin rai. Lalle, Allah bã Ya son dukan mai tãƙama, mai alfahari."
19"Kuma ka tsakaita a tafiyarka, kuma ka runtse ga sautinka. Lalle mafi mũnin sautuka haƙĩƙa shĩ ne sautin jãkuna.(3) "
20Ashe, ba ku gani ba, cħwa Allah Yã hõre muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasã, kuma Ya zuba ni´imõminsa a kanku, bayyanannu da ɓõyayyu? Kuma akwai daga mutãne wanda ke yin jidãli ga al´amarin Allah, bã da wani ilmi ba, kuma bã da wata shiriya ba, kumã ba da wani littãfi mai haskakãwa ba.
21Kuma idan aka ce musu, "Ku bi abin da Allah ya saukar," sai su ce: "ôa, munã bin abin da muka sãmi ubanninmu a kansa." shin kõ dã Shaiɗan nã kiran su ne zuwa ga azãbar sa´ir,
22kuma wanda ya mĩka fuskarsa zuwa ga Allah, alhãli kuma yanã mai kyautatãwa, to, lalle ya yi riƙo ga igiya amintacciya. Kuma zuwa ga Allah ãƙibar al´amura take.
23Kuma wanda ya kãfirta, to, kada kãfircinsa ya baƙanta maka rai, zuwa gare Mu makõmarsu take, sa´an nan Mu bã su lãbari game da abin da suka aikata. Lalle Allah, Masani ne ga abin da ke a cikin ƙirãza.
24Munã jĩshe su dãdi kaɗan sa´an nan Mu tĩlasta su ga shiga zuwa azãba kakkaura.
25Kuma lalle, idan ka tambaye su, "Wãne ne ya halĩtta sammai da kasa?" Lalle zã su ce: "Allah ne." Ka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah" ôa, mafi yawansu ba su sani ba.
26Abin da yake a cikin sammai da ƙasa duka na Allah kawai ne. Lalle, Allah Shĩ ne Mawadãci, Gõdadde.
27Kuma dã dai abin da ke a cikin ƙasa duka, na itãce, ya zama alƙalumma, kuma tħku tanã yi masa tawada, a bayansa da waɗansu tħkuna bakwai kalmõmin Allah ba zã su ƙãre ba.(1) Lalle, Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima.
28Halittarku bã ta zama ba, kuma tãyar da ku bai zama ba, fãce kamar rai guda. Lalle, Allah Mai jĩ ne, Mai gani.
29Ashe, ba ku ga, lalle, Allah Yanã shigar da dare a cikin rãna ba, kuma Yanã shigar da rãna a cikin dare kuma Yã hõre rãnã da watã kõwane yanã gudãna zuwa a ajali ambatacce kuma lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa?
30Wannan fa dõmin Allah Shĩ ne Gaskiya, kuma abin da suke kira wanda bã Shi ba, shi ne ƙaryã, kuma lalle, A1lah shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma.
31Ashe, ba ka ga lalle jirgin ruwa nã gudãna ba a cikin tħku da ni´imar Allah dõmin Ya nũna muku daga ãyõyinSa? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga dukan mai haƙuri, mai gõdiya.
32Kuma idan tãguwar ruwa, kamar duwatsu, ta rufe su, sai su kira Allah sunã tsarkakħwar addini a gare shi. To, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudu, sai daga cikinsu akwai mai taƙaitãwa kuma bãbu mai musun ãyõyinMu fãce dukkan mayaudari mai yawan kãfirci.
33Ya ku mutãne! Ku bauta wa Ubangijinku da taƙawa, kuma ku ji tsõron wani yini, rãnar da wani mahaifi bã ya sãka wa abin haifuwarsa da kõme kuma wani abin haifuwa bã ya sãka wa mahaifinsa da kõme. Lalle wa´adin Allah gaskiya ne. Sabõda haka, kada wata rãyuwa ta kusa ta rũde ku, kuma kada marũɗin(1) nan ya rũɗħ ku game da Allah.
34Lalle, Allah a wurinsa kawai sanin sa´a yake, kuma Yanã saukar da girgije, kuma Yanã sanin abin da yake a cikin mahaiffannai kuma wani rai bai san abin da yake aikatãwa a gõbe ba, kuma wani rai bai san a wace ƙasã yake mutuwa ba. Lalle Allah Masani ne Mai ƙididdidigħwa.
Chapter 32 (Sura 32)
1A. L̃. M̃.
2Saukar da Littafin bãbu shakka a gare shi, daga Ubangijin tãlikai yake.
3Kõ sunã cħwa (Muhammadu ne) ya ƙirƙira shi? ôa, shĩ ne gaskiya daga Ubangijinka, dõmin ka yi gargaɗi ga mutãne waɗanda wani mai gargaɗi bai je musu ba a gabãninka, fãtan zã su shiryu.
4Allah ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu a cikin kwãnuka shida, sa´an nan Ya daidaita a kan Al´arshi. Bã ku da, baicin Shi, wani majiɓinci kuma babu wani maceci. Shin, bã zã ku yi tunãni ba?
5Yanã shirya al´amari daga sama zuwa ga ƙasã, sa´an nan ya tãka zuwa gare Shi a cikin yini, wanda gwargwadonsa shħkaru dubu ne ga abin da kuke lissafãwa.
6Wannan shĩ ne Masanin fake da bayyane, Mabuwãyi, Mai jinƙai.
7Wanda Ya kyautata kõme, Wanda Ya halitta shi. Shi ne kuma Ya fãra halittar mutum daga lãka.
8Sa´an nan Ya sanya ɗiyansa daga wani asali na wani ruwa wulãkantacce.
9Sa´an nan Ya daidaita shi, kuma Ya hũra a cikinsa, daga ruhinSa kuma Ya sanya muku ji, da ganunuwa da zukãta. Gõdiyarku kaɗan ce ƙwarai.
10Kuma suka ce: "Shin, idan mun ɓace a cikin ƙasã, shin, lalle mu, tabbas ne munã zama a cikin wata halitta sãbuwa?" ôa, su game da gamuwa da Ubangijinsu kãfirai
11Ka ce: "Mala, ikin mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke karɓar rãyukanku.(1) Sa´an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku."
12Kuma da kã gani a lõkacin da mãsu laifi suke mãsu sunkuyar da kawunansu a wurin Ubangijinsu, "Ya Ubangijinmu! Mun gani, kuma mun ji, to, Ka mayar da mu mu aikata aiki na ƙwarai. Lalle mũ mãsu yaƙĩni ne."
13Kuma dã Mun so dã Mun bai wa kõwane rai shiriyarsa to, amma magana ta tabbata daga gare Ni! Lalle ne Inã cika Jahannama daga aljannu da mutãne gabã ɗaya.
14To, ku ɗanɗana sabõda abin da kuka manta na haɗuwa da ranarku wannan. Lalle Mũ mã Mun manta da ku, kuma ku dãnɗani azãbar dawwama sabõda abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
15Waɗanda ke ĩmãni da ãyõyinMu kawai, sũ ne waɗanda idan aka karanta musu ãyõyinMu sai su fãɗi sunã mãsu sujada kuma su yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu, alhãli kuwa su bã su yin girman kai.
16Sãsanninsu nã nĩsanta daga wurãren kwanciya, sunã kiran Ubangijinsu bisa ga tsõro da ɗammãni, kuma sunã ciryawa daga abin da Muka azurta su.
17Sabõda haka wani rai bai san abin da aka ɓõye musu ba, na sanyin idãnu, dõmin sakamako ga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
18Shin, wanda ya zama mũmini yanã kamar wanda ya zama fãsiƙi? Bã zã su yi daidai ba.
19Amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwafai, to, sunã da gidãjen Aljannar makõma, a kan liyãfa sabõda abin da suka kasance sunã aikatãwa.
20Kuma waɗanda suka yi fãsiƙanci to makõmarsu ita ce wuta, kõ da yaushe suka yi nufin su fita daga gare ta, sai a mayar da su a cikinta, kuma a ce musu: "Ku ɗanɗana azãbai wutã, wadda kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
21Kuma lalle Munã ɗanɗana musu daga azãba, mafi ƙasƙanci, kãfin a kai ga azãba mafi girma, dõmin fãtan za su kõmo.
22Kuma wãne ne ya fi zãlunci bisa ga wanda aka tunãtar da ãyõyin Ubangijinsa, sa´an na ya bijire daga barinsu? Lalle Mũ, Mãsu yin azãbar rãmuwa ne ga mãsu laifi.
23Kuma lalle haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã Littafi,(1) sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga haɗuwa da shi. Kuma Mun sanya shi ya zama shiriya ga Banĩ Isrã´ĩla.
24Kuma Mun sanya shugabanni daga cikinsu, sunã shiryarwa da umurninMu, a lõkacin da suka yi haƙuri, kuma sun kasance sunã yin yaƙĩni da ãyõyinMu.
25Lalle Ubangijinka shĩ ne zai rarrabe a tsakãninsu a Rãnar Ƙiyãma a cikin abin da suka kasance sunã sãɓa wa jũna a cikinsa.
26Shin, ba ya shiryar da su cħwa da yawa Muka halakara gabãninsu, daga al´ummõmi sunã tafiya a cikin masaukansu?(2) Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi. Shin, ba su jĩ ne?
27Shin, kuma ba su gani ba cħwa lalle Mũ, Munã kõra ruwa zuwa ga ƙasã ƙeƙasasshiya, sa´an nan Mu fitar, game da shi, wata shũka wadda dabbõbinsu, da su kansu ke ci daga gare ta? Ashe fa ba su gani ba?
28Kuma sunã cħwa, "Yaushe wannan hukunci yake, aukuwa idan kun kasance mãsu gaskiya?"
29Ka ce: "Ranar hukuncin nan, ĩmãnin waɗanda suka kãfirta bã zai amfãne su ba (a cikinta) kuma bã zã a yi musu jinkiri ba."
30Sabõda haka ka kau da kai daga barinsu, kuma, ka yi jira lalle, sũ ma mãsu jira ne.
Chapter 33 (Sura 33)
1Yã kai Annabi! Ka bi Allah da taƙawa, kuma kada ka yi ɗã´ã ga kãfirai da munãfukai. Lalle, Allah Ya kasance Mai ilmi, Mai hikima.
2Kuma ka bi abin da aka yi wahayi da shi zuwa gare ka daga Ubangijinka. Lalle, Allah Ya kasance Mai labartawa ga abin da kuke aikatawa.
3Ka dõgara ga Allah. Kuma Allah Ya isa Ya zama wakĩli.
4Allah bai sanya zũciya biyu ba ga wani namiji a cikinsa, kuma bai sanya mãtanku waɗanda kuke yin zihãri daga gare su, su zama uwãyenku ba, kuma bai sanya ɗiyan hankãkarku su zama ɗiyanku ba. wannan abu nãku, maganarku ce da bãkunanku alhãli kuwa Allah na faɗar gaskiya, kuma Shĩ ne ke shiryarwa ga hanyar ƙwarai.
5Ku kira su ga ubanninsu, shi ne mafi ãdalci a wurin Allah. To, idan ba ku san ubanninsu ba, to, ´yan´uwanku ga addini da dĩmajojinku. Kuma bãbu laifi a gare ku ga abin da kuka yi kuskure da shi, kuma amma (akwai laifi) ga abin da zukãtanku suka ganganta, kuma Allah Ya kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
6Annabi ne mafi cancanta(1) ga mũminai bisa ga su kansu, kuma mãtansa uwãyensu ne. Kuma ma´abuta zumunta waɗansunsu sun fi waɗansu a cikin Littãfin Allah bisa ga mũminai da Muhãjirai, fãce fa idan kun aikata wani alhħri zuwa ga majiɓintanku. Wancan yã kasance a cikin Littafi, rubũtacce.
7Kuma a lõkacin da Muka riƙi alkawarin Annabawa daga gare su, kuma daga gare ka, kuma daga Nũhu da Ibrãhĩm da Mũsa da kuma Ĩsã ɗan Maryama,kuma Muka riƙi wani alkawari mai kauri daga gare su.
8Dõmin Ya tambayi mãsu gaskiya a kan gaskiyarsu, kuma Yã yi tattalin wata azãba mai raɗaɗi ga kãfirai.
9Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da waɗansu rundunõni suka zo muku, sai Muka aika wata iskã a kansu da waɗansu rundunõni waɗanda ba ku gani ba, Kuma Allah Yã kasance Mai gani ga abin da kuke aikatãwa.
10A lõkacin da suka zo muku daga samanku da kuma ƙasa daga gare ku, kuma a lõkacin da gannai suka karkata kuma zukãta suka kai ga maƙõsai, kuma kuka yi zaton zace-zace, game da Allah.
11A can aka jarrabi mũminai, kuma aka yi girgiza da su, girgiza mai tsanani.
12Kuma a lõkacin da munafukai da waɗanda akwai cũta a cikin zukãtansu ke cħwa, Allah da ManzonSa, "Ba su yi mana wa´adin kõme ba, fãce rũɗi."
13Kuma a lõkacin da wata ƙungiya daga gare su, ta ce, "Ya mutãnen Yasriba!(1) Bã ku da wani matsayi, sabõda haka ku kõma." Kuma wata ƙungiya daga gare su na nħman izni ga Annabi sunãcħwa, "Lalle gidãjenmu kuranye suke," alhãli kuwa bã kuranye suke ba, bã su da nufin kome fãce gudu.
14Kuma dã an shige ta (Madĩna) a kansu, daga sasanninta, sa´an nan aka tambaye su fitina (kãfirci), lalle dã sun jħ mata, kuma dã ba su zauna a cikinta (Madĩna) ba fãce kaɗan.
15Kuma lalle haƙĩƙa, sun kasance sunã yi wa Allah alkawari, a gabãnin wannan; Bã zã su jũya dõmin gudu ba, kuma alkawarin Allah ya kasance abin tambaya.
16Ka ce: "Gudun nan bã zai amfãne ku ba daga mutuwa ko kisa. Kuma har in kun gudu, bã zã a jĩshe ku dãɗĩ ba fãce kaɗan."
17Ka ce: "Wãne ne wanda yake tsare ku daga Allah, idan Yã yi nufin wata cũta game da ku?" Kuma bã zã su sãmar wa kansu wani majiɓinci ba, banda Allah, kuma bã zã su sãmar wa kansu wani mataimaki ba.
18Lalle Allah Ya san mãsu hana mutãne fita daga cikinku, da mãsu cħwa ga ´yan´uwansu,"Ku zo nan a wurinmu." Kuma bã zã su shiga yãƙi ba fãce kaɗan.
19Suna mãsu rõwa gare ku, sa´an nan idan tsõro ya zo, sai ka gan su sunã kallo zuwa gare ka, idãnunsu sunã kħwaya, kamar wanda ake rufe hankalinsa sabõda mutuwa. Sa´an nan idan tsõron ya tafi,sai su yi muku miyãgun maganganu da harussa mãsu kaifi, sunã mãsu rõwa a kan dũkiya. Waɗannan, ba su yi ĩmani ba, sabõda hakaAllah Ya ɓãta ayyukansu. Kuma wannan ya kasance mai sauƙi ga Allah.
20Sunã zaton ƙungiyõyin kãfirai ba su tafi ba. Kuma idan ƙungiyõyin kãfirai sun zo, sunã gũrin da dai sun zama a karkara a cikin ƙauyãwa, sunã tambayar lãbãranku. Kuma kõ dã sun kasance a cikinku, bã zã su yi yãƙi ba, fãce kaɗan.
21Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasanee yanã fãtan rahamar Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya ambaci Allah da yawa.
22Kuma a lõkacin da mũminai suka ga ƙungiyõyin kãfirai, sai suka ce, "Wannan ne abin da Allah da ManzonSa suka yi mana wa´adi, Allah da ManzonSa sunyi gaskiya." Kuma wannan bai ƙãra musu kõme ba fãce ĩmãni da sallamãwa.
23Daga mũminai akwai waɗansu mazãje da suka gaskata abin da suka yi wa Allah alkwari a kansa, sa´an nan a cikinsu, akwai wanda ya biya bukãtarsa,(1) kuma daga cikinsu akwai wanda ke jira. Kuma ba su musanya ba, musanyawa.
24Dõmin Allah Ya sãka wa masu gaskiya da gakiyarsu, kuma Ya azabtar da munafukai idan Ya so, ko Ya karɓi tũba a kansu. Lalle, Allah Ya kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
25Kuma Allah Yã mayar(2) da waɗanda suka kãfirta da fushinsu, ba su sãmi wani alhħri ba. Allah Ya isar wa mũminai daga barin yãƙi. Kuma Allah Ya kasance Mai ƙarfi, Mabuwãyi.
26Kuma Ya saukar(3) da waɗannan da suka taimake su daga mazõwa Littãfi, daga birãnensu, kuma Ya jħfa tsõro a cikin zukatansu; wata ƙungiya kunã kashħwa, kuma kunã kãma wata ƙungiyar.
27Kuma Ya gãdar da ku gõnakinsu da gidãjensu da dũkiyõyinsu, da wata ƙasa wadda ba ku taɓa tãkarta bã. Kuma Allah ya kasance Mai ĩkon yi ne a kan kõme.
28Yã kai Annabi! Ka ce wa matanka, "Idan kun kasance kunã nufin rãyuwar dũniya da ƙawarta, to, ku zo in yi muku kyautar ban kwãna kuma in sake ku, saki mai kyau."
29"Kuma idan kun kasance kunã nufin Allah da Manzonsa da gidan Lãhria, to, lalle, Allah Yã yi tattalin wani sakamako mai girma ga mãsu kyautatãwa daga gare ku."
30Yã mãtan Annabi! Wadda ta zo da alfãsha bayyananna daga cikinku zã a ninka mata azãba ninki biyu. Kuma wancan yã kasance mai sauƙi ga Allah.
31Kuma wadda ta yi tawãli´u daga cikinku ga Allah da ManzonSa, kuma ta aikata aiki na ƙwarai, zã Mu bã ta sakamakonta ninki biyu, kuma Mun yi mata tattalin arziki ma karimci.
32Yã mãtan Annabĩ! Ba ku zama kamar kõwa ba daga mãtã, idan kun yi taƙawa, sabõda haka, kada ku sassautar da magana, har wanda ke da cũta a cikin zuciyarsa ya yi ɗammani, kuma ku faɗi magana ta alheri.
33Kuma ku tabbata a cikin gidãjenku,(1) kuma kada ku yi fitar gãye-gãye irin fitar gãye-gãye ta jãhiliyyar farko. Kuma ku tsaĩ da salla, kuma ku bãyar da zakka, ku yi ɗã,ã ga Allah da ManzonSa. Allah na nufin Ya tafiyar da ƙazamta kawai daga gare ku, yã mutãnen Babban Gida! Kuma Ya tsarkake ku, tsarkakħwa.
34Kuma ku tuna abin da ake karantawa a cikin ɗãkunanku daga ãyõyin Allah da hukunci. Lalle Allah Yã kasance Mai tausasãwa Mai labartawa.
35Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli´u maza da mãsu tawãlĩu mãtãda mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.
36Kuma ba ya halatta ga mũmini kuma haka ga mũmina, a lõkacin da Allah da Manzonsa Ya hukunta wani umurni, wani zãɓi daga al´amarinsu ya kasance a gare su. Kuma wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa, to, yã ɓace, ɓacħwa bayyananna.(1)
37Kuma a lõkacin(2) da kake cħwa ga wanda Allah Ya yi ni´ima a gare shi kai kuma ka yi ni´ima a gare shi, "Ka riƙe mãtarka, kuma ka bi Allah da taƙawa," kuma kana ɓõyħwa a cikin ranka abin da Allah zai bayyana(3) shi, kanã tsõron mutãne, alhãli kuwa Allah ne Mafi cancantar ka ji tsõronSa. to a lõkacin da zaidu ya ƙãre bukãtarsa daga gare ta, Mun aurar da kai ita, dõmin kada wani ƙunci ya kasance a kan mũminai a cikin (auren mãtan) ɗiyan hankãkarsu, idan sun ƙãre bukãta daga gare su. Kuma umurnin Allah yã kasance abin aikatãwa.
38Wani ƙunci bai kasance a kan Annabi ba ga abin da Allah Ya faralta a kansa, a kan ƙã´idar, Allah a cikin (Annabãwa )waɗanda suka shige daga gabãninsa. Kuma umurnin Allah yã kasance abin ƙaddarãwa tabbatacce.
39Waɗanda ke iyar da Manzancin Allah, kuma sunã tsõronSa, kuma bã su tsõron kõwa fãce Allah, Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai hisabi.
40Muhammadu bai kasance uban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kõme.
41Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ambaci Allah, ambata mai yawa.
42Kuma ku tsarkake shi, a sãfiya da maraice.
43(Allah) Shĩ ne Wanda ke tsarkake ku, da mala´ikunSa (sunã yi muku addu´a), dõmin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske. Kuma (Allah) Yã kasance Mai Jĩn ƙai ga mũminai.
44Gaisuwarsu a rãnar da suke haɗuwa da shi "Salãm", kuma Yã yi musu tattalin wani sakamako na karimci.
45Yã kai Annabi! Lalle Mũ Mun aike ka kanã mai shaida, kuma mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi.
46Kuma mai kira zuwa ga Allah da izninSa, kuma fitila mai haskakãwa.
47Kuma ka yi bushãra ga mũminai cħwa, sũnã da falalamai girma daga Allah.
48Kuma kada ka yi ɗã´a ga kãfirai da munãfukai, kuma ka ƙyã1e cũtarsu (gare ka), kuma ka dõgara ga Allah. Allah Yã isa zama wakĩli.
49Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! idan kun auri mũminai mãtã, sa´an nan kuka sake su a gabãnin ku shãfe su, to, bã ku da wata idda da zã ku lissafa a kansu, kuma ku yi musu kyautar jin dãɗi(1) kuma ku sake su saki mai kyau.
50Yã kai Annabi! Lalle Mũ, Mun halatta maka mãtanka waɗanda ka bai wa sadãkõkinsu da abin da hannun dãmanka ya mallaka daga abin da Allah Ya bã ka na ganĩma, da ´yã´yan baffanka,da ´ya´yan goggonninka da ´yã´yan kãwunka da ´yã´yan innõninka waɗanda suka yi hijira tãre da kai, da wata mace mũmina idan ta bãyar da kanta ga Annabi, idan shi Annabi yanã nufin ya aure ta (hãlin wannan hukunci) kħɓe yake gare ka,banda gamũminai. Lalle Mun san abin da Muka faralta a kansu (smũminai) game da mãtansuda abin da hannayensu suka mallaka. Do min kada wani ƙunci ya kasance a kanka, kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
51Kanã iya jinkirtar da(1) wadda ka ga dãmã daga gare su, kuma kanã tãro wadda kake so zuwa gare ka. Kuma wadda ka nħma daga waɗanda ka nĩsantar, to, bãbu laifi agare ka. Wannan yã fi kusantar da sanyaya idãnunsu, kuma bã zã su yi baƙin ciki ba, kuma su yarda da abin da ka bã su, sũ duka. Kuma Allah Yanã sane da abin da yake a cikin zukãtanku. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai haƙuri.
52Waɗansu mãtã bã su halatta a gare ka a bãyan haka, kuma ba zã ka musanya su da mãtan aure ba, kuma kõ kyaunsu yã bã ka sha´awa, fãce dai abin da hannun dãmanka ya mallaka. Kuma Allah Yã kasance Mai tsaro ga dukan kõme.
53Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada kũ shiga gidãjen Annabi, fãce fa idan an yi izni a gare ku zuwa ga wani abinci, bã da kun tsaya jiran nunarsa ba, kuma amma idan an kira ku, to, ku shiga, sa´an nan idan kun ci, to ku wãtse, kuma bã da kun tsaya kunã masu hĩra da wani Iãbãri ba. Lalle wannan yanã cũtar da Annabi, to, yanã jin kunyarku, alhãli kuwa Allah bã Ya jin kunya daga gaskiya. Kuma idan zã ku tambaye su waɗansu kãyã, to, ku tambaye su daga bãyan shãmaki. Wannan ya fi muku tsarki ga zukãtanku da zukãtansu. Kuma bã ya halatta a gare ku, ku cũci Manzon Allah, kuma bã ya halatta ku auri mãtansa a bãyansa har abada. lalle wannan a gare ku yã kasance babban abu a wurin Allah.
54Idan kun bayyana wani abu, kõ kuma kuka ɓõye shi, to, lalle Allah Ya kasance Masani ga kõme.
55Bãbu laifi a kansu game da ubanninsu, kuma bãbu game da ɗiyansu, kuma bãbu game da ´yan´uwansu maza, kuma bãbu game da ɗiyan ´yan´uwansu maza, kuma bãbu game da ɗiyan ´yan´uwansu mãtã, kuma bãbu game da mãtan mũminai, kuma bãbu game da abin da hannãyensu suka mallaka, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Yã kasance Mahalarci a kan kõme.
56Lalle, Allah da malã´ikunSa sunã salati(1) ga Annabi. Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni!Ku yi salãti a gare shi, kuma ku yi sallama dõmin amintarwa a gare shi.
57Lalle waɗanda ke cũtar Allah da MauzonSa Allah Yã la´ane su, a cikin dũniya da Lãhira, kuma Yã yi musu tattalin azãba mai wulãkantarwa.
58Kuma waɗanda suke cũtar mũminai maza dã muminai mãtã, bã da wani abu da suka aikata ba to, lalle sun ɗauki ƙiren ƙarya da zunubi bayyananne.
59Yã kai Annabi! Ka(2) ce wa mãtan aurenka da ´yã´yanka da mãtan mũminai su kusantar da ƙasã daga manyan tufãfin da ke a kansu. Wancan ya fi sauƙi ga a gane su dõmin kada a cũce su. Kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai Jin ƙai.
60Lalle, idan munãfukai da waɗanda yake akwai wata cuta a cikin zukãtansu, da mãsu tsħgumi a cikin Madĩna, ba su hanu ba (daga hãlãyensu), (3) lalle, zã Mu shũshũta ka a gare su, sa´an nan bã zã su yi maƙwabtaka da kai ba, a cikinta, fãce kaɗan.
61Sunã la´anannu, inda duka aka sãme su a kãmã su, kuma a karkashe su karkashħwa.
62A kan hanyar Allah (ta gyaran jama´a) a cikin waɗanda suka shũɗe gabãninka, kuma bã zã ka sãmi musanyãwa ba ga hanyar Allah.
63Sunã tambayar ka(1) ga Sã´a. Ka ce: "Saninta yanã wurin Allah kawai." Kuma me yã sanar da kai cħwa anã tsammãnin sa´a ta kasance kusa?
64Lalle Allah Yã la´ani kãfirai, kuma Yã yi musu tattalin wata wuta mai ƙũna.
65Sunã madawwama a cikinta har abada, bã su sãmun majiɓinci, kuma bã su sãmun mataimaki.
66Rãnar da ake jũya fuskõkinsu a cikin wuta sunã cħwa, "Kaitonmu, sabõda,rashin biyarmu ga Allah da rashin biyarmu ga Manzo!"
67Kuma suka ce: "Yã Ubangijinmu! Lalle mũ mun(2) bi shugabanninmu da manyanmu! Sai suka ɓatar da mu daga hanya!
68"Yã Ubangijinmu! Ka ba su ninki biyu na azãba, kuma ka la´ane su, la´ana mai girma."
69Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kasance kamar waɗanda suka cũci(3) Mũsã sa´an nan Allah Ya barrantar da shi daga abin da suka ce. Kuma ya kasance mai daraja a wurin Allah.
70Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku faɗi magana madaidaiciya.
71Ya kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gãfarta zunubanku. Kuma wanda ya yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, to, lalle, yã rabbanta, babban rabo mai girma.
72Lalle Mũ, Mun gitta amãna ga sammai da ƙasã da duwãtsu, sai suka ƙi ɗaukarta kuma sukaji tsõro daga gare ta, kuma mutum ya ɗauke ta, lalle shĩ (mutum) ya kasance mai yawan zãlunci, mai yawan jãhilci.
73Dõmin Allah Ya azabta munãfukai maza da munãfukai mãtã, da mushirikai maza da mushirikai mãtã, kuma Allah Yã karɓi tũba ga mũminai maza da mũminai mãtã. Kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai.
Chapter 34 (Sura 34)
1Gõdiya ta tabbata ga Allah, wanda Yake abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã Nãsa ne, kuma shĩ ne Mai hikima, Mai labartawa.
2Yã san abin da yake shiga a cikin ƙasã da abin da yake fita daga gare ta, da abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa a cikinta, kuma Shĩ ne Mai jin ƙai, Mai gãfara.
3Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Sã´a bã zã ta zo mana ba." Ka ce: "Kayya! Na rantse da Ubangijĩna, lalle, zã ta zõ muku." Masanin gaibi, gwargwadon zarra bã ta nĩsanta daga gare Shi a cikin sammai kuma bã ta nĩsanta a cikin ƙasã, kuma bãbu mafi ƙaranci daga wancan kuma bãbu mafi girma fãce yanã a cikin Littãfi bayyananne.
4Dõmin Ya sãkã wa waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Waɗancan suna da wata gãfara da wani arziki mai karimci.
5Kuma waɗanda suka yi mãkirci ga ãyõyinMu, sunã mãsu gajiyarwa, waɗannan sunã da wata azãba daga azãba mai raɗaɗi.
6Kuma waɗanda aka bai wa ilmi sunã ganin abin nan da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, shi ne gaskiya, kuma yanã shiryarwa zuwa ga hanyar Mabuwãyi, Gõdadde.
7Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Shin zã mu nũna muku wani namiji wanda yake gaya muku wai idan an tsattsãge ku, kõwace irin tsattsãgħwa, lalle kũ, tabbas, kunã a cikin wata halitta sãbuwa.?"
8"Ya ƙãga ƙarya ga Allah ne kõ kuwa akwai wata hauka a gare shi?" ôa, waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba, sunã a cikin azãba da ɓãta mai nĩsa.
9Ashe fa, ba su yi dũbi ba zuwa ga abin da ke a gaba gare su da abin da ke a bãyansu daga sama da ƙasã? idan Mun so, sai Mu shãfe ƙasã da su, kõ kuma Mu kãyar da wani ɓaɓɓake daga sama a kansu. Lalle, a cikin wancan akwai ãyã ga dukan bãwã mai maida al´amarinsa ga Allah.
10Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun bai wa Dãwũda wata falala dagagare Mu. Yã duwatsu, ku konkõma sautin tasbihi tãre da shi kuma da tsuntsãye. Kuma Muka tausasa masa baƙin ƙarfe.
11Ka aikata sulkuna kuma ka ƙaddara lissãfi ga tsãrawa, kuma ka aikata aikin ƙwarai. Lalle NĩMai gani ne ga abin da kuke aikatãwa.
12Kuma ga Sulaimãn, Mun hõre masa iska, tafiyarta ta safiya daidai da wata, kuma ta maraice daidai da wata. Kuma Muka gudãnar masa da marmaron gaci, kuma daga aljannu (Muka hõre masa) waɗanda ke aiki a gaba gare shi, da iznin Ubangijinsa. Wanda ya karkata daga cikinsu, daga umurninMu, sai Mu ɗanɗana masa daga azãbar sa´ĩr.
13Sunã aikata masa abin da yake so, na masallatai da mutummutumai da akussa kamar kududdufai, da tukwãne kafaffu. Ku aikata gõdiya, yã ɗiyan Dãwũda, kuma kaɗan ne mai gõdiya daga bãyĩNa.
14Sa´an nan a lõkacin da Muka hukunta mutuwa a kansa bãbu abin da ya ja hankalinsu, a kan mutuwarsa, fãce dabbar ƙasa (gara) wadda take cin sandarsa. To a lõkacin da ya fãɗi, sai aljannu suka bayyana (ga mutãne) cħwa dã sun kasance sun san gaibi, dã ba su zauna ba a cikin azãba mai wulãkantarwa.
15Lalle, haƙĩƙa, akwai ãyã ga saba´ãwa(1) a cikin mazauninsu: gõnakin lambu biyu, dama da hagu. "Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku yi gõdiya gare shi. Gari mai dãɗin zama, da Ubangiji Mai gãfara."
16Sai suka bijire sabõda haka Muka saki Mãlãlin Arimi (dam) a kansu, kuma Muka musanya musu gõnakinsu biyu da waɗansu gõnaki biyu mãsu ´ya´yan itãce kaɗan: talãkiya da gõriba da wani abu na magarya kaɗan.
17Wancan, da shi Muka yi musu sakamako sabõda kãfircinsu. Kuma lalle, bã Mu yi wa kõwa(2) irin wannan sakamako, fãce kafirai.
18Kuma Muka sanya, a tsakaninsu da tsakãnin(3) garũruwan da Muka Sanya albarka a cikinsu, waɗansu garũruwa mãsuganin jũna kuma Muka ƙaddara tafiya a cikinsu, "Ku yi tafiya a cikinsu, darũruwa da rãnaiku, kunã amintattu."
19Sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka nĩsantar da tsakãnin tafiyõyinmu," kuma suka zãlunci kansu, sabõda haka Muka sanya su lãbãran hĩra kuma Muka kekkħce su(4) kõwace, irin kekkħcewa. Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga dukan mai yawan haƙuri, mai yawan gõdiya.
20Kuma lalle, haƙĩƙa, Iblĩs ya gaskata zatonsa a kansu, sai suka bi shi fãce wani ɓangare na mũminai.
21Kuma bã ya da wani dalĩli a kansu fãce dai dõmin Mu san wanda yake yin ĩmãni da Lãhira daga wanda yake a cikin shakka daga gare ta. Kuma Ubangijinka, a kan kõme, Mai tsaro ne.
22Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya (cħwa abũbuwan bautãwa ne) baicin Allah, bã su Mallakar ma´aunin zarra a cikin sammai, kuma bã su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bã su da wani rabon tãrħwa a cikinsu (sammai da ƙasa),kuma bã Shi da wani mataimaki daga gare su.
23"Kuma wani cħto bã ya amfãni a wurinSa face fa ga wanda Ya yi izni a gare shi. Har a lõkacin da aka kuranye(1) tsõro daga zukãtansu, sai su ce, ´Mħne ne Ubangijinku Ya ce?´ Suka ce: ´Gaskiya´, kuma shi ne Maɗaukaki, Mai girma,"
24Ka ce: "Wãne ne yake azurta ku daga sama da ƙasa?" Ka ce: "Allah kuma lalle mũ kõ ku, wani yanã a kan shiriya, kõ yana a cikin ɓata bayyananniya."
25Ka ce: "Bã zã a tambaye ku ba ga abin da muka aikata daga laifi, kuma bã zã a tambaye mu daga abin da kuke aikatawa ba."
26Ka ce: "Ubangijinmu zai tãra tsakãninmu, sa´an nan Ya yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya. Kuma Shĩ ne Mahukunci, Masani."
27Ka ce: "Ku nũna mini waɗanda kuka riskar da Shi, su zama abõkan tãrayya. ôa, Shĩ ne Allah, Mabuwãyi, Mai hikima."
28Kuma ba Mu aika ka ba fãce zuwa ga mutãne gabã ɗaya, kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
29Sunã cħwa, "Yaushe ne wannan wa´adi zai auku idan kun kasance mãsu gaskiya?"
30Ka ce: "Kunã da mi´ãdin wani yini wanda bã ku jinkirta daga gare shi kõ da sa´a ɗaya, kuma bã ku gabãta."
31Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Bã zã mu yi ĩmanida wannan Alƙur´ãni ba, kuma bã zã mu yi ĩmani da abin da yakea gabãninsa ba (na waɗansu littattafan sama)." Kuma dã kã gani a lõkacin da azzãlumai suke abin tsayarwa wurin Ubangijinka, sashensu na mayar wa sãshe maganar maraunana (mabiya) suke cħwa makangara (shũgabanni) "Ba dõminku ba, lalle, dã mun kasance mũminai."
32Makangara suka ce wa maraunana, "Ashe, mũ ne muka kange ku daga shiriya a bãyan ya zo muku? Ã,a´ kun dai kasance mãsu laifi."
33Kuma maraunana suka ce wa makangara. "ôa, (ku tuna) mãkircin dare da na rãna a lõkacin da kuke umurnin mu da mu kãfirta da Allah, kuma mu sanya Masa abõkan tãrayya." Kuma suka assirtar da nadãma a lõkacin da suka ga azãba. Kuma Muka sanya ƙuƙumma a cikin wuyõyin waɗanda suka kãfirta. Lalle, bã zã a yi musu sakamako ba fãce da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
34Kuma ba mu aika wani mai gargaɗi ba a cikin wata alƙarya fãce mani´imtanta (shũgabanni) sunce, "Lalle mũ, mãsu kãfirta ne da abin da aka aiko ku da shi."
35Kuma suka ce: "Mũ ne mafiya yawa ga dũkiya da ɗiya, kuma mu ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
36Ka ce: "Lalle, Ubangijĩna Yanã shimfiɗa arziki ga wanda Ya so, kuma Yanã ƙuntatãwa, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba."
37Kuma dũkiyarku ba ta zamo ba, haka ɗiyanku ba su zamo abin da yake kusantar da ku ba a wurinMu, kusantarwar muƙãmi fãce wanda, ya yi ĩmãni kuma ya aikata aikin ƙwarai. To, waɗannan sunã da sakamakon ninkawa sabõda abin da suka aikata. Kuma su amintattu ne a cikin bħnãye.
38Kuma waɗanda suke mãkirci a cikin ãyõyinMu, sunã nħman gajiyarwa, waɗannan abin halartãwa ne a cikin azãba.
39Ka ce: "Lalle, Ubangijĩna Yanã shimfida arziki ga wanda Ya so daga bãyinSa, kuma Yanã ƙuntatãwa a gare shi, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu, to, Shĩ ne zai musanya shi, kuma Shĩ ne Mafi fĩcin mãsu azurtawa."
40Kuma rãnar da Allah Ya ke tãra su gabã ɗaya, sa´an nan Ya ce wa Malã´iku, "Shin, waɗannan kũ ne suka kasance sunã bauta wa?"
41Sukace: "Tsarki ya tabbata a gare Ka. Kai ne Majiɓincinmu, bã su ba. ôa,sun kasance sunã bauta wa aljannu. Mafi yawansu, da sũ suka yi ĩmani."
42Sabõda haka, a yau sãshenku bã ya mallakar wani amfãni ga wani sãshen, kuma bã ya mallakar wata cũta, kuma Munã cħwa ga waɗanda suka yi zalunci, Ku ɗanɗani azabar wutã wadda "kuka kasance game da ita, kunã ƙaryatãwa."
43Kuma idan an karanta ãyõyinMu bayyanannu a kansu, sai su ce: "Wannan bai zama ba fãce namiji ne yanã son ya kange ku daga abin da ubanninku suka kasance sunã bauta wa." Kuma su ce: "Wannan bai zama ba fãce ƙiren ƙarya da aka ƙãga." Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: ga gaskiya a lõkacin da ta je musu: "Wannan bã kõme ba fãce sihiri ne bayyananne."
44Kuma ba Mu bã su waɗansu littattafai ba waɗanda suke karãtun su, kuma ba Mu aika wani mai gargaɗi ba zuwa gare su a gabãninka!
45Kuma waɗanda suke a gabãninsu, sun ƙaryata ,alhãli kuwa ba su kai ushurin-ushurin abin da Muka bã su ba, sai suka ƙaryata ManzanniNa! To, yãya musũNa (ga maƙaryata) ya kasance?
46Ka ce: "Ina yi muku wa´azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu dõmin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa´an nan ku yi tunãni, bãbu wata hauka ga ma´abũcinku. Shĩ bai zama ba fãce mai gargaɗi ne a gare ku a gaba ga wata azãba mai tsanani.
47Ka ce: "Abin da na rõƙe ku na wani sakamako, to, amfãninsa nãku ne. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Allah, kuma shi Mahalarci ne a kan dukan kõme."
48Ka ce: "Lalle Ubangijina Yanã jħfa gaskiya.(Shi) Masanin abũbuwan fake ne."
49Ka ce: "Gaskiya ta zo, kuma ƙarya bã ta iya fara (kome) kuma bã ta iya mayarwa."
50Ka ce: "Idan na ɓace, to, inã ɓacħwa ne kawai a kan kaina. Kuma idan na shiryu, to, sabõda abin da Ubangijina Yake yõwar wahayi ne zuwa a gare ni. Lalle Shĩ Mai ji ne, Makusanci."
51Kuma dã kã gani, a lõkacin da suka firgita, to, bãbu kuɓuta, kuma aka kãma su daga wuri makusanci.
52Kuma suka ce: "Mun yi ĩmãni da Shi." To inã zã su sãmu kãmãwa daga wuri mai nisa?
53Kuma lalle sun kãfirta da Shi a gabãnin haka, kuma sunã jĩfa da jãhilci daga wuri mai nĩsa.
54Kuma an shãmakance a tsakãninsu da tsakãnin abin da suke marmari, kamar yadda aka aikata da irin ƙungiyõyinsu a gabãninsu. Lalle sũ sun kasance a cikin shakka mai sanya kõkanto.
Chapter 35 (Sura 35)
1Gõdiya ta tabbata ga Allah, Mai fãra halittar sammai da ƙasã, Mai sanya malã´iku manzanni mãsu fukãfukai, bibbiyu, da uku-uku da hurhuɗu. Yanã ƙãrãwar abin da Ya ke so a cikin halittar. Lalle Allah Mai ĩkon yi ne a kan kõme.
2Abin da Allah Ya buɗa wa mutãne daga rahama, to, bãbu mai riƙewa a gare shi, kuma abin da Ya riƙe, to, bãbu mai saki a gare shi, waninSa, kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima.
3Yã kũ mutãne! Ku tuna ni´imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasã? Bãbu wani abin bautãwa, fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?
4Kuma idan sun ƙaryata ka, to, lalle, an ƙaryata waɗansu Manzanni a gabãninka, kuma zuwa ga Allah ake mayar da al´amura.
5Yã kũ mutãne! Lalle wa´adin Allah gaskiya ne, sabõda haka kada rãyuwar dũniya ta rũɗar da ku, kuma kada marũɗi ya rũɗe ku game da Allah.
6Lalle Shaiɗan maƙiyi ne a gare ku, sai ku riƙe shi maƙiyi. Yanã kiran ƙungiyarsa kawai ne, dõmin su kasance ´yan sa´ir.
7Waɗanda suka kãfirta suna da azãba mai tsanani kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wata gãfara da sakamako mai girma.
8Shin to, wanda aka ƙawãta masa aikinsa, har ya gan shi mai kyau (yanã daidai da waninsa)? Sabõda haka, lalle, Allah Yanã ɓatar da wanda Yake so, kuma Yanã shiryar da wanda Yake so, sabõda haka kada ranka ya halaka a kansu dômin baƙin ciki. Lalle Allah Masani ne ga abin da suke sanã´antawa.
9Kuma Allah ne Ya aika da iskõki har su mõtsar da girgije, sa´an nan Mu kõra shi zuwa ga gari matacce, sa´an nan Mu rãyar da ƙasã game da shi a bayan mutuwarta. Kamar wancan ne Tãshin Ƙiyãma yake.
10Wanda ya kasance yanã nħman wata izza, to, Allah ne da izza gabã ɗaya. zuwa gare Shi magana mai dãɗi ke hawa, kuma aiki na ƙwarai Yanã ɗaukar ta Kuma waɗanda ke yin mãkircin mũnanan ayyuka, sunã da wata azãba mai tsanani, kuma mãkircin waɗannan yanã yin tasgaro.
11Kuma Allah ne Ya halitta ku daga turɓãya, sa´an nan daga ɗigon maniyyi, sa´an nan Ya sanya ku surkin maza da mãtã. Kuma wata mace bã ta yin ciki, kuma bã ta haihuwa, fãce da saninSa, kuma bã zã a rãyar da wanda ake rãyarwa ba, kuma bã zã a rage tsawon ransa ba fãce yanã a cikin Littãfi. Lalle, wancan mai sauki ne ga Allah.
12Kuma kõguna biyu ba su daidaita: Wannan mai ruwan dãɗi, mai zãƙi, mai sauƙin haɗiya kuma wannan mai ruwan gishiri mai zartsi, kuma daga kõwane, kunã cin wani nama sãbo, kuma kunã fitar da kawa wadda kuke tufantarta, kuma kanã ganin jirãge a cikinsa sunã mãsu gudãna, dõmin ku nħmo daga falalarSa, kuma ɗammãninku zã ku dinga gõdħwa.
13Yanã shigar da dare a cikin rãna, kuma Yanã shigar da rãna a cikin dare. Kuma Ya hõre rãnã da watã kõwannensu yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce Wannan Shĩ ne Allah, Ubangijinku, gare Shi mulki yake, kuma waɗanda kuke kira waninSa bã su mallakar kõ fãtar gurtsun dabĩno.
14Idan kun kira su, bã zã su ji kiranku ba, kuma kõ sun jiya, bã zã su karɓa muku ba, kuma a Rãnar Ƙiyãma zã su kãfirce wa shirkinku, kuma bãbu mai bã ka lãbãri, kamar wanda ya sani.
15Yã kũ mutãne! Kũ ne mãsu bukãta zuwa ga Allah, kuma Allah, Shĩ ne Mawadãci, Gõdadde.
16Idan Ya so, zai tafi da ku, kuma Ya zo da wata halitta sãbuwa.
17Kuma wancan bai zama mabuwãyi ba ga Allah.
18Kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, bai ɗaukar nauyin wani rai. Kuma idan ran da aka nauyaya wa kãya ya yi kira (ga wani mataimaki) zuwa ga kãyansa, bã zã a dauki kõme ba daga gare shi, kuma kõ dã (wanda ake kiran) yã kasance makusancin zumunta ne. Kanã gargaɗi kawai ne ga waɗanda ke tsoron Ubangijinsu a fake, kuma suka tsayar da salla. Kuma wanda ya tsarkake, to, yanã tsarkaka ne dõmin kansa. Kuma zuwa ga Allah kawai makõma take.
19Kuma makãho bã ya daidaita da mai gani.
20Kuma duffai bã su daidaita, kuma haske bã ya daidaita.
21Kuma inuwa bã ta daidaita, kuma iskar zãfi bã ta daidaita.
22Kuma rãyayyu bã su daidaita kuma matattu ba su daidaita. Lalle Allah Yanã jiyar da wa´azi ga wanda Ya so, kuma ba ka jiyar da waɗanda suke a cikin kaburbura.
23Ba ka zama ba fãce mai gargaɗi kawai.
24Lalle Mũ Mun aike ka da gaskiya, kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi. Kuma bãbu wata al´umma fãce wani mai gargaɗi yã shũɗe a cikinta.
25Kuma idan sunã ƙaryata ka, to, haƙĩƙa, waɗanda suke a gabãninsu sun ƙaryata. Manzanninsu sun jħ musu da hujjõji, kuma da takardu, kuma da Littafi mai haske.
26Sa´an nan Na kãma waɗanda suka kãfirta. To, yãya musũNa yake?
27Ba ka gani ba, lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama? Sai Muka fitar, game da shi,´yã´yan itãce mãsu sãɓanin launuka kuma daga duwatsu akwai zane-zane, farfaru da jãjãye, mãsu sãɓanin launin, da mãsu launin baƙin ƙarfe, baƙãƙe.
28Kuma daga mutãne da dabbõbi da bisãshen gida, mãsu sãɓãnin launinsu kamar wancan. Malamai kawai ke tsõron Allah daga cikin bãyinSa. Lalle, Allah, Mabuwãyi ne, Mai gãfara.
29Lalle waɗanda ke karãtun Littãfin Allah(1) kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar daga abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, sunã fãtan (sãmun) wani fatauci ne wanda bã ya yin tasgaro.
30Dõmin (Allah) zai cika musu sakamakonsu, kuma Ya ƙarã musu daga falalarSa. Lalle Shi Mai gãfara ne, Mai gõdiya.
31Kuma abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, daga Littãfi, shi ne gaskiya, mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi. Lalle ne Allah ga bãyinSa, haƙĩƙa, Mai labartawa ne, Mai gani.
32Sa´an nan Mun gãdar da Littãfin, ga waɗanda Muka zãɓa daga bãyinMu, sa´an nan daga cikinsu, akwai mai zãlunci ga kansa, kuma daga cikinsu akwai mai tsakaitãwa, kuma daga cikinsu akwai mai tsħrħwa da ayyukan alhħri da iznin Allah. Waccan ita ce falalar (Allah) mai girma.
33Gidãjen Aljannar zamã sunã shigar su. Anã ƙawãce su a cikinsu, da ƙawã ta mundãye daga zĩnãriya da lu´ulu´u, kuma tufãfinsu, a cikinsu alharĩni ne.
34Kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya tafiyar da baƙin ciki daga gare mu. Lalle Ubangijinmu, haƙĩƙa Mai gafarane, Mai godiya."
35"Wanda Ya saukar da mu a gidan zamã, daga falalarSa, wata wahala bã ta shãfar mu a cikinsa, kuma wata kãsãwa bã ta shãfar mu a cikinsa."
36Kuma waɗanda suka kãfirta sunã da wutar Jahannama, bã a yin hukunci a kansu balle su mutu kuma bã a sauƙaƙa musu daga azãbarta. Kamar haka Muke sãka wa kõwane mai yawan kãfirci.
37Kuma sũ, sunã hargõwar nħman ãgaji a cikinta. (Sunã cħwa) "Yã Ubangijinmu! Ka fitar da mu, mu aikata aiki mai kyau, wanin wanda muka kasance munã aikatãwa." Ashe, kuma, ba Mu rãyar da ku ba, abin da mai tunãni zai iya yin tunãni a ciki, kuma mai gargaɗi yã jħ muku? To, ku ɗanɗana, sabõda haka bãbu wani mataimaki, ga azzãlumai.
38Lalle Allah ne Masanin gaibin sammai da ƙasã. Lalle Shĩ ne Masani ga abin da yake ainihin zukata.
39Shĩ ne Wanda Ya sanya ku mãsu maye wa junã, a cikin ƙasã. To, wanda ya kãfirta, to, kãfircinsa yanã a kansa. Kuma kãfircin kãfirai bã ya kãra musu kõme fãce baƙin jini, kuma kãfircin kãfirai bã ya kãra musu kõme face hasãra.
40Ka ce: "Shin, kun ga abũbuwan shirkinku, waɗanda kuke kira, wasun Allah? Ku nũna mini, mħne ne suka halitta daga ƙasã? Kõ sunã da tãrayya ne a cikin sammai? Kõ kuma Mun bã su wani littãfi ne sabõda haka sunã a kan wata hujja ce daga gare shi? ôa, azzãlumai bã su yin wani wa´adi, sãshensu zuwa ga sãshe, fãce rũɗi."
41Lalle Allah Yanã riƙe sammai da ƙasã dõmin kada su gushe. Kuma haƙĩƙa, idan sun gushe, bãbu wani baicinSa da zai riƙe su. Lalle Shi Yã kasance Mai haƙuri, Mai gãfara.
42Kuma suka(1) yi rantsuwa da Allah, mafi nauyin rantsuwarsu, "Lalle, idan wani mai gargaɗi ya zo musu tabbas zã su kasance mafi shiryuwa, daga ɗayan al´ummõmi." To, a lõkacin da mai gargaɗi ya jħ musu, bai ƙarã su da kõme ba fãce gudu.
43Dõmin nũna girman kai a cikin ƙasã da mãkircin cũta. Kuma mãkirci na cũta bã ya fãdãwa fãce a kan mutãnensa. To shin sunã jiran (wani abu ne) fãce dai hanyar (kãfiran) farko. To, bã zã ka sãmi musanya ba ga hanyar Allah. Kuma bã zã ka sãmi jũyarwa ba ga hanyar Allah.
44Ashe, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã, dõmin su dũba yadda ãƙibar waɗannan da suke a gabãninsu ta kasance? Alhãli kuwa sun kasance mafĩfĩta ƙarfi daga gare su? Kuma Allah bai kasance wani abu nã iya rinjãyarSa ba, a cikin sammai, kuma haka a cikin kaƙã. Lalle Shi ne Ya kasance Masani, Mai ĩkon yi.
45Kuma dã Allah Yanã kãma mutãne sabõda abin da suka aikata, dã bai bar wata dabba ba a kanta (kasã). Amma Yanã jinkirta musu zuwa ga ajalin da aka ambatã. Sa´an nan idan ajalinsu ya zo, to, lalle Allah yã kasance Mai gani ga bãyinSa.
Chapter 36 (Sura 36)
1Y. S̃.
2Inã rantsuwa da Al-ƙur´ãni(1) Mai hikima.
3Lalle kai, haƙĩƙa kanã cikinManzanni.
4A kan hanya madaidaiciya.
5(Allah Ya saukar da Al-kur´ãni) saukarwar Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
6Dõmin ka yi gargaɗi ga waɗansu mutãne da ba a yi gargaɗi ga ubanninsu ba, sabõda haka sũmasu rafkana ne.
7Lalle, haƙĩƙa, kalma(2) tã wajaba a kan mafi yawansu, dõmin sũ, bã zã su yi ĩmãni ba.
8Lalle Mũ, Mun sanya ƙuƙumma a cikin wuyõyinsu, sa´an nan sũ (ƙuƙumman sun kai) har zuwa ga haɓõɓinsu, sabõda haka, sũ banƙararru ne.
9Kuma Muka sanya wata tõshiya a gaba gare su, da wata tõshiya a bãyansu, sabõda haka Muka rufe su, sai suka zama bã su gani.
10Kuma daidai yake a gare su, shin, ka yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, sũ bã zã su yi ĩmãni ba.
11Kanã yin gargaɗi kawai ga wanda ya bi Alƙur´ãni ne, kuma ya ji tsõron mai rahama a fake. To, ka yi masa bushãra da gãfara da wani sakamako na karimci.
12Lalle Mũ, Mũ ne ke rãyar da matattu kuma Mu rubũta abin da suka gabãtar, da gurãbunsu, kuma kõwane abu Mun ƙididdige shi, a cikin babban Littãfi Mabayyani.
13Kuma ka buga musu misãli: Waɗansu ma´abũta alƙarya, a lõkacin da Manzanni(1) suka jħ mata.
14A lõkacin da Muka aika (Manzannin) biyu zuwa gare su, sai suka ƙaryata su, sa´an nan Muka ƙarfafa (su) da na uku, sai suka ce: "Lalle mũ, Manzanni ne zuwa gare ku."
15Suka ce: "Kũ ba ku zamo bafãce mutãne ne kamarmu kuma Mai rahama bai saukar da kõme ba, ba ku zamo ba fãce ƙarya kuke yi."
16Suka ce: "Ubangijinmu Yã sani, lalle mũ, haƙiƙa Manzanni nezuwa gare ku."
17"Kuma bãbu abin da ke kanmu, fãce iyar da manzanci bayyananne."
18Suka ce: "Lalle mũ munã shu´umci da ku! Haƙĩƙa idan ba ku, hanu ba, haƙĩƙa, zã mu jħfe ku, kuma haƙĩƙa wata azãba mai raɗaɗi daga gare mu zã ta shãfe ku."
19Suka ce: "Shu´umcinku, yanã tãre da ku. Ashe, dõmin an tunãtar da ku? ôa, kũ dai mutãne ne mãsu ƙħtare haddi."
20Kuma wani mutum daga mafi nĩsan birnin ya je, yanã tafiya da gaggãwa, ya ce: "Ya mutãnħna! Ku bi Manzannin nan.
21"Ku bi waɗanda bã su tambayar ku wata ijãra kuma sũ shiryayyu ne."
22"Kuma mene ne a gare ni, bã zan bauta wa Wanda Ya ƙãga halittata ba, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku?"
23"Shin, zan riƙi waninSa abũbuwan bautãwa? Idan Mai rahama Ya nufe ni da wata cũta, to cħtonsu bã ya amfanĩna da kõme, kuma bã za su iya tsãmar da ni bã."
24"Lalle nĩ, a lõkacin nan, tabbas, inã a cikin ɓata bayyananna."
25"Lalle ni, nã yi ĩmãni da Ubangijinku, sabõda haka ku saurãre ni."
26Aka ce(2) (masa), "Ka shiga Aljanna." Ya ce, "Dã dai a ce mutãnħna sunã iya sani."
27"Game da gãfarar da Ubangijjĩna ya yi mini, kuma Ya sanya ni a cikin waɗanda aka girmama."
28Kuma ba Mu saukar da waɗansu runduna ba daga sama(1) a kan (halaka) mutãnensa, daga bãyansa, kuma bã zã Mu kasance. Mãsu saukarwa ba.
29Ba ta kasance ba face tsawa guda, sa´an nan sai gã su sõmammu.
30Yã nadãma a kan bãyĩNa! Wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu yi masa izgili.
31Ba su gani ba, da yawa Muka halakar da (mutãnen) ƙarnõni a gabãninsu kuma cħwa su bã zã su kõmo ba?
32Kuma lalle bãbu kõwa fãce waɗanda ake halartarwa ne a wurinMu.
33Kuma ãyã ce a gare su: Ƙasã matacciya, Mu rãyar da ita, Mu fitar da ƙwãya daga gare ta, sai gã shi daga gare ta suke ci.
34Kuma Muka sanya, a cikinta (ƙasã), waɗansu gõnaki na dabĩno da inabõbi, kuma Muka ɓuɓɓugar da ruwa daga marħmari a cikinta.
35Dõmin su ci ´ya´yan itãcensa, alhãli kuwa hannãyensu ba su aikata shi ba. Shin, to, bã zã su gõdħ ba?
36Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya halitta nau´uka, namiji da mace, dukansu, daga abin da ƙasã ke tsirarwa, kuma daga kansu, kuma daga abin da ba su sani ba.
37Kuma ãyã ce a gare su: Dare Muna feɗe rãna daga gare shi, sai gã su sunã mãsu shiga duhu.
38Kuma rãnã tanã gudãna zuwa ga wani matabbaci nãta. Wannan ƙaddarãwar Mabuwãyi ne, Masani.
39Kuma da watã Mun ƙaddara masa manzilõli, har ya kõma kamar tsumagiyar murlin dabĩno wadda ta tsũfa.
40Rãnã bã ya kamãta a gare ta, ta riski watã. Kuma dare bã ya kamãta a gare shi ya zama mai tsħre wa yini, kuma dukansua cikin sarari guda suke yin iyo.
41Kuma ãyã ce a gare su. Lalle Mũ, Mun ɗauki zuriyarsu a cikin jirgin, wanda aka yi wa lõdi.
42Kuma Muka halitta musu, daga irinsa, abin da suke hawa.
43Kuma idan Mun so, zã Mu nutsar da su, har bãbu kururuwar neman ãgaji, a gare su, kuma ba su zama anã tsirar da su ba.
44Sai fa bisa ga wata rahama daga gare Mu, da jiyarwa dãɗi zuwa ga wani ɗan lõkaci.
45Kuma idan aka ce musu, "Ku kãre abin da ke a gaba gare ku da abin da yake a bãyanku, dõmin tsammãninku a ji tausayinku."
46Kuma wata ãyã daga ãyõyin Ubangijinsu bã ta zuwa a gare su, sai sun kasance sunã mãsu bijirħwa daga gare ta.
47Kuma idan aka ce musu, "Ku ciyar daga abin da Allah Ya azurta ku," sai waɗanda suka kãfirta su ce ga waɗanda suka yi ĩmãni, "Ashe, zã mu ciyar da wanda idan Allah Ya so Yanã ciyar da shi? Ba ku zama ba fãce a cikin ɓata bayyananniya."
48Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi yake (aukuwa) idan kun kasance mãsu gaskiya?"
49Bã su jiran (kõme) fãce wata tsãwa guda, zã ta kãma su, alhãli kuwa sunã yin husũma.
50Bã zã su iya yin wasiyya(1) ba, kuma bã zã su iya kõmãwa zuwa ga iyãlansu ba.
51Kuma aka yi bũsa a cikin ƙaho, to, sai gã su, daga kaburbura zuwa ga Ubangijinsu, sunã ta gudu.
52Suka ce: "Yã bonenmu! Wãne ne ya tãyar da mu daga barcinmu?" "Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa´adi da shi, kuma Manzanni sun yi gaskiya."
53Ba ta kasance ba fãce wata tsãwa ce guda, sai gã su duka, sunã abin halartarwa a gare Mu.
54To, a yau, bã zã a zãlunci wani rai da kõme ba. Kuma bã zã a sãkã muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
55Lalle, ´yan Aljanna, a yau, sunã cikin shagali, sunã mãsu nishãɗi.
56Sũ da mãtan aurensu sunã cikin inuwõwi, a kan karagai, sunã mãsu gincira.
57Sunã da, ´ya´yan itãcen marmari a cikinta kuma sunã sãmun abin da suke kiran a kãwo.
58"Aminci," da magana,(1) daga Ubangiji Mai jin ƙai.
59"Ku rarrabe dabam, a yau, yã kũ mãsu laifi!"
60"Ashe, ban yi muku umurni na alkawari ba, yã ɗiyan Ãdamu? cħwa kada ku bauta wa Shaiɗan, lalle shĩ, maƙiyi ne a gareku bayyananne?"
61"Kuma ku bauta Mini. Wannan ita ce hanya madaidaciya."
62"Kuma lalle haƙĩƙa, (Shaiɗan) yã ɓatar da jama´a mãsu yawa daga gare ku. Ashe to ba ku kasance kunã yin hankali ba?"
63"Wannan ita ce Jahannama wadda kuka kasance anã yi muku wa´adi da ita."
64"Ku shigħ ta a yau, sabõda abin da kuka kasance kunã yi na kãfirci."
65A yau, Munã sanya hãtimin rufi a kan bãkunansu, kuma hannãyensu su yi Mana magana, kuma ƙafãfunsu su yi shaidu da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
66Dã Mun so, dã Mun shãfe gani(2) daga idãnunsu, sai su yi tsħre ga hanya, to, yaya zã su yi gani?
67Kuma da Mun so, da Mun juyar da halittarsu a kan halinsu, saboda haka ba zã su iya shuɗewa ba, kuma ba zã su komo ba.
68Kuma wanda Muka rãya shi, Manã sunkuyar da shi ga halittarsa. Ashe, bã su hankalta?
69Ba Mu sanar da shi (Annabi) wãkã ba, kuma wãkã ba ta kamãta da shi (Annabi) ba. Shi (Al-ƙur´ãni) bai zama ba fãce tunãtarwa ce, da abin karãtu bayyananne.
70Dõmin ya yi gargaɗi ga wanda ya kasance mai rai, kuma magana ta wajaba a kan kãfirai.
71Shin, ba su gani ba (cħwa) lalle Mun halitta musu dabbõbi daga abin da HannayenMu suka aikata, sai sunã mallakar su?
72Kuma Muka hõre su, sabõda su, sabõda haka daga gare su abin hawansu yake, kuma daga gare su suke ci.
73Kuma sunã da waɗansu amfãnõni a cikinsu, da abũbuwan shã. Ashe fa, bã zã; su gõdħ ba?
74Kuma suka riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa wanin Allah, ɗammãninsu zã su taimake su.
75Bã zã su iya taimakonsu ba, alhãli kuwa sũ runduna ce wadda ake halartarwa (a cikin wutã).
76Sabõda haka, kada maganarsu ta ɓãta maka rai. Lalle Mũ, Munã sanin abin da suke asirtãwa da abin da suke bayyanãwa.
77Ashe, kuma mutum bai ga (cħwa) lalle Mũ, Mun halitta shi daga maniyyi ba, sai gã shi mai yawan husũma, mai bayyanãwar husũmar.
78Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu?"
79Ka ce: "Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwace halitta, Mai ilmi ne."
80"Wanda ya sanya muku wutã daga itãce kõre, sai gã ku kunã kunnãwa daga gare shi."
81"Shin, kuma Wanda Ya halitta sammai da ƙasã bai zama Mai ĩkon yi ba ga Ya halitta kwatankwacinsu? Na´am, zai iya! Kuma Shĩ Mai yawan halittãwa ne,Mai ilmi."
82UmurninSa idan Yã yi nufin wani abu sai Ya ce masa kawai, "Ka kasance," sai yana kasancewa (kamar yadda Yake nufi).
83Sabõda haka, tsarki yã tabbata ga Wanda mallakar kõwane abu take ga HannãyenSa, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku.
Chapter 37 (Sura 37)
1Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
2Sa´an nan mãsu yin tsãwa(1) dõmin gargaɗi.
3Sa´an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
4Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa Ɗaya ne.
5Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
6Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
7Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
8Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama´a mafi ɗaukaka (Malã´iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane għfe.
9Dõmin tunkuɗħwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
10Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
11Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
12ôa, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
13Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
14Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
15Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
16"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa,ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
17"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
18Ka ce: "Na´am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
19Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
20Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
21Wannan ita ce rãnar rarrabħwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
22Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
23Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
24Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
25Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
26ôa, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
27Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
28Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jħ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
29Suka ce: "ôa, ba ku kasance mũminai ba.
30"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. ôa, kun kasance mutãne ne mãsu kħtare iyãka."
31"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
32"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
33To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
34Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
35Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
36Kuma sunã cħwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
37ôa, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
38Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
39Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
40Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
41Waɗannan sunã da abinci sananne.
42´Ya´yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
43A cikin gidãjen Aljannar ni´ima.
44A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
45Anã kħwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marħmari.
46Farã mai dãɗi ga mashãyan.
47A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
48Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
49Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
50Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
51Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
52Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
53"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
54(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
55Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
56Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
57"Kuma bã dõmin ni´imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
58"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
59"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
60Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
61Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
62Shin wancan shĩ ne mafi zama alhħri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
63Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
64Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
65Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
66To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa´an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
67Sa´an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
68Sa´an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
69Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
70Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
71Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
72Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
73Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
74Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
75Kuma lalle, haƙĩƙa´ Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
76Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
77Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
78Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama´ar ƙarshe.
79Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
80Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
81Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
82Sã´an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
83Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
84A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
85A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mħne ne kuke bautãwa?"
86"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
87"To, mħne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
88Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
89Sã´an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
90Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
91Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa´an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
92"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
93Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
94Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
95Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
96"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
97Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa´an nan ku jħfa shi a cikin Jahĩm."
98Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
99Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
100"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
101Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro(1) mai haƙuri.
102To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mħ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
103To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga għfen gõshinsa.
104Kuma Muka kira shi cħwa "Ya Ibrahĩm!"
105"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
106Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
107Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
108Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
109Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
110Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
111Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
112Kuma Muka yi masa bushãra(1) Da Is´hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
113Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is´hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
114Kuma lalle, Mun yi ni´ima ga Mũsã da Hãrũna.
115Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
116Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
117Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
118Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
119Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
120Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
121Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
122Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
123Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
124A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
125"Shin, kunã bauta wa Ba´al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
126"Allah Ubangijinku,kuma Ubangijin ubanninku farko?"
127Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
128Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
129Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
130Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
131Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
132Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
133Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
134A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
135Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
136Sã´an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
137Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
138Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
139Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
140A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
141Sã´an nan ya yi ƙuri´a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
142Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
143To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
144Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
145Sai Muka jħfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
146Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
147Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
148Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
149Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da ´ya´ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
150Kõ kuma Mun halitta malã´iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
151To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cħwa.
152"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
153Shin, Yã zãɓi ´yã´ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
154Mħ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
155Shin, bã ku tunãni?
156Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
157To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
158Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
159Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
160Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
161To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
162Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
163Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
164"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,(1) fãce yanã da matsayi sananne."
165"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
166"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
167Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cħwa,
168"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
169"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
170Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
171Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
172Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
173Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
174Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
175Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.(2)
176Shin fa, da azabarMu suke nħman gaggãwa?
177To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
178Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
179Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
180Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
181Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
182Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
Chapter 38 (Sura 38)
1Ṣ̃, Inã rantsuwa da Al-ƙur´ãni mai hukunce-hukunce.
2ôa, waɗanda suka kãfirta sunã cikin girman kai (ga rikon al´ãdunsu) da sãɓãni (tsakãnin jũnansu).
3Da yawa Muka halakar da wani ƙarni, a gabãninsu, suka yi kira (nħman cħto), bãbu lõkacin kuɓucewa.
4Kuma suka yi mãmãki dõmin Mai gargaɗi, daga cikinsu, ya je musu. Kuma kãfirai sukace, "Wannan mai sihiri ne, maƙaryaci."
5"Shin, yã sanya gumãka duka su zama abin bautawa guda? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmaki!"
6Shũgabanni daga cikinsu, suka tafi (suka ce),"Ku yi tafiyarku, ku yi haƙuri a kan abũbuwan bautawarku. Lalle wannan, haƙiƙa, wani abu ne ake nufi!"
7"Ba mu taɓa ji ba, game da wannan a cikin addinin ƙarshe. Wannan bai zama ba fãce ƙiren ƙarya."
8"Shin, an saukar da Alƙur´ãni ne a kansa, a tsakãninmu (mũ kuma ba mu gani ba )?" ôa, su dai sunã cikin shakka daga hukunciNa ôa, ba su i da ɗanɗanar azãba ba.
9Ko kuma a wurinsu ne ake ajiye taskõkin rahamar Ubangijinka, Mabuwãyi, Mai yawan kyauta?
10Kõ kuma sũ ne da mallakar sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu? To sai su hau a cikin sammai (dõmin, su hana saukar Alƙur´ãni ga Muhammadu).
11Rundunõni ne abin da ke can, rusassu, na ƙungiyõyinsu.
12Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, da Ãdãwa da Fir´auna mai turãkun (da suka kafe mulkinsa).
13Da Samũdãwa da mutãnen Luɗu da ma´abũta ƙunci,(1) waɗancan ne ƙungiyõyin.
14Bãbu kõwa a cikinsu fãce ya ƙaryata Manzanni, sabõda haka azãbãTa ta wajaba.
15Kuma waɗannan(2) bã su jiran kõme fãce tsãwã guda, wadda bã ta da hani.
16Kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka gaggauta mana da rabonmu, a gabãnin rãnar bincike."(3)
17Ka yi haƙuri bisa ga abin da suke faɗa (na izgili), kuma ka ambaci bãwanMu Dãwũda ma´abũcin ƙarfin ibãda. Lalle, shi, mai mayar da al´amari ga Allah ne.
18Lalle Mũ, Mun hõre duwãtsu tãre da shi, sunã yin tasbĩhi maraice da fitõwar rãnã.
19Da tsuntsãye waɗanda ake tattarawa, kõwannensu mai kõmãwa ne a gare shi.
20Kuma Muka ƙarfafa mulkinsa, kuma Muka bã shi hikima(1) da rarrabħwar magana.
21Kuma shin, lãbãrin mãsu husũma ya zo maka, a lõkacin da suka haura gãrun masallaci?
22A lõkacin da suka shiga ga Dãwũda, sai ya firgita daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro, masu husuma biyu ne; sãshenmu ya zãlunci sãshe. Sabõda haka, ka yi hakunci a tsakãninmu da gaskiya. Kada ka ƙħtare haddi kuma ka shiryar da mu zuwa, ga tsakar hanya."
23"Lalle wannan dan´uwãna ne, yanã da tunkiya casa´in da tara, kuma inã da tunkiya guda, sai ya ce: ´Ka lãmunce mini ita. Kuma ya buwãye ni ga magana."
24(Dãwũda) ya ce: "Lalle, haƙiƙa ya zãlunce(2) ka game da tambayar tunkiyarka zuwa ga tumakinsa. Kuma lalle ne mãsu yawa daga abõkan tarayya, haƙiƙa, sãshensu na zambatar sãshe fãce waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai." Kuma Dãwũda ya tabbata cħwa Mun fitine shi ne, sabõda haka, ya nħmi Ubangijinsa gãfara,kuma ya fãɗi yanã mai sujada, kuma ya mayar da al´amari ga Allah.
25Sabõda haka Muka gãfarta masa wancan, kuma lalle yanã da wata kusantar daraja a wurinMu, da kyaun makõma.
26Yã Dãwũda! Lalle Mũ Mun sanya ka Halĩfa a cikin ƙasã. To, ka yi hukunci tsakãnin mutãne da gaskiya, kuma kada ka biye wa son zũciyar, har ya ɓatar dakai daga hanyar Allah. Lalle waɗanda ke ɓacħwa daga hanyar Allah sunã da wata azãba mai tsanani dõmin abin da suka manta, a rãnar hisãbi
27Kuma ba Mu halitta sama da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu ba a kan ƙarya. Wannan shĩ ne zaton waɗanda suka kãfirta. To, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta daga wutã.
28Kõ zã Mu sanya waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai kamar waɗanda suke mãsu barna ne a cikin ƙasa? Ko kuma za Mu sanya masu bin Allah da taƙawa kamar fãjirai makarkata?
29(Wannan) Littãfi ne, Mun saukar da shi zuwa gare ka, yanã, mai albarka, dõmin su lũra da ãyõyinsa, kuma don mãsu hankali su riƙa yin tunãni.
30Kuma Muka bai wa Dãwũda Sulaimãn. Mãdalla da bãwanMu, shi. Lalle shi (Sulaimãn) mai mayar da al´amari ne ga Allah.
31A lõkacin da aka gitta masa dawãki mãsu asali,(1) a lõkacin maraice.
32Sai ya ce: "Lalle nĩ, na fĩfĩta son dũkiya daga tunãwar Ubangijina, har (rãnã) ta faku da shãmaki!"
33"Ku mayar da su a gare ni." Sai ya shiga yankansu(2) da takõbi ga ƙwabrukansu da wuyõyinsu.
34Kuma lalle haƙĩƙa, Mun fitini (3) Sulaiman kuma Muka jħfa wani jikin mutum a kan karagarsa. Sa´an nan ya mayar da al´amari zuwa gare Mu.
35Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka gãfarta mini, kuma Ka bã ni mulki wanda bã ya kamãta da kõwa daga bãyãna.(4) Lalle Kai, Kai ne Mai yawan kyauta.
36Sabõda haka Muka hõre masa iska(5) tanã gudu da umurninsa, tãna tãshi da sauƙi, inda ya nufa.
37Da shaiɗanu dukan mai gini, da mai nutsa (a cikin kõguna.)
38Waɗansu, ɗaɗɗaure a cikin marũruwa.
39Wannan kyautarMu ce. Sai ka yi kyauta ga wanda kake so, ko kuma ka riƙe, bãbu wani bincike.
40Kuma lalle, haƙĩƙa yanã da kusantar daraja a wurinMu da kyaun makõma.
41Kuma ka ambaci bãwanMu Ayyũba(6) a lõkacin da ya kirãyi Ubangijinsa, ya ce: "Lalle nĩ, Shaiɗan yã shãfe ni da wahala da kuma wata azãba."
42Ka shura da ƙafarka. Wannan abin wanka ne mai sanyi da abin shã.
43Kuma Muka bã shi iyalansa da kwatankwacinsu tãre da su sabõda rahama daga gare Mu, da tunãtarwa ga mãsu hankali.
44Kuma ka riƙi wata ƙulla da hannunka, ka yi dũka da ita kuma kada ka karya rantsuwarka. Lalle Mũ, Mun sãme shi mai haƙuri. Madalla da bãwa, shĩ Lalle shĩ mai mayar da al´amari ga Allah ne.
45Kuma ka ambaci bãyinMu: Ibrahĩm da ls´hãƙa da Ya´aƙũba, ma´abũta ƙarfin (ɗaukar umurninMu) da basĩra.
46Lalle Mũ, Mun keɓance su game da wata, tsattsarkar aba: Hukunce-hukuncen gidan dũniya (mai tunãtar da su Lãhira).
47Kuma lalle sũ a wurinMu, tabbas, sunã daga zãɓaɓɓu, mafĩfĩta.
48Kuma ka ambaci Isma´ĩla da llyãs da Zulkifli, kuma dukansu sunã daga zãɓaɓɓu.
49Wannan tunãtarwa ce, kuma lalle mãsu bin Allah da taƙawa, sunã da kyakkyawar makõma.
50Gidãjen Aljannar zama , alhãli kuwa tanã abar buɗe wa kõfõfi sabõda su.
51Sunã gingincire a cikinsu, sunã kira a cikinsu, ga ´ya´yan itãcen marmari mãsu yawa, da abin shã.
52Kuma a wurinsu akwai mãtan aure mãsu gajarta ganinsu ga mazansu, tsãrar jũna.
53Wannan shĩ ne abin da ake yi muku wa´adi ga rãnar hisãbi.
54Lalle wannan, haƙĩƙa, azurtarwarMu ce, bã ta ƙãrħwa.
55Wannan shĩ ne kuma lalle makangara, haƙĩƙa, sunã da mafi sharrin makõma.
56Jahannama, sunã shigarta. To, shimfiɗar tã mũnana, ita.
57Wannan shĩ ne! To, su ɗanɗane shi: ruwan zãfi ne da ruɓaɓɓen jini.
58Da wani daga siffarsa nau´i-nau´i.
59Wannan wani yanki ne mai kũtsawa tãre da ku, bãbu marãba a gare su, lalle sũ, mãsu shiga Wutã ne.
60Suka ce: "ôa, ku ne bãbu marãba a gare ku, kũ ne kuka gabãtar da shi a gare mu." To, matabbatar tã mũnana (ita wutar).
61Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Wanda ya gabãtar da wannan a gare mu, to, Ka ƙãra masa azãba, ninki, a cikin wutã."
62Kuma suka ce: "Mħ ya sãme mu, bã mu ganin waɗansu mazãje, mun kasance munã ƙidãya su daga asharãrai?"
63"Shin, mun riƙe su abin izgili ne kõ idãnunmu sun karkata daga gare su ne?"
64Lalle wannan, haƙĩƙa, gaskiya ne, husũmar mutãnen wutã.
65Ka ce: "Nĩ mai gargaɗikawai ne, kuma babu wani abin bautawa sai Allah, Makaɗaici, Mai tilastawa."
66"Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu Mabuwãyi, Mai gãfara."
67Ka ce: "Shĩ (Alkur´ãni) babban lãbãri ne mai girma".
68"Kũ, mãsu bijirħwa ne daga gare shi!"
69"Wani ilmi bai kasance a gare ni ba game da jama´a (malã´iku) mafi ɗaukaka a lõkacin da suke yin husũma."
70"Ba a yi mini wahayin kõme ba face cħwa ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyanãwa."
71A lõkacin da Ubangijinka Ya ce wa malã´iku, "Lalle Nĩ Mai halitta mutum ne daga lãkã.
72"Sa´an nan idan Nã daidaita shi, kuma Na hũra (wani abu) daga RuhĩNa a cikinsa to ku fãɗi kunã mãsu sujada a gare; shi."
73Sai malã´ikun suka yi sujada dukansu, gabã ɗaya.
74Fãce Iblis, ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai.
75(Allah) Ya ce, "Yã Ibilis! Mħ ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Nã halitta da HannayeNa biyu? Shin, kã yi girman kai ne, kõ kuwa kã kasance daga maɗaukaka ne?"
76Ya ce, "Nĩ, mafifici ne daga gare shi: Kã halitta ni daga wutã, kuma Kã halitta shi daga lãkã."
77Ya ce, "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai la´ananne ne."
78"Kuma lalle a kanka akwai la´anaTa har zuwa rãnar sakamako."
79Ya ce, "Ya Ubangijina! To, Ka yi mini jinkiri zuwa ga rãnar da ake tãyar da su."
80Ya ce, "To, lalle kanã daga waɗanda aka yi wa jinkiri,
81"Zuwa ga yinin lõkaci sananne."
82Ya ce, "To, inã rantsuwa da buwãyarKa, lalle, inã ɓatar da su gabã ɗaya.
83"Fãce bãyinKa tsarkakakku daga gare su."
84(Allah) Ya ce, "To, (wannan magana ita ce) gaskiya. Kuma gaskiya Nake faɗa."
85"Lalle zã Ni cika Jahannama daga gare ka, kuma daga wanda ya bĩ ka daga gare su, gabã ɗaya"
86Ka ce: "Bã ni tambayar ku wata ijãra, a kansa kuma bã ni daga mãsu ƙãƙalen faɗarsa."
87"Shĩ (Alkur´ãn) bai zama ba fãce ambato ne ga dukan halitta."
88"Kuma lalle zã ku san babban lãbãrinsa(1) a bayan ɗan lõkaci."
Chapter 39 (Sura 39)
1Saukar da Littãfin daga Allah ne, Mabuwãyi, Mai hikima.
2Lalle Mũ Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka, da gaskiya. Sabõda haka, ka bauta wa Allah kanã mai tsarkake addini a gare Shi.
3To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi(2) ba, (sunã cħwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci.
4Dã Allah Yã yi nufin Ya riƙi ɗã, to, lalle sai Ya zãɓa daga abin da Yake halittãwa abin da Yake so. Tsarki ya tabbata a gare Shi. Shĩ ne Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa.
5Ya halitta sammai da ƙasã da gaskiya. Yanã shigar da dare a kan rãna, kuma Yanã shigar da rãnã a kan dare kuma Yã hõre rãnã da watã, kõwannensu yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce. To, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai gãfara.
6Yã halitta ku daga rai guda, sa´an nan Ya sanya ma´auranta daga gare shi. Kuma ya saukar muku daga dabbõbin gida nau´i takwas Yanã halitta ku a cikin cikunnan uwayenku, halitta a bãyan wata halitta, a cikin duffai uku. Wannan shĩ ne Allah Ubangijinku. Mulki a gare shi yake. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?
7Idan kun kãfirta to, lalle Allah Wadãtacce ne daga barinku, kuma bã Shi yarda da kãfirci ga bãyinSa, kuma idan kun gõde, Zai yarda da ita (gõdiyar) a gare ku, kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, bã ya ɗaukar nauyin wani. Sa´an nan kuma makõmarku zuwa ga Ubangijinku take, dõmin Ya bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa. Lalle Shĩ, Masani ne ga abin da yake a ainihin zukata.
8Kuma idan wata cũta ta shãfi mutum, sai ya kira Ubangijinsa, yanã mai mai da al´amari zuwa gare Shi, sa´an nan idan Ya jũyar da cũtar da ni´ima ta daga gare Shi, sai ya manta da abin da ya kasance yanã kira zuwa gare shi a gabãnin haka, kuma ya sanya wa Allah waɗansu abõkan tarħwa dõmin ya ɓatar (da su) daga hanyarSa. Ka ce (masa), "Ka ji dãɗi da kãfircinka, a ɗan lõkaci, lalle kai daga ´yan wutã ne."
9Shin, wanda yake mai tawãli´u sã´õ´in dare, yanã mai sujada kuma yanã mai tsayi ga salla, yanã tsõron Lãhira, kuma yanã fãtan rahamar Ubangijinsa, (yanã daidai da waninsa?) Ka ce: "Ashe, waɗanda suka sani, sunã daidaita da waɗanda ba su sani ba?" Mãsu hankali kawai ke yin tunãni.
10Ka ce: (Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi ĩmãni!Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Waɗanda suka kyautata a cikin wannan dũniya sunã da sakamako mai kyau, kuma ƙasar Allah mai fãɗi(1) ce. Mãsu haƙuri kawai ake cika wa ijãrarsu, bã da wani lissãfi ba.
11Ka ce: "Lalle nĩ, an umurce ni da in bauta wa Allah, inã tsarkake addini a gare Shi.
12"Kuma an umurce ni da in kasance farkon mãsu miƙa wuya (ga umurnin Allah)."
13Ka ce: "Lalle nĩ inã tsõro, idan na sãɓã wa Ubangijĩna, ga azãbar yini mai girma."
14Ka ce: "Allah nake bautã wa, inã mai tsarkake addinĩna a gare Shi.
15"To, ku bauta wa abin da kuke so, waninSa." Ka ce: "Lalle mãsu hasãra, sũ ne waɗanda suka yi hasarar rãyukansu da iyãlansu, a Rãnar Ƙiyãma. To, waccan fa, ita ce hasãra bayyananna."
16Sunã da waɗansu inuwõwi na wutã daga samansu, kuma daga ƙasansu akwai waɗansu inuwõwi. Wancan Shĩ ne Allah ke tsõratar da bãyinSa da shi. Yã bãyĩNa! To, ku bĩ Ni da taƙawa.
17Kuma waɗanda suka nĩsanci Shaiɗannu ga bauta musu, kuma suka mai da al´amari ga Allah, sunã da bushãra. To, ka bãyar da bushãra ga bãyiNa.
18Waɗanda ke sauraren(1) magana, sa´an nan su bi mafi kyaunta. waɗancan sũ ne Allah Ya shiryar da su, kuma waɗancan su ne mãsu hankali,
19Shin fa, wanda kalmar azãba ta wajaba a kansa? Shin fa, kanã iya tsãmar da wanda ke a cikin wutã?
20Amma waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa, sunã da bħnãye, daga samansu akwai waɗansu bħnãye ginannu, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Alkawarin Allah. Allah bã Ya sãɓã wa alkawarinSa.
21Shin, ba ka gani ba cħwa lalle Allah Yã saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Yã gudãnar da shi yanã marħmari a cikin ƙasã sa´an nan Yã fitar da shũka game da shi, launukan shũkar mãsu sãɓãnin jũna sa´annan shũkar ta ƙeƙashe har ka gan ta fatsifatsi, sa´an nan Allah Ya sanya ta dandaƙaƙƙiya? Lalle ne ga wancan akwai tunãtarwa ga mãsu hankali (ga iyãwar gudãnar da ruwa a cikin gidãjen Aljanna).
22Shin fa, wanda Allah Ya buɗa ƙirjinsa, dõmin Musulunci sa´an nan shi yanã a kan haske daga Ubangijinsa, (zai zama kamar waninsa)? To, bone yã tabbata ga maƙeƙasa zukãtansu daga ambaton Allah. Waɗancan sunã a cikin wata ɓata bayyananna.
23Allah Ya sassaukar da mafi kyaun lãbãri, Littãfi mai kama da jũna, wanda ake konkoma karãtunsa fãtun waɗanda ke tsõron Ubangijinsu, sunã tãƙura sabõda Shi, sa´an nan fãtunsu da zukãtansu su yi laushi zuwa ga ambaton Allah. Waccan ita ce shiryarwar Allah, Yanã shiryar da wanda Ya so game da ita. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bã shi da wani mai shiryarwa.
24Shin fa, wanda ke kãre mũguwar azãba da fuskarsa (yanã zama kamar waninsa) a Rãnar ƙiyãma? Kuma a ce wa azzãlumai, "Ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
25Waɗanda ke a gabãninsu, sun ƙaryata, sai azãba ta jħ musu daga inda ba su sani ba.
26Sai Allah Ya ɗanɗana musu azãbar wulãkanci a cikin rãyuwar dũniya, kuma lalle azãbar Lãhira ita ce mafi girma, dã sun kasance sunã da sani.
27Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun buga wa mutãne a, cikin wannan Alƙur´ãni, daga kõwane misãli, ɗammãninsu su yi tunãni.
28Abin karantãwa ne na Lãrabci, ba mai wata karkata ba, ɗammãninsu, su yi taƙawa.
29Allah Yã buga misãli; wani mutum (bãwa) a cikinsa akwai mãsu tarayya, mãsu mũgun hãlin jãyayya, da wani mutum (bãwa) dukansa ga wani mutum. Shin, zã su daidaita ga misãli? Gõdiya ta tabbata ga Allah (a kan bayãni). ôa, mafi yawan mutãne ba su sani ba.
30Lalle kai mai mutuwa ne, kuma su mã lalle mãsu mutuwa ne.
31Sa´an nan, lalle kũ, a Rãnar Ƙiyãma, a wurin Ubangijinku, zã ku yi ta yin husũma.
32To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya yi ƙarya ga Allah, kuma ya ƙaryata gaskiya a lõkacin da ta jħ masa? Shin bãbu mazauni a cikin Jahannama ga kãfirai?
33Kuma wanda ya zo da gaskiya, kuma ya gaskata a game da ita, waɗancan sũ ne mãsu taƙawa.
34Sunã da abin da suke so wajen Ubangijinsu. Wancan shĩ ne sakamakon mãsu kyautatãwa.
35Dõmin Allah Ya kankare musu mafi mũnin abin da suka aikata, kuma Ya sãkã musu ijãrarsu da mafi kyaun abin da suka kasance sunã aikatãwa.
36Ashe Allah bai zama Mai isa ga BãwanSa ba? Kuma sunã tsõratar da kai ga waɗanda suke waninSa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to, bã, shi da mai shiryarwa.
37Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, bã shi da mai ɓatarwa. Ashe, Allah bai zama Mabuwãyi ba, Mai azãbar rãmuwa?
38Kuma lalle idan ka tambaye su: "Wane ne ya halitta sammai da ƙasã?" Haƙĩƙa, zã su ce, "Allah ne." Ka ce: "Ashe, to, kun gani abin da kuke kira, waɗanda suke wanin Allah ne, idan Allah Ya nufe ni da wata cũta, shin sũ abũbuwan nan mãsu kuranye, cutarsa ne? Kõ kuma Ya nufe ni da wata rahama, shin, su abũbuwan nan mãsu kãme rahamarSa ne?" Ka ce: "Mai isata Allah ne, gare Shi mãsu tawakkali ke dõgara."
39Ka ce: "Yã mutãnena! Ku yi aiki a kan hãlinku, lalle nĩ, inã aiki a kan hãlĩna. Sa´an nan zã ku sani."
40"Wanda azãba ta je masa, zã ta wulãkanta shi, kuma wata azãba mai dawwama za ta sauka a kansa."
41Lalle Mũ Mun saukar da littãfi a gare ka dõmin mutãne da gaskiya. Sa´an nan wanda ya nħmi shiriya, to, dõmin kansa, kuma wanda ya ɓace, to, yanã ɓacħwa ne a kanta. Kuma ba ka zama wakĩli a kansu ba.
42Allah ne ke karɓar rãyuka a lõkacin mutuwarsu, da waɗannan da ba su mutu ba, a cikin barcinsu. Sa´an nan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin tunãni.
43Kõ kuma sun riƙi mãsu cħto ne, waɗansun Allah? Ka ce: "Shin, kuma kõ dã sun kasance bã su da mallakar kõme, kuma bã su hankalta?"
44Ka ce: "Cħto gabã ɗaya ga Allah yake. Mulkin sammai da ƙasã Nãsa ne. Sa´an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku."
45Kuma idan aka ambaci Allah Shi kaɗai zukãtan waɗanda ba su yi ĩmãni ba da Lãhira, su yi ƙiyãma, kuma idan an ambaci waɗanda suke kiran, wasunSa, sai gãsu sunã yin bushãrar farin ciki.
46Ka ce: "Ya Allah, Mai ƙãga halittar sammai da ƙasã, Masanin gaibi da bayyane! Kai ne ke yin hukunci a tsakãnin bãyinKa a cikin abin da suka kasance sunã sãɓa wa jũna a cikinsa."
47Kuma dã waɗanda suka yi zãlunci sunã da abin da ke cikin ƙasã gaba ɗaya, da misãlinsa a tãre da shi lalle dã sun yi fansa da shi daga mummunar azãba, a Rãnar Ƙiyãma. Kuma abin da ba su kasance sunã zato ba, daga Allah, ya bayyana a gare su.
48Mũnãnan ayyuka da suka aikata, suka bayyana a gare su, kuma abin da suka kasance sunã yi, na izgili, ya wajaba a kansu.
49To, idan wata cũta ta shãfi mutum, sai ya kirãye Mu, sa´an nan idan Muka canza masa ita, ya sãmi ni´ima daga gare Mu, sai ya ce: "An bã ni ita ne a kan wani ilmi nãwa kawai." ôa ita wannan (magana) fitina ce, kuma amma mafi yawansu ba su sani ba.
50Lalle waɗanda ke a gabãninsu, sun faɗe ta, sabõda haka abin da suka kasance sunã aikatãwa bai wadãtar da su da kõme ba.
51Sai (sakamakon) mũnãnan abin da suka aikata ya same su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci daga waɗannan, (sakamakon) munãnan abin da suka aikata zai sãme su, kuma ba su zama mabuwãya ba.
52Ashe kuma ba su sani ba cħwa Allah, na shimfiɗa arziƙi ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuƙuntawa? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin ĩmãni.
53Ka ce: (Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi barna a kan rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."
54"Kuma ku mayar da al´amari zuwa ga Ubangijinku, kuma ku sallama Masa, a gabãnin azãba ta zo muku, sa´an nan kuwa bã zã a taimake ku ba."
55"Kuma ku bi mafi kyaun abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, a gabãnin azãba ta zo muku, bisa auke, kuma kũ ba ku sani ba."
56"Kada wani rai ya ce: ´Yã nadãmãta a kan abin da na yi sakaci a cikin sãshen Allah´ kuma lalle na kasance, haƙĩƙa, daga mãsu izgili!"´
57"Ko kuma (kada) ya ce: ´Da Allah Ya shiryar da ni, dã na kasance daga mãsu taƙawa.´"
58"Ko kuma (kada (ya ce: a lõkacin da yake ganin azãba, ´Dã lalle a ce inã da wata kõmawa (zuwa dũniya) dõmin in kasance daga mãsu kyautatãwa.´"
59"Na´am! Lalle ne ãyõyiNa sun jħ maka, sai ka ƙaryata a game da su, kuma ka yi girman kai, kuma ka kasance daga kãfirai."
60Kuma a Rãnar Ƙiyãma kanã ganin waɗanda suka yi ƙarya ga Allah fuskõkinsu sunã mãsu yin baƙi. Ashe bãbu mazauni a cikin Jahannama ga mãsu girman kai?
61Kuma Allah na tsĩrar da waɗanda suka yi taƙawa a game da wurin sãmun babban rabonsu, cũta bã zã tashãfe su ba, kuma ba su zama sunã baƙin ciki ba.
62Allah ne Mai halitta dukan kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme.
63Shĩ ke da mabũɗan sammai da ƙasã. Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah, waɗannan sũ nemãsu hasãra.
64Ka ce: "Shin, wanin Allah kuke umurni na da in bauta wa? Yã ku jãhilai!"
65Kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga waɗanda suke a gabãninka, "Lalle idan ka yi shirki haƙĩƙa aikinka zai ɓãci, kuma lalle zã ka kasance daga mãsu hasãra."
66ôaha! Ka bauta wa Allah kaɗai, kuma ka kasance daga mãsu gõdiya.
67Kuma ba su ƙaddara Allah a kan haƙĩƙanin(1) ĩkon yinsa ba: Ƙasã duka damƙarSa ce, a Rãnar Ƙiyãma, kuma sammai abũbuwan naɗewa ne ga dãmanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirki da shi.
68Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasã suka sũma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa) sa´an nan aka hũra a cikinsa, wata hũrãwa, sai gã su tsaitsaye, sunã kallo.
69Kuma ƙasã ta yi haske da hasken Ubangijinta, kuma aka aza littãfi, kuma aka zo da Annabãwa da mãsu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakãninsu, da gaskiya, alhãli kuwa, sũ, bã zã a zãlunce su ba.
70Kuma aka cika wa kõwane rai abin da ya aikata. Kuma (Allah) Shĩ ne Mafi sani game da abin da suke aikatãwa.
71Kuma aka kõra waɗanda suka kãfirta zuwa Jahannama, jama´a-jama´a har a lõkacin da suka je mata, sai aka buɗe ƙõfõfinta, kuma matsaranta suka ce musu, "Ashe, waɗansu Manzanni, daga cikinku ba su je muku ba, sunã karanta ãyõyin Ubangijinku a kanku, kuma sunã yi muku gargaɗin gamuwa da yininku wannan?" Suka ce, "Na´am, "kuma amma kalmar azãba ita ce ta wajaba a kan kãfirai!"
72Aka ce, "Ku shiga ƙõfõfin Jahannama, kaunã madawwama a cikinta. Sa´an nan mazaunin makangara yã munana."
73Kuma aka kõra waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa zuwa Aljanna jama´a-jama´a har a lõkacin da suka jħ mata, alhãli kuwa an buɗe kõfõfinta, kuma matsaranta suka ce musu, "Aminci ya tabbata a gare ku, kun ji dãɗi, sabõda haka ku shige ta, kunã madawwama( a cikinta)."
74Kuma suka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya yi mana gaskiya ga wa´adinSa, kuma Ya gãdar da mu ƙasã, munã zama a cikin Aljanna a inda muke so." To, madalla da ijãrar ma´aikata.
75Kuma kanã ganin malã´iku sunã mãsu tsayãwa da haƙƙoƙin da aka ɗõra musu daga kħwayen Al´arshi, sunã tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu. Kuma aka yi hukunci a tsakãninsu da gaskiya. Kuma aka ce, "Gõdiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu."
Chapter 40 (Sura 40)
1Ḥ. M̃.
2Saukar da Littãfi daga Allah ne, Mabuwãyi, Masani.
3Mai gãfarta zunubi kuma Mai karɓar tũba Mai tsananin azãba, Mai wadãtarwa bãbu abin bautawa fãce Shi, zuwa gare Shi makõma take.
4Bãbu mai jãyayya a cikin ãyõyin Allah, fãce waɗanda suka kãfirta. Sabõda haka kada jũyãwarsu a cikin garũruwa ta rũɗe ka
5Mutãnen Nũhu sun ƙaryata a gabãninsu, da ƙungiyõyin da suke a bãyansu, kuma kõwace al´umma tã yi nufi game da Manzonsu, dõmin su kãmã shi. Kuma suka yi jãyayya da ƙarya dõmin su gusar da gaskiya da ita. Sai Na kãmã su. To, yãya azãbãTa take?
6Kuma kamar haka kalmar Ubangijinka ta wajaba a kan waɗanda suka kãfirta, dõmin sũ ´yan wutã ne.
7Waɗanda ke ɗaukar Al´arshi da waɗanda ke kħwayenta, sunã tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu, kuma sunã yin ĩmãni da Shi, kuma sunã yin istigfãri dõmin waɗanda suka yi ĩmãni, (sunã cħwa), "Yã Ubangijinmu! Kã yalwaci dukan kõme da rahama da ilmi to Ka yi gãfara ga waɗanda suka tũba kuma suka bi hanyarKa, kuma Ka tsare musu azãbar Jahĩm."
8"Ya Ubangijinmu! Kuma Ka shigar da su a gidãjen Aljannar zama, wannan da Ka yi musu wa´adi, sũ da wanda ya kyautatu daga ubanninsu da mãtan aurensu da zurriyarsu. Lalle Kai, Kai ne Mabuwãyi, Mai hikima."
9"Kuma Ka tsare su daga mũnãnan ayyuka, kuma wanda Ka tsare shi daga mũnãnan ayyuka a rãnarnan, to, lalle, Ka yi masa rahama kuma wancan shi ne babban rabo mai girma."
10Lalle waɗanda suka kãfirta, anã kiran su, "Haƙĩƙa, ƙin Allah (a gare ku) shĩ ne mafi girma daga ƙinku ga kanku a lõkacin da ake kiran ku zuwa ga ĩmãni, sai kunã ta kãfircħwa."
11Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Kã matar da mu sau biyu, kuma Kã rãyar da mu sau biyu, sabõda haka mun yarda da laifuffukan mu. To, shin, akwai wata hanya zuwa ga fita?"
12Wancan sababinsa, lalle (shi ne) idan an kirãyi Allah Shi kaɗai, sai ku kãfirta, kuma idan aka yi shirki game da Shi, sai ku yi ĩmãni. To, hukuncin fa, na Allah Maɗaukaki, Mai girma ne.
13Shĩ ne Wanda ke nũna muku ãyõyinSa, kuma Ya saukar da arziki daga sama sabõda ku, kuma bãbu mai yin tunãni fãce mai mayar da al´amari ga Allah.
14Sabõda haka ku kirãyi Allah, kunã mãsu tsarkake addini a gare Shi, kuma kõ dã kãfirai sun ƙi.
15Mai ɗaukaka darajõji (dõmin mũminai), Mai Al´arshi, Yanã jħfa rũhi(1) daga al´amarinSa a kan wanda Ya so daga bãyinSa, dõmin ya yi gargaɗi kan rãnar gamuwa.
16Rãnar da suke bayyanannu, bãbu wani abu daga gare su wanda yake iya bõyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa.
17Yau anã sãka wa kõwane rai a game da abin da ya aikata, bãbu zãlunci a yau. Lalle Allah Mai gaggawar hisãbi ne.
18Kuma ka yi musu gargaɗi kan rãnar (Sã´a) makusanciya, a lõkacin da zukãta suke mãsu cika da bakin ciki, ga maƙõsansu. Bãbu wani masõyi ga azzãlumai, kuma bãbu wani mai cħto da zã a yi wa dã´a (ga cħtonsu).
19(Allah) Ya san yaudarar idãnu da abin da ƙirãza ke ɓõyħwa.
20Kuma Allah Shĩ ke yin hukunci da gaskiya, waɗannan da kuke kira, waninSa,bã su yin hukunci da kõme. Lalle Allah, Shĩ ne Mai ji, Mai gani.
21Ashe, ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã, dõmin su dũba ga yadda ãƙibar waɗanda suka kasance a gabãninsu ta zama? Sun kasance sũ ne mafi tsananin ƙarfi daga gare su, da kufaifan aiki a cikin ƙasã, sai Allah Ya kãmã su da laifuffukansu. Kuma bã su da wani mai tsarħwa daga Allah.
22Wancan sababinsa, dõmin sũ Manzanninsu sun kasance sunã zuwa gare su da hujjõji bayyanannu, sai suka kãfirta, sai Allah Ya kãmã su. Lalle Shĩ Mai ƙarfi ne, Mai tsananin azãba.
23Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Mũsã a game da ãyõyinMu da wani dalĩli bayyananne.
24Zuwa ga Fir´auna da Hãmãna da Kãrũna, sai suka ce: "Mai sihiri ne, maƙaryaci."
25Sa´an nan, a lõkacin da ya jħ musu da gaskiya daga wurinMu, suka ce: "Ku kashe ɗiyan waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, kuma ku rãyar da mãtansu." Kuma mugun shirin kãfirai, bai zama ba fãce a cikin bata.
26Kuma Fir´auna ya ce: "Ku bar ni in kashe Mũsã, kuma shĩ, ya kirãyi Ubangijinsa. Lalle ne nĩ, inã tsõron ya musanya addininku, kõ kuwa ya bayyana ɓarna a cikin kasã."
27Kuma Mũsã ya ce: "Lalle nĩ, nã nħmi tsari da Ubangijĩna kuma Ubangijinku, daga dukan makangari, wanda bã ya ĩmani da rãnar Hisãbi."
28Kuma wani namiji mũmini daga dangin Fir´auna, yanã bõye ĩmãninsa, ya ce: "Ashe, za ku kashe mutum dõmin ya ce Ubangijina Allah ne, alhãli kuwa haƙĩƙa ya zo muku da hujjõji bayyanannu daga Ubangijinku? Idan yã kasance maƙaryaci ne, to, ƙaryarsa na kansa, kuma idan ya kasance mai gaskiya ne, sãshen abin da yake yi muku wa´adi zai sãme ku. Lalle ne Allah bã Ya shiryar da wanda yake mai barna, mai yawan ƙarya."
29"Yã kũ mutãnħna! Kunã da mulki a yau, kuma kũ ne marinjãya a cikin kasã to wãne ne zai taimake mu daga azãbar Allah idan ta zo mana?" Fir´auna ya ce: "Bã ni nũnamuku kõme face abin da na gani, kuma ba ni shiryar da ku, sai ga hanyar shiryuwa."
30Kuma wannan da ya yi ĩmãni ya ce: "Ya mutãnħnã! Lallene, nĩ, inã yi muku tsõron kwatankwacin rãnar ƙungiyõyi."
31"Kwatankwacin al´adar mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdãwa da waɗanda ke a bãyansu. Kuma Allah bã Ya nufin zãlunci ga bãyinSa."
32"Kuma ya mutãnħna! Lallenĩ, inã yi muku tsõron rãnar kiran jũna."
33"A rãnar da zã ku jũya, kunã mãsu bãyar da bãya (gudãne) bã ku da wani mai tsaro daga Allah. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bã shi da wani mai shiryarwa."